Sashe 16
Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
SUKUWA maza 'yan daurin aure, ana gama daurin
aure suka nufu daula hotel, don cin abincin daurin
aure, wato walima ta zama kadai 'yan daurin
aure.
Aliyu ba abunda ya dame shi sai washe baki
yake, yana ta gaisawa da mutane. Da yawa
mutane sunata mamaki, don sun san miskilanci
da rashin yawan dariya irin na Aliyu, amma yanzu
ya kasa rufe bakinsa saboda fara'a da amsa
gaisuwar jama'a da masu sanyawa auren nasu
albarka.
Cikin gida kuw, masu gidan yaransu da manyansu
cikin farin ciki suke da wannan aure na Aliyu da
zainab, saboda kawunan su a hade yake.
Su sadiya dasu ni'ima kuwa sai murna suke suna
zuba shewa da tafi.
Zainab kuwa tana dakin umma kudundune cikin
bacin rai, duniyar tayi mata zafi, ta rasa mai yake
mata dadi. Ita bata ga laifin auntyn ta ba, dole
tace taci amanarta. Mai auntyn ta rage ta dashi?
Ta dauketa kamar 'yar cikinta, amma yau
sakayyar da zata yi mata kenan ta aure mata
miji? Ta sake fashewa da kuka.
Meyasa haka? Meyasa yaya Aliyu mata haka?
Tana ganin yaya Aliyu mai rikon gaskiya da
amana, ashe shima zai iyabin son zuciyarsa. Ya
aureta yaci amanar matarsa? Wayyo ni Allah!
Kaico da wannan rayuwar, ranta ya rinka kuna,
makogwaronta ya rinka daci, ta rinka jin wani
yuuu a kanta. Ta dafe kan tana jin wani sara
mata da yake yi, wasu duhu suka gifta ta idonta,
idanuwanta suka rufe tayi baya ta fadi
numfashinta ya dauke.
Umma da ummi suka shigo dakin a lokaci daya,
suka ganta a wannan halin. Gaba daya sukayo
kanta suka dagota suna salati, umma ta
rungumeta tana salati tare da nanata kalmar
innalillahi wa'inna ilaihi raji'un."
yayin da ummi tayi falo da sauri tana salati,
mutane suka yo caa akanta suna tambayarta
lafiya? Ta rude sai fadi take ku kirawo mana
direba, zainab ce ta suma."
sadiya da ni'ima suka saka ihu suka yi cikin
dakin. Dakyar aka samu direban aunty sadiya a
waya, don duka direbobin sun kwashi mutane
suna can daula hotel.
Aka dauki zainab bata san inda kanta yake ba,
suka tafi asibiti. Sunata neman wayar Aliyu gaba
daya wayoyinsa a kulle suke saboda jama'a.
Haka ta Abba da daddy ma du ba'a samu.
A asibiti kuwa gaba daya matan sun cika daki
sunata koke koke, su umma da ummi kuwa da
mama matar baban su zainab, sunyi jugum-
jugum sai salati suke suna hailala a zuciyarsu,
tare da nemawa zainab lafiya cikin zukatansu.
'yan nurse din duk suka korasu falon asibitin,
sannan likita ya fara yiwa zainab taimakon
gaggawa.
Cikin ikon Allah ta farfado, sai likitan yayi mata
allurar bacci donta samu nutsuwa.
Sai sha biyu aka tashi daga walima, sannan aka
samu lambar wayar Abba da daddy. Suna jin
zainab a asibiti suka ce subhanallhi, meya faru
kuma haka? Umma tace, "shidewa tayi ta zube a
sume." to Allah sauwake gamu nan zuwa." Abba
ya binciko Aliyu cikin abokansa yace kaifa muke
jira ka gama sallamar abokanka kazo muje wata
'yar anguwa. Aliyu ya amsa musu cikin
girmamawa, bai tsaya tambayarsu ina zasuje ba.
Aliyu yana gaba kusa da direba, Abba da daddy
suna baya. Direba ya kaisu asibiti, tunda suka
shiga gaban Aliyu yake faduwa, yake tunanin me
kuma ya faru?
Direba ya tsaya suka fito, suka nufi falon asibitin
jikin Aliyu a sanyaye,
yana hango su umma da ummi, ni'ima da sadiya
da hajiya ya fara karanto kalmar "innalillahi
wa'ina ilaihi raji'un.
Daga nan ya rinka tsintar bayanin da ummi take
musu, na abunda ya samu zainab, ran Aliyu ya
baci hankalinsa ya tashi. Bai tsaya sauraron
ummi datake gaya masa likita yace kada a shiga
inda take ba, da saurinsa ya nufi dakin da aka
kwantar da zainab din.
A hankali ya murda kofar ya shiga
da sallamarsa aciki.
Nurse din data ke gadinta tana zaune gefe daya
tana sauraron farkwanta, tana ganin Aliyu tasan
shi sarai, don haka ta mike ta fito.
Aliyu ya tasaya gaban zainab yana kallonta,
yarinyarshi zainab mai kyau da nutsuwa, lallai ta
shiga tashin hankali, yau daya kawai ta rame
haka. Yasa hannu ya shafi fuskarta, tayi fiyau da
ita. Saiya ga takara fari, dan bakinta lebenta
jajaye, siririn dogon hancinta mai tsawo, ga zara-
zaran gashin idonta, baki lafiyayyen gashin girarta
daya kwanta das kan girar.
Ya zame dan kwallin kanta, bakin gashinta mai
tsawo da sheki wanda kullum yake kasancewa
cikin gyara, yaita walwali yana sheki, shiyasa bai
taba hanata zuwa salon ba, yanzu du sati biyu
take zuwa salon, dan ya fuskanci bata damu da
kitsoba saide kalba.
A hankali ya rankwafa kanta ya hada fuskarsa da
tata, cikin kyakyawan lafazi muryansa can cikin
makogwaronsa yace "zeeyta
ki soni don Allah ki kaunaceni, bani da buri
kullum saina yanda zan mallakeki. Zainab kece
rayuwata, tun ranar da kika fado duniya ina
ganinki Allah ya dasa min kaunarki a zuciyata,
kullum kwanan duniya karamin kaunarki akeyi.
Zeeyta ba kya ceto rayuwar yayanki ba, ki
tsamoni daga cikin damuwa ba? Haba zeeyta, ke
kadaice farin cikin rayuwata." aka taba kauren
kofar ya dan ja baya. Likita ne zai shigo, yayi
saurin gyara mata dan kwalinta ya rufa mata
maya fi, wai don kada yaga jikinta.
Likitan yayi sallama, yace, ta farka ne? Yace
mishi a'a ya mika masa hannu suna gaisawa..
aure suka nufu daula hotel, don cin abincin daurin
aure, wato walima ta zama kadai 'yan daurin
aure.
Aliyu ba abunda ya dame shi sai washe baki
yake, yana ta gaisawa da mutane. Da yawa
mutane sunata mamaki, don sun san miskilanci
da rashin yawan dariya irin na Aliyu, amma yanzu
ya kasa rufe bakinsa saboda fara'a da amsa
gaisuwar jama'a da masu sanyawa auren nasu
albarka.
Cikin gida kuw, masu gidan yaransu da manyansu
cikin farin ciki suke da wannan aure na Aliyu da
zainab, saboda kawunan su a hade yake.
Su sadiya dasu ni'ima kuwa sai murna suke suna
zuba shewa da tafi.
Zainab kuwa tana dakin umma kudundune cikin
bacin rai, duniyar tayi mata zafi, ta rasa mai yake
mata dadi. Ita bata ga laifin auntyn ta ba, dole
tace taci amanarta. Mai auntyn ta rage ta dashi?
Ta dauketa kamar 'yar cikinta, amma yau
sakayyar da zata yi mata kenan ta aure mata
miji? Ta sake fashewa da kuka.
Meyasa haka? Meyasa yaya Aliyu mata haka?
Tana ganin yaya Aliyu mai rikon gaskiya da
amana, ashe shima zai iyabin son zuciyarsa. Ya
aureta yaci amanar matarsa? Wayyo ni Allah!
Kaico da wannan rayuwar, ranta ya rinka kuna,
makogwaronta ya rinka daci, ta rinka jin wani
yuuu a kanta. Ta dafe kan tana jin wani sara
mata da yake yi, wasu duhu suka gifta ta idonta,
idanuwanta suka rufe tayi baya ta fadi
numfashinta ya dauke.
Umma da ummi suka shigo dakin a lokaci daya,
suka ganta a wannan halin. Gaba daya sukayo
kanta suka dagota suna salati, umma ta
rungumeta tana salati tare da nanata kalmar
innalillahi wa'inna ilaihi raji'un."
yayin da ummi tayi falo da sauri tana salati,
mutane suka yo caa akanta suna tambayarta
lafiya? Ta rude sai fadi take ku kirawo mana
direba, zainab ce ta suma."
sadiya da ni'ima suka saka ihu suka yi cikin
dakin. Dakyar aka samu direban aunty sadiya a
waya, don duka direbobin sun kwashi mutane
suna can daula hotel.
Aka dauki zainab bata san inda kanta yake ba,
suka tafi asibiti. Sunata neman wayar Aliyu gaba
daya wayoyinsa a kulle suke saboda jama'a.
Haka ta Abba da daddy ma du ba'a samu.
A asibiti kuwa gaba daya matan sun cika daki
sunata koke koke, su umma da ummi kuwa da
mama matar baban su zainab, sunyi jugum-
jugum sai salati suke suna hailala a zuciyarsu,
tare da nemawa zainab lafiya cikin zukatansu.
'yan nurse din duk suka korasu falon asibitin,
sannan likita ya fara yiwa zainab taimakon
gaggawa.
Cikin ikon Allah ta farfado, sai likitan yayi mata
allurar bacci donta samu nutsuwa.
Sai sha biyu aka tashi daga walima, sannan aka
samu lambar wayar Abba da daddy. Suna jin
zainab a asibiti suka ce subhanallhi, meya faru
kuma haka? Umma tace, "shidewa tayi ta zube a
sume." to Allah sauwake gamu nan zuwa." Abba
ya binciko Aliyu cikin abokansa yace kaifa muke
jira ka gama sallamar abokanka kazo muje wata
'yar anguwa. Aliyu ya amsa musu cikin
girmamawa, bai tsaya tambayarsu ina zasuje ba.
Aliyu yana gaba kusa da direba, Abba da daddy
suna baya. Direba ya kaisu asibiti, tunda suka
shiga gaban Aliyu yake faduwa, yake tunanin me
kuma ya faru?
Direba ya tsaya suka fito, suka nufi falon asibitin
jikin Aliyu a sanyaye,
yana hango su umma da ummi, ni'ima da sadiya
da hajiya ya fara karanto kalmar "innalillahi
wa'ina ilaihi raji'un.
Daga nan ya rinka tsintar bayanin da ummi take
musu, na abunda ya samu zainab, ran Aliyu ya
baci hankalinsa ya tashi. Bai tsaya sauraron
ummi datake gaya masa likita yace kada a shiga
inda take ba, da saurinsa ya nufi dakin da aka
kwantar da zainab din.
A hankali ya murda kofar ya shiga
da sallamarsa aciki.
Nurse din data ke gadinta tana zaune gefe daya
tana sauraron farkwanta, tana ganin Aliyu tasan
shi sarai, don haka ta mike ta fito.
Aliyu ya tasaya gaban zainab yana kallonta,
yarinyarshi zainab mai kyau da nutsuwa, lallai ta
shiga tashin hankali, yau daya kawai ta rame
haka. Yasa hannu ya shafi fuskarta, tayi fiyau da
ita. Saiya ga takara fari, dan bakinta lebenta
jajaye, siririn dogon hancinta mai tsawo, ga zara-
zaran gashin idonta, baki lafiyayyen gashin girarta
daya kwanta das kan girar.
Ya zame dan kwallin kanta, bakin gashinta mai
tsawo da sheki wanda kullum yake kasancewa
cikin gyara, yaita walwali yana sheki, shiyasa bai
taba hanata zuwa salon ba, yanzu du sati biyu
take zuwa salon, dan ya fuskanci bata damu da
kitsoba saide kalba.
A hankali ya rankwafa kanta ya hada fuskarsa da
tata, cikin kyakyawan lafazi muryansa can cikin
makogwaronsa yace "zeeyta
ki soni don Allah ki kaunaceni, bani da buri
kullum saina yanda zan mallakeki. Zainab kece
rayuwata, tun ranar da kika fado duniya ina
ganinki Allah ya dasa min kaunarki a zuciyata,
kullum kwanan duniya karamin kaunarki akeyi.
Zeeyta ba kya ceto rayuwar yayanki ba, ki
tsamoni daga cikin damuwa ba? Haba zeeyta, ke
kadaice farin cikin rayuwata." aka taba kauren
kofar ya dan ja baya. Likita ne zai shigo, yayi
saurin gyara mata dan kwalinta ya rufa mata
maya fi, wai don kada yaga jikinta.
Likitan yayi sallama, yace, ta farka ne? Yace
mishi a'a ya mika masa hannu suna gaisawa..