Sashe 17
Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
YACE kada ka damu idan ta farka normal zaka ganta.
Sai dai don Allah adinga kiyaye wa abunda zai bata mata
rai."Aliyu ya gyada kai, yace "insha Allahu za'a kula.
Abba da daddy suka shigo suka tsaya akanta
suna yi mata addu'a da fatan Allah ya bata lafiya.
**** *** ****
saratu da lawisa sun saka mansura a gaba
sunayi mata fanfo zuga iri-iri, lawisa tace, "don
haka nake gaya miki, ki kula da yarinyar nan,
mutum mai shiru-shiru abun tsorone, kinga yanzu
ta kaiki ta baro. Ta gama sanin sirrinki kaf gashi
yanzu ya aureta ta zamo kishiyarki, wallahi ko
kadan kada ki saurara mata, kada ki barta ta
zauna don ba gidan zama tazo ba.
Kuma wallahi ki fito da kudi mu shiga malamai ki
samo kansa, ki mallake shi tsab. Dai-dai da
uwarsa da ubansa ki rabasu dashi, ya zamo babu
wanda yake gabansa saike da yaronki.
Mansura tace, "um! Wannan uban 'yan taurin kan
zai mallaku ne, tun kwanakin baya fa na kashe
kudi akansa, amma inda kika san dutse haka
yake, kwata-kwata baya lankwasuwa. Kuma
halinsa ne bawai ni kadai yake yiwa hakan ba, ita
kanta yarinyar baki ga yanda yake takura mata
ba. Inta jin tausayinta. Ashe shidai akwai abunda
yake kullawa ransa.
Kiga mutum kullum kicin-kicin dashi ba fara'a shi
ba zai zauna ayi wata hira mai dadi dashi ba
ballantana kiga dariyarsa. Wallahi na gaya miki
sai muyi kwana biyu dashi bama magana, don
haka ma tsani naga yazo garin gwanda yana can.
In nayi magana yace wai dan Allah na rabu dashi
ban iya soyayya ba. Du wayewata yana cewa ban
iya soyayya ba, yanzu daya auri wannan
gidahumar kifin rijiyar aina ga ta yanda zasuyi
soyayyar.
Saratu yayarta tace, to inbanda ke da abunki
wannan ai du shi zai koya mata." mansura tace,
tabdijam wannan, wannan dinne zai zauna yana
koya wa mace wani abu, ai shi inbanda isa da iko
da gadara babu abunda ya iya. Shifa ason ransa
komai saide kayi masa yana daga kwance, tunda
naga sangartar tasa tayi yawa kai tsaye inya ce
inyi masa abu nake cewa bazan iya ba.
Lawisa tace wallahi na gaya miki namiji ba dan
goyo bane, ko uwarka ka yanka ka bashi inya
tashi mantawa zaiyi ya zuba ma rashin mutunci."
saratu tace to ba gashi ya mata ta gani, ta rike
'yar tamkar cikinsu don yankan kauna ya tashi ya
aureta.
Mansura tace shekara takwas ina rikon 'yar nan,
ko shekara banyi gidan miji ba ya tattaro min
rikon 'ya, karshe abunda ya sakamin dashi
kenan? Ai duk zasu ci buhun ubansu, mun saka
kafar wando daya dasu. Wallahi saina rushe
zamansu, basu bajin dadin rayuwar, mu zuba su
gani.
**** *** ****
kwanan zainab biyu a asibiti, tayi bacci ta huta
sosai, don data farka take komawa baccin
zuciyarta ta huta ta samu nutsuwa, ta manta da
abunda ya faru.
Dakin cike yake, da mutanen gidan, zainab ta
farka ta yunkura zata mike, umma ta dagota a
hankali tana yi mata sannu. Zainab tayi salati
tace, "umma meye na ganni a asibiti? Tace ishiru
bakida lafiya ne, zo muje ki wanke bakinki."
ta kamata takaita toilet ta wanke mata bakinta
da fuskarta. Ta dawo da ita ta zauna a bakin
gado 'yan uwanta da iyayenta suna mata sannu.
Ummi ta hada mata shayi mai kauri tana bata da
kofin, mama ta zubo mata farfesun kaza ana bata
tanaci, taci dayawa.
Aliyu ne ya turo kofa ya shigo da sallamarsa, tayi
kur ta zubo masa ido tana so ta tuno wani abu,
shikuwa murmushi yake yi, ya daga hannunsa
sama yana yiwa Allah godiya.
Ta kura masa ido tana kallonshi ko kiftawa
batayi, a hankali abun ya fara taro mata cikin
kwakwalwarta, tabbas abunda taji ba mafarki
bane gaskiya ne, yanzu ita matar yayanta Aliyu
ne da gaske? Hawaye ya fara zubowa a idonta,
ta mike a hankali tana takawa sannu a hankali ta
nufi inda Aliyu yake a tsaye, ta durkusa a
gabansa cikin kuka, ta rike kafafuwansa tasa
kanta ajiki tana kuka, da sheshsheka tana cewa,
yaya, haba yayana yaza kayi min haka? Haba
yaya kaine fa uwata? Yaya yaza ka rikide ka
zama mijina? Yaya du abunda uwa take yiwa
'yarta tunda na rasa mamana kai ka fansheta, ka
juye ta a wajena, ka hanani maraicin rashin uwa,
ka zama kaine uwar tawa. Ya zakayi min haka
yayana? Kaifa mijin auntyna ce, matar da na
dauketa kamar 'yar uwata da muke ciki daya, ta
rikeni da gaskiya da rikon amana, zumunci ne mai
karfi tsakanina da ita.
Yaya ya zakayi sanadiyyar rugujewar wannan
zumuncin? yaya don Allah, yaya don girman zatin
Allah ka taimake rayuwata ka sauwakemin
aurenka ka bani ko waye kaga dama."
dakin shiru yayi bakajin motsin komai sai
kukanta, mahaifinta ya taso yazo ya dagata, yace
"haba zainab ina ganinki da hankali da ilimi, ashe
sun zamo na banza tunda zaki iya cewa mijinki
ya sakeki." tace kayi hakuri daddyna
bazan iya zama da auren nan ba, naci amanar
auntyna, da wani ido zan kalli auntyna? Na
yaudareta naci amanarta, naso kaina daddy,
bazan iyaci amanar auntyna ba."
daddyn yace yau, "zainab yau zan gaya miki
abunda baki saniba, tun kafin Aliyu ya san zai
san mansura mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke." ta
juyo a razane ta kalli mahaifinta. Ya daga mata
kai yace kwarai hakane.
Bazan taba mantawa bayan mamanki ta haifi
sadik da
banda lpia ina fatan zky hkri
[9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**7
Sai dai don Allah adinga kiyaye wa abunda zai bata mata
rai."Aliyu ya gyada kai, yace "insha Allahu za'a kula.
Abba da daddy suka shigo suka tsaya akanta
suna yi mata addu'a da fatan Allah ya bata lafiya.
**** *** ****
saratu da lawisa sun saka mansura a gaba
sunayi mata fanfo zuga iri-iri, lawisa tace, "don
haka nake gaya miki, ki kula da yarinyar nan,
mutum mai shiru-shiru abun tsorone, kinga yanzu
ta kaiki ta baro. Ta gama sanin sirrinki kaf gashi
yanzu ya aureta ta zamo kishiyarki, wallahi ko
kadan kada ki saurara mata, kada ki barta ta
zauna don ba gidan zama tazo ba.
Kuma wallahi ki fito da kudi mu shiga malamai ki
samo kansa, ki mallake shi tsab. Dai-dai da
uwarsa da ubansa ki rabasu dashi, ya zamo babu
wanda yake gabansa saike da yaronki.
Mansura tace, "um! Wannan uban 'yan taurin kan
zai mallaku ne, tun kwanakin baya fa na kashe
kudi akansa, amma inda kika san dutse haka
yake, kwata-kwata baya lankwasuwa. Kuma
halinsa ne bawai ni kadai yake yiwa hakan ba, ita
kanta yarinyar baki ga yanda yake takura mata
ba. Inta jin tausayinta. Ashe shidai akwai abunda
yake kullawa ransa.
Kiga mutum kullum kicin-kicin dashi ba fara'a shi
ba zai zauna ayi wata hira mai dadi dashi ba
ballantana kiga dariyarsa. Wallahi na gaya miki
sai muyi kwana biyu dashi bama magana, don
haka ma tsani naga yazo garin gwanda yana can.
In nayi magana yace wai dan Allah na rabu dashi
ban iya soyayya ba. Du wayewata yana cewa ban
iya soyayya ba, yanzu daya auri wannan
gidahumar kifin rijiyar aina ga ta yanda zasuyi
soyayyar.
Saratu yayarta tace, to inbanda ke da abunki
wannan ai du shi zai koya mata." mansura tace,
tabdijam wannan, wannan dinne zai zauna yana
koya wa mace wani abu, ai shi inbanda isa da iko
da gadara babu abunda ya iya. Shifa ason ransa
komai saide kayi masa yana daga kwance, tunda
naga sangartar tasa tayi yawa kai tsaye inya ce
inyi masa abu nake cewa bazan iya ba.
Lawisa tace wallahi na gaya miki namiji ba dan
goyo bane, ko uwarka ka yanka ka bashi inya
tashi mantawa zaiyi ya zuba ma rashin mutunci."
saratu tace to ba gashi ya mata ta gani, ta rike
'yar tamkar cikinsu don yankan kauna ya tashi ya
aureta.
Mansura tace shekara takwas ina rikon 'yar nan,
ko shekara banyi gidan miji ba ya tattaro min
rikon 'ya, karshe abunda ya sakamin dashi
kenan? Ai duk zasu ci buhun ubansu, mun saka
kafar wando daya dasu. Wallahi saina rushe
zamansu, basu bajin dadin rayuwar, mu zuba su
gani.
**** *** ****
kwanan zainab biyu a asibiti, tayi bacci ta huta
sosai, don data farka take komawa baccin
zuciyarta ta huta ta samu nutsuwa, ta manta da
abunda ya faru.
Dakin cike yake, da mutanen gidan, zainab ta
farka ta yunkura zata mike, umma ta dagota a
hankali tana yi mata sannu. Zainab tayi salati
tace, "umma meye na ganni a asibiti? Tace ishiru
bakida lafiya ne, zo muje ki wanke bakinki."
ta kamata takaita toilet ta wanke mata bakinta
da fuskarta. Ta dawo da ita ta zauna a bakin
gado 'yan uwanta da iyayenta suna mata sannu.
Ummi ta hada mata shayi mai kauri tana bata da
kofin, mama ta zubo mata farfesun kaza ana bata
tanaci, taci dayawa.
Aliyu ne ya turo kofa ya shigo da sallamarsa, tayi
kur ta zubo masa ido tana so ta tuno wani abu,
shikuwa murmushi yake yi, ya daga hannunsa
sama yana yiwa Allah godiya.
Ta kura masa ido tana kallonshi ko kiftawa
batayi, a hankali abun ya fara taro mata cikin
kwakwalwarta, tabbas abunda taji ba mafarki
bane gaskiya ne, yanzu ita matar yayanta Aliyu
ne da gaske? Hawaye ya fara zubowa a idonta,
ta mike a hankali tana takawa sannu a hankali ta
nufi inda Aliyu yake a tsaye, ta durkusa a
gabansa cikin kuka, ta rike kafafuwansa tasa
kanta ajiki tana kuka, da sheshsheka tana cewa,
yaya, haba yayana yaza kayi min haka? Haba
yaya kaine fa uwata? Yaya yaza ka rikide ka
zama mijina? Yaya du abunda uwa take yiwa
'yarta tunda na rasa mamana kai ka fansheta, ka
juye ta a wajena, ka hanani maraicin rashin uwa,
ka zama kaine uwar tawa. Ya zakayi min haka
yayana? Kaifa mijin auntyna ce, matar da na
dauketa kamar 'yar uwata da muke ciki daya, ta
rikeni da gaskiya da rikon amana, zumunci ne mai
karfi tsakanina da ita.
Yaya ya zakayi sanadiyyar rugujewar wannan
zumuncin? yaya don Allah, yaya don girman zatin
Allah ka taimake rayuwata ka sauwakemin
aurenka ka bani ko waye kaga dama."
dakin shiru yayi bakajin motsin komai sai
kukanta, mahaifinta ya taso yazo ya dagata, yace
"haba zainab ina ganinki da hankali da ilimi, ashe
sun zamo na banza tunda zaki iya cewa mijinki
ya sakeki." tace kayi hakuri daddyna
bazan iya zama da auren nan ba, naci amanar
auntyna, da wani ido zan kalli auntyna? Na
yaudareta naci amanarta, naso kaina daddy,
bazan iyaci amanar auntyna ba."
daddyn yace yau, "zainab yau zan gaya miki
abunda baki saniba, tun kafin Aliyu ya san zai
san mansura mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke." ta
juyo a razane ta kalli mahaifinta. Ya daga mata
kai yace kwarai hakane.
Bazan taba mantawa bayan mamanki ta haifi
sadik da
banda lpia ina fatan zky hkri
[9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**7