Sashe 9
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani daki ne mai kyau sosai kamar ba dakin asbiti ba suka shiga, Dr Ansar da Dr Asmad ne a gaba sai Abba da Bobbo dake biye da su a baya, wajen gadon suka yi burki tana kwance kamar gawa don babu inda ke motsi a jikinta addu'oi suka fara tofa mata suna addu'ar Allah ya bata lafiya
"Dr zuwa yaushe zata farka?" Dr ya yi tambayar.
"Nan da minti talatin zuwa awa daya." Dr Ansar ya bashi amsa yana kallon agogonsa.
"Ok Allah ya kaimu." Duk suka faɗa.
Sannan suka fita daga dakin aka bar Nenne da Ummi, Nenne ce ta matsa tare da riko hannun Meesha tana mata addu'a, Ummi kam kasa matsawa ta yi sai dai ita dinma addu'a take yi mata daga inda take zaune.
Dr Asmad ne tare da su Abba, yana tsugune gaban su kansa a kasa magana yake son yi amma ya kasa.
"Asmad kamar kana son yin magana ko?" Abba ya tambaya.
Dan sosa kai ya yi ya ce
"Amm dama Abba cewa zan yi ko da Ameesha ta farfaɗo karku sanar mata da matsayin ni mijinta ne."
"Me ya sa za yi haka? Kasan dai dole zata san da maganar ko?" Bobbo ya yi saurin jeho masa tambayar.
"Eh! Bobbo ina son sanar mata da kaina ne, ina rokon alfarma."
"To ai shi kenan tunda kai ka bukaci haka." Abba ya bashi amsa. Daga haka suka shiga hiransu da ciye ciyen.
Cikin dakin kuwa Nenne tana rike da hannun Meesha sai taga hannun ya soma motsi....
```Tofa jama'a ga dai Meesha nan ta fara motsi alamar ta farka shin a wane yanayi zata farfaɗo?
To wai idan ta farfaɗo ta ji maganar aurenta da Dr kuna ganin zata yadda?
Ya Dr zai kasance bayan farfaɗowar Ameesha?
Duk da wannan amsar yana ga Zulayheart Yar gidan Haruna, ku biyoni a hankali zan warware maku komai da yadda Allah, i hearttttt Your My fans```
_*Yar mutan Rano*_
[10/8, 8:15 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
```Har abada bazan manta da Alhairin ku a gareni ba, tabbas ba dan kuba wallahi da yanzu babu sauran maganar labarin SANGARTA, amma kasancewar ku a wajena yasa ku ku ka assasani har labarin ya kawo yanzu, ina kara godiya a gareku Allah ya saka maku da mafificin Alhairin sa ameen da ku nake
KHADIJAH S MUHAMMAD ( Bestyna)
&
BADEEYAR ADAM (Beauty Queen) Allah ya barmu da k'aunar juna```
*Dedicated to LAIFIN WA & SANGARTA FANS* ina son ki sosai😍😍😍
*34*
Da sauri Nenne ta kara damke hannun, cikin zuciyarta tana tasbihi ga Allah a haka duk jikin Ameesha suka fara motsi
"Alhamdulillah!" Nenne tafa murya a bayyane.
Ummi da sai a lokacin ta kula da sauri ta matso tana faɗin
"Kamar tana motsi ko?"
"Eh! Bari a kira Dr." Nenne ta yi maganar tana mik'ewa.
"A'a zauna kawai bari na kira shi." Ummi ta dire maganar tana fita daga dakin ranta fes.
Lokacin da Ummi ta sanar masu duk sun ji dadi, suna addu'ar Allah yasa ta warke kenan, babu kamar Dr da ya ji maganar kamar anyi masa bushara da aljanna, sujada ya yiwa Allah don nuna jin dadin sa, ji ya yi kamar ya ri ga kowa ganin Ameeshar sa, sai dai yana kunyar su Ummi, lokacin da ya dawo tunaninsa wayam yaga wajen ma'ana har su Abba sun tafi ganin Ameesha kenan? Ya yi maganar shi ma yana nufa dakin.
Su kam su Abba kusan a tare suka shiga, kan gadon duk suka nufa tare da zuba mata ido,
"Dr ashe ta farka?" Abba ya tambaya.
"Eh! Ta farka yanzu, sai dai akwai buk'ata ta samu hutu."
"Ku yi hakuri ku dan bani waje." Dr ya yi maganar yana nufa wajen gadon, ya soma duba ta ganin numfashin ta ya dawo normal, sai dai bata buɗe ido ba, ganin haka da Dr Ansar ya yi sai ya ce
"Kin farka?"
A hankali ta soma buɗe ido har ta bude su duka, ta daura idonta akan na Dr Ansar tana masa wani irin kallo na mamaki, sam Dr bai damu da haka ba.
farin ciki ne ya kama Abba da su Nenne ai da sauri suka shiga ɗakin, ganin an turo kofar yasa Ameesha saurin daga kai tana kallon masu shigowa bata ce komai ba sai lumshe ido da ta yi
"Alhamdulillah! Autar Ummi." Ummi ta yi maganar cikin farin ciki.
A karo na biyu ta kuma buɗe ido ta zuba su kan fuskar Ummi, ko kadan bakinta bai motsa da sunan magana ba.
Gaba daya suka fita sai Nenne kawai aka bari a daki, Nenne bata yi musu ba domin babu mamaki Ameesha ta farka tana bukatar wani abu babu kowa.
A inda suke Dr ya same su "Abba ina son magana da ku a office." Dr Ansar ya yi maganar yana tafiya, bayan sa suka bi Ummi da Abba da Bobbo, sai Dr Asmad da ya bisu a baya.
A hankali likitan ya zare farin gilashin da ke fuskarshi, lokaci d'aya kuma ya tattara hankalinshi a kan Su Abba da suke zaune su ma hankalinsu a kanshi.
"Ita cutar Amnesia cuta ce da take samuwa ta hanyar duk wani abu da zai taba Kwakwalwa sannan a rasa hankali gabadaya, musamman idan kai ya bugu sosai. Lokacin da mutum zai dawo hankalinshi sai ya manta dukkan wasu abubuwa da suka faru da shi. Wannan ita ce ake kira Amnesia."
Ya tsahirta hade da kallon su Abba kafin ya ci gaba.
"Cutar ta kasu kashi - kashi, amma kashin da ya fi shahara shi ne: *Anterograde* da *Retrograde*
Antrograde: ita mutum baya iya tuna abinda ya faru da shi nan take, yanzu zai yi abu, yanzu kuma zai manta ya yi."
"Subhanallah! Abba ya fad'a cikin jimami
Likitan ya ci gaba " Retrograde kuwa, mutum ya kan manta komai ne na baya, sai dai ya dora sabon tunani."
"Allah mai iko" Abbah ya kuma fad'a.
"Cutar ba ta da magani da ake sha don a warke, sai dai ko a magance wani ciwo da aka ji a lokacin da tsautsayin ya faru. Kuma ba a yi mata aiki, ma'ana a yanka mutum don kwashe cutar. Dabaru kawai ake amfani dasu wajen magance ta, shi ne tunawa mutum duk abu muhimmi da ya faru da shi, yin wani abu a gabanshi wanda ya saba yi, ci ko shan wani favourite food na shi, sanya kida ko amfani da wani abu me kamshi da ya sani."
Ya dan tsahirta yana duban Asmad da ya yi shiru kamar bai taba jin bayanin cutar ba sai yau.
" Don haka da ma na fada maku, koda kun kawo ta zamu yi amfani da wasu hanyoyi ne don jaraba sa'armu, wanda ba lallai ne kuma ayi nasara ba. Kuma yanzu haka da su din muka yi amfani, inda muka yi nasara Kwakwalwarta ta cafki sauti guda daya, a yanayin yadda ta tashi, muna da tabbacin dawowar tunaninta, amma dai sai a hankali za ta rika tuna wasu abubuwan, abu d'aya zaku yi shi ne, tuna mata duk wani da kuka san tana yi lokacin da take da lafiya, ko kawo abinda kuka san tana so lokacin da take da lafiya....
"To in sha Allah zamu yi kokari Allah ya saka da Alhairi." Abba ne ya yi maganar cikin dakiyar zuciya.
Daga wannan bayanin suka yi sallama da Dr Ansar, cikin mutunci.
Sai da suka leka dakin da Ameesha take, ganin tana bacci yasa suka fita don komawa masaukinsu don su huta, tunanin Abba shi ne da me za'a fara tuni ga Ameesha.
DR bai tsaya jira su Abba ba, ya koma hotel zuciyarsa tana takaicin rashin sa bo da Ameesha kafin ta samu ciwon, domin da ace ya saba da ita da kansa zai rika tuna mata har ta koma dai dai, tunanin Meena ce ta fado masa a fili ya furta
"Dole ana bukatar Meena a wannan lokacin, domin tafi kowa sanin abin da Ameesha ke aikatawa da wanda ta fi so, matsalar bata a kusa da daga yau ta fara..." Da sauri ya juyo, ganin Abba ne ya dafa shi sai ya saki murmushi.
"Tunanin me kake yi haka sai sambatu kake yi?" Abba ya yi tambayar yana rike da kafadar Dr Asmad.
"Babu komai fa Abba."
"Ka kwantar da hankalinka ka ji ko? Mu je ciki ka samu ko abinci ka ci, dubi yadda ka koma lokaci ɗaya?"
"Bana jin yunwa Abba." Dr ya bashi amsa.
"No! Mu je dai ban yadda da kai ba." Cikin murmushi Abba ya dire maganar.
Babu yadda Dr ya iya haka nan ya bi su Abba ciki.
Shigar su dakin ba jimawa wayar Abba ya soma ruri, daukowa ya yi yana mamakin ganin Number Jaheed kuma da Number kasar CAIRO
"Ikon Allah." Ya furta yana kara wayar a kunnensa.
"Kuna airport fa ka ce? To sai ku dauko mota ta kawo ku, Steigenberger Hotel El-Tahrir muna ciki yanzu haka." Daga haka ya kashe wayar.
Ummi ta bishi da kallo ta ce
"Su waye ke airport?"
"Su Jaheed mana, wai sun kasa jure rashin ganin Ameesha, shi ne suka biyo mu."
Murmushi Ummi ta yi a zuciyarta ta ce "ikon Allah soyayyar yan'uwa jini daya ba wasa ba." Amma a fili sai ta ce
"To ai shi kenan tunda sun iso sun kyauta."
"Sun kyauta kuwa, amma da sun yi shawara baza su taho yanzu." Cikin faɗa Abba ya dire maganar yana shiga toilet.
Mintina ƙalilan suka kira Ummi suna sanar mata ga su cikin hotel ɗin, kusan a tare suka fita harabar hotel ɗin, Dr ma da yake ya ji wayar da suke har ya ri ga su zuwa, rungume juna sukai da Jaheed yana tambayarsa jikin Ameesha.
"Alhamdulillah! Dr ya bashi amsa, tare da kai dubansa ga Meena ya ce
"Madallah dake kawarmu wallahi kamar dai kin san muna da buk'atar ki a dai dai wannan lokacin."
Murmushi Meena ta yi ta ce
"Kuma sai gani, na kasa jure rashin ganin Ameesha na kwana biyu."
"Kamar yadda ita dinma yanzu taimakon ki take buk'ata, yanzu dai mu shiga ku samu ku ci abinci ku dan huta sai mu je wajen ta."
"Dr zuwa yaushe zata farka?" Dr ya yi tambayar.
"Nan da minti talatin zuwa awa daya." Dr Ansar ya bashi amsa yana kallon agogonsa.
"Ok Allah ya kaimu." Duk suka faɗa.
Sannan suka fita daga dakin aka bar Nenne da Ummi, Nenne ce ta matsa tare da riko hannun Meesha tana mata addu'a, Ummi kam kasa matsawa ta yi sai dai ita dinma addu'a take yi mata daga inda take zaune.
Dr Asmad ne tare da su Abba, yana tsugune gaban su kansa a kasa magana yake son yi amma ya kasa.
"Asmad kamar kana son yin magana ko?" Abba ya tambaya.
Dan sosa kai ya yi ya ce
"Amm dama Abba cewa zan yi ko da Ameesha ta farfaɗo karku sanar mata da matsayin ni mijinta ne."
"Me ya sa za yi haka? Kasan dai dole zata san da maganar ko?" Bobbo ya yi saurin jeho masa tambayar.
"Eh! Bobbo ina son sanar mata da kaina ne, ina rokon alfarma."
"To ai shi kenan tunda kai ka bukaci haka." Abba ya bashi amsa. Daga haka suka shiga hiransu da ciye ciyen.
Cikin dakin kuwa Nenne tana rike da hannun Meesha sai taga hannun ya soma motsi....
```Tofa jama'a ga dai Meesha nan ta fara motsi alamar ta farka shin a wane yanayi zata farfaɗo?
To wai idan ta farfaɗo ta ji maganar aurenta da Dr kuna ganin zata yadda?
Ya Dr zai kasance bayan farfaɗowar Ameesha?
Duk da wannan amsar yana ga Zulayheart Yar gidan Haruna, ku biyoni a hankali zan warware maku komai da yadda Allah, i hearttttt Your My fans```
_*Yar mutan Rano*_
[10/8, 8:15 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
```Har abada bazan manta da Alhairin ku a gareni ba, tabbas ba dan kuba wallahi da yanzu babu sauran maganar labarin SANGARTA, amma kasancewar ku a wajena yasa ku ku ka assasani har labarin ya kawo yanzu, ina kara godiya a gareku Allah ya saka maku da mafificin Alhairin sa ameen da ku nake
KHADIJAH S MUHAMMAD ( Bestyna)
&
BADEEYAR ADAM (Beauty Queen) Allah ya barmu da k'aunar juna```
*Dedicated to LAIFIN WA & SANGARTA FANS* ina son ki sosai😍😍😍
*34*
Da sauri Nenne ta kara damke hannun, cikin zuciyarta tana tasbihi ga Allah a haka duk jikin Ameesha suka fara motsi
"Alhamdulillah!" Nenne tafa murya a bayyane.
Ummi da sai a lokacin ta kula da sauri ta matso tana faɗin
"Kamar tana motsi ko?"
"Eh! Bari a kira Dr." Nenne ta yi maganar tana mik'ewa.
"A'a zauna kawai bari na kira shi." Ummi ta dire maganar tana fita daga dakin ranta fes.
Lokacin da Ummi ta sanar masu duk sun ji dadi, suna addu'ar Allah yasa ta warke kenan, babu kamar Dr da ya ji maganar kamar anyi masa bushara da aljanna, sujada ya yiwa Allah don nuna jin dadin sa, ji ya yi kamar ya ri ga kowa ganin Ameeshar sa, sai dai yana kunyar su Ummi, lokacin da ya dawo tunaninsa wayam yaga wajen ma'ana har su Abba sun tafi ganin Ameesha kenan? Ya yi maganar shi ma yana nufa dakin.
Su kam su Abba kusan a tare suka shiga, kan gadon duk suka nufa tare da zuba mata ido,
"Dr ashe ta farka?" Abba ya tambaya.
"Eh! Ta farka yanzu, sai dai akwai buk'ata ta samu hutu."
"Ku yi hakuri ku dan bani waje." Dr ya yi maganar yana nufa wajen gadon, ya soma duba ta ganin numfashin ta ya dawo normal, sai dai bata buɗe ido ba, ganin haka da Dr Ansar ya yi sai ya ce
"Kin farka?"
A hankali ta soma buɗe ido har ta bude su duka, ta daura idonta akan na Dr Ansar tana masa wani irin kallo na mamaki, sam Dr bai damu da haka ba.
farin ciki ne ya kama Abba da su Nenne ai da sauri suka shiga ɗakin, ganin an turo kofar yasa Ameesha saurin daga kai tana kallon masu shigowa bata ce komai ba sai lumshe ido da ta yi
"Alhamdulillah! Autar Ummi." Ummi ta yi maganar cikin farin ciki.
A karo na biyu ta kuma buɗe ido ta zuba su kan fuskar Ummi, ko kadan bakinta bai motsa da sunan magana ba.
Gaba daya suka fita sai Nenne kawai aka bari a daki, Nenne bata yi musu ba domin babu mamaki Ameesha ta farka tana bukatar wani abu babu kowa.
A inda suke Dr ya same su "Abba ina son magana da ku a office." Dr Ansar ya yi maganar yana tafiya, bayan sa suka bi Ummi da Abba da Bobbo, sai Dr Asmad da ya bisu a baya.
A hankali likitan ya zare farin gilashin da ke fuskarshi, lokaci d'aya kuma ya tattara hankalinshi a kan Su Abba da suke zaune su ma hankalinsu a kanshi.
"Ita cutar Amnesia cuta ce da take samuwa ta hanyar duk wani abu da zai taba Kwakwalwa sannan a rasa hankali gabadaya, musamman idan kai ya bugu sosai. Lokacin da mutum zai dawo hankalinshi sai ya manta dukkan wasu abubuwa da suka faru da shi. Wannan ita ce ake kira Amnesia."
Ya tsahirta hade da kallon su Abba kafin ya ci gaba.
"Cutar ta kasu kashi - kashi, amma kashin da ya fi shahara shi ne: *Anterograde* da *Retrograde*
Antrograde: ita mutum baya iya tuna abinda ya faru da shi nan take, yanzu zai yi abu, yanzu kuma zai manta ya yi."
"Subhanallah! Abba ya fad'a cikin jimami
Likitan ya ci gaba " Retrograde kuwa, mutum ya kan manta komai ne na baya, sai dai ya dora sabon tunani."
"Allah mai iko" Abbah ya kuma fad'a.
"Cutar ba ta da magani da ake sha don a warke, sai dai ko a magance wani ciwo da aka ji a lokacin da tsautsayin ya faru. Kuma ba a yi mata aiki, ma'ana a yanka mutum don kwashe cutar. Dabaru kawai ake amfani dasu wajen magance ta, shi ne tunawa mutum duk abu muhimmi da ya faru da shi, yin wani abu a gabanshi wanda ya saba yi, ci ko shan wani favourite food na shi, sanya kida ko amfani da wani abu me kamshi da ya sani."
Ya dan tsahirta yana duban Asmad da ya yi shiru kamar bai taba jin bayanin cutar ba sai yau.
" Don haka da ma na fada maku, koda kun kawo ta zamu yi amfani da wasu hanyoyi ne don jaraba sa'armu, wanda ba lallai ne kuma ayi nasara ba. Kuma yanzu haka da su din muka yi amfani, inda muka yi nasara Kwakwalwarta ta cafki sauti guda daya, a yanayin yadda ta tashi, muna da tabbacin dawowar tunaninta, amma dai sai a hankali za ta rika tuna wasu abubuwan, abu d'aya zaku yi shi ne, tuna mata duk wani da kuka san tana yi lokacin da take da lafiya, ko kawo abinda kuka san tana so lokacin da take da lafiya....
"To in sha Allah zamu yi kokari Allah ya saka da Alhairi." Abba ne ya yi maganar cikin dakiyar zuciya.
Daga wannan bayanin suka yi sallama da Dr Ansar, cikin mutunci.
Sai da suka leka dakin da Ameesha take, ganin tana bacci yasa suka fita don komawa masaukinsu don su huta, tunanin Abba shi ne da me za'a fara tuni ga Ameesha.
DR bai tsaya jira su Abba ba, ya koma hotel zuciyarsa tana takaicin rashin sa bo da Ameesha kafin ta samu ciwon, domin da ace ya saba da ita da kansa zai rika tuna mata har ta koma dai dai, tunanin Meena ce ta fado masa a fili ya furta
"Dole ana bukatar Meena a wannan lokacin, domin tafi kowa sanin abin da Ameesha ke aikatawa da wanda ta fi so, matsalar bata a kusa da daga yau ta fara..." Da sauri ya juyo, ganin Abba ne ya dafa shi sai ya saki murmushi.
"Tunanin me kake yi haka sai sambatu kake yi?" Abba ya yi tambayar yana rike da kafadar Dr Asmad.
"Babu komai fa Abba."
"Ka kwantar da hankalinka ka ji ko? Mu je ciki ka samu ko abinci ka ci, dubi yadda ka koma lokaci ɗaya?"
"Bana jin yunwa Abba." Dr ya bashi amsa.
"No! Mu je dai ban yadda da kai ba." Cikin murmushi Abba ya dire maganar.
Babu yadda Dr ya iya haka nan ya bi su Abba ciki.
Shigar su dakin ba jimawa wayar Abba ya soma ruri, daukowa ya yi yana mamakin ganin Number Jaheed kuma da Number kasar CAIRO
"Ikon Allah." Ya furta yana kara wayar a kunnensa.
"Kuna airport fa ka ce? To sai ku dauko mota ta kawo ku, Steigenberger Hotel El-Tahrir muna ciki yanzu haka." Daga haka ya kashe wayar.
Ummi ta bishi da kallo ta ce
"Su waye ke airport?"
"Su Jaheed mana, wai sun kasa jure rashin ganin Ameesha, shi ne suka biyo mu."
Murmushi Ummi ta yi a zuciyarta ta ce "ikon Allah soyayyar yan'uwa jini daya ba wasa ba." Amma a fili sai ta ce
"To ai shi kenan tunda sun iso sun kyauta."
"Sun kyauta kuwa, amma da sun yi shawara baza su taho yanzu." Cikin faɗa Abba ya dire maganar yana shiga toilet.
Mintina ƙalilan suka kira Ummi suna sanar mata ga su cikin hotel ɗin, kusan a tare suka fita harabar hotel ɗin, Dr ma da yake ya ji wayar da suke har ya ri ga su zuwa, rungume juna sukai da Jaheed yana tambayarsa jikin Ameesha.
"Alhamdulillah! Dr ya bashi amsa, tare da kai dubansa ga Meena ya ce
"Madallah dake kawarmu wallahi kamar dai kin san muna da buk'atar ki a dai dai wannan lokacin."
Murmushi Meena ta yi ta ce
"Kuma sai gani, na kasa jure rashin ganin Ameesha na kwana biyu."
"Kamar yadda ita dinma yanzu taimakon ki take buk'ata, yanzu dai mu shiga ku samu ku ci abinci ku dan huta sai mu je wajen ta."