Sashe 10
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ina ai babu maganar hutu kawai a kaimu muga autar Ummi." Ya Jaheed ya yi maganar.
"To ai sai ku je mu kam zamu huta dawowar mu kenan." Abba ne ya yi masu maganar cikin fara'a.
To Abba suka amsa suna shiga cikin mota.
"Ke Meena da kin zauna ki huta, don yanayin jikinki fa."
"A'a Ummi zan iya zuwa, ina son ganin Meesha sosai ne nayi missing ɗin ta."
"To ai shi kenan a dawo lafiya."
Har a lokacin da suka isa asibitin Ameesha bacci take yi, don haka zama suka yi bayan sun gaisa da Nenne, tare da tambayar ta mai jiki.
"Da sauki tun ɗazun da ta farka ta koma bacci har yanzu bata tashi ba."
"Allah yasa ta tashi cikin nasara." Ya Jaheed ya faɗa.
"Amin." Nenne ta amsa tana faɗin
"Oh! Ni yarsu, sannu Meena da k'ok'ari ko nauyin jikinki baki ji?"
Murmushi ta yi ta ce
"Allah Nenne akan Meesha har mantawa nakeyi da wani nauyin jiki."
"Ai naga alama, Allah ya bar kaunar juna kin cika kawa ta gari, samun irin ki sai an tona."
Meena dai murmushi ta yi , tana zaune a ɗakin burinta bai wuce ganin Meesha ta farka, a lokacin kuwa su ya Jaheed da matarsa Badiyyah da mijin Meena Abdul hotel suka koma Meena da Dr sai Nenne kadai ke asibitin.
Sai da Meesha ta share awanni uku tana bacci kafin ta tashi, idonta kyar akan Meena tana kallonta, murmushi Meena ta yi ta ce
"Yes Meena ce Besty friend dinki a gaban ki, ya jikin?"
Ameesha shiru ta yi tana kallon Meena kamar mai son tuno wani, amma ta kasa, ita kam Meena buɗe jaka ta yi ta ciro kwalbar turare wani Meesha tafi kauna da so sunan turaren *Obsessed* a duniya shi ne turaren Meena.
Mik'awa Meesha ta yi cikin murmushi ta ce
"Ga tsaraba na kawo maki, nasan zaki yi farin ciki."
Amsa Meesha ta yi tana jijjuya...
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:16 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*35*
So take ta tuna wani abu, sai dai sam k'wak'walwa ta ta kasa tunowa, Meena ta kula da haka sai kawai cikin sauri ta ce
"Kin manta ranar da muka je sahad, kika ga turaren har ki ka ɗauka! Duba sunan ki gani Obsessed sunansa."
"Meena Obsessed! Ameesha ta maimaita sunan da wata irin murya.
"Yes! Shi fatan kin tuna?"
A hankali lokacin da ta saya turaren ya fara dawo mata, sai dai ta kasa tuna wani abu bayan shi, kanta ne ya yi wani irin sarawa
"Wash! Ta furta a fili
"Mu je ki yi wanka kafin Abba ya zo."
"Abbana? Ina Abba yake Ummi fa?"
"Duk za ki gansu, yanzu dai ta shi ki yi wanka."
Da kanta ta yi wanka, ta shirya cikin doguwar rigar atamfa, sosai kayan sun yi mata kyau, Nenne ta haɗa mata shayi domin babu abinci cikin dakin, Dr Asmad ya tafi kawowa.
"Na gode! Ta faɗa tana kai cup bakinta, tas ta shanye tana aje cup din ta furta
"Alhamdulillah!"
Murmushin nasara Nenne ta yi, domin kuwa tabbas ta yadda Ameesha ta fara samun lafiya, tunda gashi har tana abubuwa da kanta.
"Ga wayar ki Ummi zata yi magana da ke." Meena ce ta yi maganar tana mik'awa Meesha wayar.
Amsar wayar ta yi tana kallon ta, sai kuma ta ɗago kai ta zubawa Meena ido, kafin ta yi magana sai jin sallamar su Abba suka yi, cikin masu amsawa har da Ameesha, wacce ta yi saurin tashi tsaye tana faɗin
"Abbana ina Ummi?" Ta kai karshen maganar tana fadawa jikinsa, don sam bata kula da Ummi ba balle su ya Jaheed.
"Kai masha Allah autar Ummi ta samu sauki, ga Ummin ki da su Jaheed." Abba ya faɗa yana dagota.
Kallon su ta yi tana ganin Ummi da sauri ta nufeta ta rungume ta cikin zallar farin ciki
Duk sun ji dadin ganin yadda ta koma, hira suka shiga yi ita dai Ameesha tana jin su, bata furta komai ba domin bata fahimtar inda hiran tasa gaba, a haka Dr Asmad ya yi sallama lokacin idonta a lumshe yake, jin sallamar sa yasa ta yi saurin bude ido domin dai take ta dauki muryar sa.
Fes ta sauke idonta akan fuskarsa, wani kallo suka wa junansu mai cike da ma'anoni daban daban, murmushi Dr ya saki tare da fadin
"Princess kin tashi?" Wani kasala ta saukar mata jin muryar sa, bata iya bashi amsa ba sai lumshe ido da tayi tare da buɗewa.
Kana kallon Dr zaka iya fahimtar yana cikin zallar farin ciki, da kansa ya zuba mata abincin ya mika mata, amsa ta yi har a time ɗin bata daina kallonsa ba.
Haka dai a hankali sauki ke samuwa ga Ameesha har aka yi kwana uku, a lokacin Dr Ansar ya ce zai sallame su, tunda zuwa yanzu ta fara tuna wasu abubuwan a hankali zata tuna komai.
Suna zaune dukan su, kanta yana saman cinyar Nenne ta yi kamar tana bacci, su kam dama hira suke zumbur kamar an tsikare ta ta mik'e tana waige-waige
"Ummi Ina Najeeb?"
"Najeeb kuma? Wanne Najeeb ɗin?"
"Ummi Najeeb mana yaron Alhaji Mansur abokin Abba?" Ameesha ta fada tana gyara zama.
"Autar Ummi Najeeb yana Nigeria fa, nan muna CAIRO ne."
"Cairo kuma? To mai ya kawo mu?"
"Baki da lafiya ne aka kawo ki."
"Bani da lafiya? To mai ya sameni? To amma Ummi ai ko a ina nake ya kamata yazo, ya zama shi zan fara gani, tunda har Abba ya soma maganar aurenmu da shi."
Shiru suka yi suna sauraron maganar ta, cike da mamaki Meena ce ta yi karfin halin yin magana
"Meesha ya sunana?"
"Haba wannan wane irin tambaya ne? Meena mai kika mai dani?"
"Yi hakuri k'awata zaki iya lissafo min duk mutanen dake dakin nan?"
Harara ta watsawa Meena ta ce
"Eh! Duk na sansu *Ummina, Meena k'awata, ga Abbana* ke duk na sanku na tuna komai.
"Kin tuna komai fa kika ce?"
"Eh! Ta bata amsa kai tsaye.
"A ranar da Abba ya kai ki school, bayan kin fito lacca zaki koma me ya faru da ke a hanya?" Meena ta yi saurin jefa mata tambaya.
"Na fito daga school na je tsallaka titi naji karan wani abu, to nidai daga haka ban kuma sanin komai ba sai yanzu."
"Gud k'awata ta koma normal Alhamdulillah!
"Amma wadinnnan ne ban san ko su waye ba.
Ta nuna su Nenne da Bobbo
"Karki damu suma kin sansu domin su ɗin suna da matukar muhimmanci a rayuwar ki, a hankali zaki san matsayin su a gareki." Ummi ta bata amsa.
Shafa kanta Nenne ta yi ta ce
" karki damu 'yata, ki kwantar da hankalinki."
Gyada kai ta yi tana gyara kwanciya, sallamar Dr ne yasa ta buɗe ido, da mamaki take kallonsa bakinta har yana rawa ta ce
"Dr!
"Na'am Princess ya jikin naki?"
Harara ta aika masa tare da fadin
"Ni kam lafiyata lau."
"Au to yi hakuri lafiyar ki lau, Allah ya kara mana lafiya." Ko kafin ta yi magana ya riga ta
"Abba Dr Ansar fa ya bamu sallama, ko yanzu zamu iya barin asibitin tunda an samu nasara."
"Kai madallah! Yanzu to sai mu hada kayanmu, mu koma hotel zuwa gobe sai mu koma Nigeria."
Duk sun yi na'am da maganar Abba, don haka cikin sauri suka haɗa kayan su, hotel suka koma Ameesha sai zubawa Abba shagwaɓa take a hanya, shi kam biye mata yake domin dai yana cikin farin cikin dawowar ta dai dai.
Suna isa kowa ya shiga dakinsa, Ameesha kam cewa ta yi inda Nenne take nan zata zauna, domin kuwa lokaci ɗaya Allah ya daura mata son Nenne saboda ta kula Nenne tana da kyawun hali.
Suna shiga akan kujera ta zube tana furta
"Wash! Kallonta Nenne ta yi ta ce
"Lafiya?"
"Lafiya lau Nennena."
Da sauri Dr ya kalleta jin yadda ta ce wai Nennenta.
"To ai shi kenan yanzu dai bari na yi wanka, sai mu fita harabar hotel mu dan sha iska, wallahi na gaji da zaman waje daya." Nenne ce mai maganar tana shiga bedroom.
"A fito lafiya Nennena." Meesha ta faɗa tana gyara kwanciya, wayarta ta jawo dan kallon wayar ta yi, cikin phone ta shiga tana duba kiran da kai mata a hankali take sauke Number har ta isa kan wanda take tunanin lambar Dr ne.
Ta ɗan yi mamaki ganin 23 /june /2018, kenan a yadda Meena ta faɗa mata ta yi wata kusan uku tare da ciwon tunda yau dai 7/ August /2018, ikon Allah lallai Allah yana kaunata. Cikin zuciyarta take maganar.
Fita ta yi ta shiga contact, number din Ni'eema ta gani, murmushi ta yi tare da danna mata ki, ringing biyu ta dauka
"Meena ko Meesha?" Shi ne farkon tambayar da ta yi.
Murmushi Meesha ta yi ta ce "Meesha ce fatan kina lafiya?"
Cike da mamaki Ni'eema ta amsa
"Lafiya lau ya jikin?" Da yake Meena ta sanar mata da ciwon Meesha ɗin, kuma lokaci zuwa lokaci takan kira ta tambayi jikin Ameesha, shi yasa yanzu ta cika da mamakin ganin kiran Meesha.
"Na warke fa nikam, ina Fasmir da Yumna?"
"Duk suna lafiya, in sha Allah gobe zamu zo gaida ki."
"Bamu dawo ba, muna Egypt yanzu haka, amma gobe zamu dawo da yaddar Allah."
"Allah ya dawo da ku lafiya." Hira suka ci gaba da yi, ya yin da Dr ya zubawa Ameesha ido, shi dai a duniya tana matukar burgeshi, duk wani abu da zata yi kyau yake mata, yana jin sonta kota ina babu ma kamar yanzu da ya yi wani irin sabo da dumin jikinta.
Muryar Nenne ce ta dawo da shi daga tunanin da ya lula
"Wayar ce dai har yanzu bata kare ba?"
"Eh! Nenne da wata k'awata muke yi, wai gobe zata zo gaidani shi ne na ce mata bamu dawo ba."
"Ayya gaskiya tana da kirki."
"Sosai kam Ni'eema keda kirki, yawwa Nenne tunda kin fito bari na cewa Abba mu zaga gari tunda gobe zamu tafi."
"Babu inda zaki." Dr ne ya yi maganar yana ci gaba da danna wayarsa.
Wani irin juyowa Ameesha ta yi ta ce
"To ai sai ku je mu kam zamu huta dawowar mu kenan." Abba ne ya yi masu maganar cikin fara'a.
To Abba suka amsa suna shiga cikin mota.
"Ke Meena da kin zauna ki huta, don yanayin jikinki fa."
"A'a Ummi zan iya zuwa, ina son ganin Meesha sosai ne nayi missing ɗin ta."
"To ai shi kenan a dawo lafiya."
Har a lokacin da suka isa asibitin Ameesha bacci take yi, don haka zama suka yi bayan sun gaisa da Nenne, tare da tambayar ta mai jiki.
"Da sauki tun ɗazun da ta farka ta koma bacci har yanzu bata tashi ba."
"Allah yasa ta tashi cikin nasara." Ya Jaheed ya faɗa.
"Amin." Nenne ta amsa tana faɗin
"Oh! Ni yarsu, sannu Meena da k'ok'ari ko nauyin jikinki baki ji?"
Murmushi ta yi ta ce
"Allah Nenne akan Meesha har mantawa nakeyi da wani nauyin jiki."
"Ai naga alama, Allah ya bar kaunar juna kin cika kawa ta gari, samun irin ki sai an tona."
Meena dai murmushi ta yi , tana zaune a ɗakin burinta bai wuce ganin Meesha ta farka, a lokacin kuwa su ya Jaheed da matarsa Badiyyah da mijin Meena Abdul hotel suka koma Meena da Dr sai Nenne kadai ke asibitin.
Sai da Meesha ta share awanni uku tana bacci kafin ta tashi, idonta kyar akan Meena tana kallonta, murmushi Meena ta yi ta ce
"Yes Meena ce Besty friend dinki a gaban ki, ya jikin?"
Ameesha shiru ta yi tana kallon Meena kamar mai son tuno wani, amma ta kasa, ita kam Meena buɗe jaka ta yi ta ciro kwalbar turare wani Meesha tafi kauna da so sunan turaren *Obsessed* a duniya shi ne turaren Meena.
Mik'awa Meesha ta yi cikin murmushi ta ce
"Ga tsaraba na kawo maki, nasan zaki yi farin ciki."
Amsa Meesha ta yi tana jijjuya...
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:16 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*35*
So take ta tuna wani abu, sai dai sam k'wak'walwa ta ta kasa tunowa, Meena ta kula da haka sai kawai cikin sauri ta ce
"Kin manta ranar da muka je sahad, kika ga turaren har ki ka ɗauka! Duba sunan ki gani Obsessed sunansa."
"Meena Obsessed! Ameesha ta maimaita sunan da wata irin murya.
"Yes! Shi fatan kin tuna?"
A hankali lokacin da ta saya turaren ya fara dawo mata, sai dai ta kasa tuna wani abu bayan shi, kanta ne ya yi wani irin sarawa
"Wash! Ta furta a fili
"Mu je ki yi wanka kafin Abba ya zo."
"Abbana? Ina Abba yake Ummi fa?"
"Duk za ki gansu, yanzu dai ta shi ki yi wanka."
Da kanta ta yi wanka, ta shirya cikin doguwar rigar atamfa, sosai kayan sun yi mata kyau, Nenne ta haɗa mata shayi domin babu abinci cikin dakin, Dr Asmad ya tafi kawowa.
"Na gode! Ta faɗa tana kai cup bakinta, tas ta shanye tana aje cup din ta furta
"Alhamdulillah!"
Murmushin nasara Nenne ta yi, domin kuwa tabbas ta yadda Ameesha ta fara samun lafiya, tunda gashi har tana abubuwa da kanta.
"Ga wayar ki Ummi zata yi magana da ke." Meena ce ta yi maganar tana mik'awa Meesha wayar.
Amsar wayar ta yi tana kallon ta, sai kuma ta ɗago kai ta zubawa Meena ido, kafin ta yi magana sai jin sallamar su Abba suka yi, cikin masu amsawa har da Ameesha, wacce ta yi saurin tashi tsaye tana faɗin
"Abbana ina Ummi?" Ta kai karshen maganar tana fadawa jikinsa, don sam bata kula da Ummi ba balle su ya Jaheed.
"Kai masha Allah autar Ummi ta samu sauki, ga Ummin ki da su Jaheed." Abba ya faɗa yana dagota.
Kallon su ta yi tana ganin Ummi da sauri ta nufeta ta rungume ta cikin zallar farin ciki
Duk sun ji dadin ganin yadda ta koma, hira suka shiga yi ita dai Ameesha tana jin su, bata furta komai ba domin bata fahimtar inda hiran tasa gaba, a haka Dr Asmad ya yi sallama lokacin idonta a lumshe yake, jin sallamar sa yasa ta yi saurin bude ido domin dai take ta dauki muryar sa.
Fes ta sauke idonta akan fuskarsa, wani kallo suka wa junansu mai cike da ma'anoni daban daban, murmushi Dr ya saki tare da fadin
"Princess kin tashi?" Wani kasala ta saukar mata jin muryar sa, bata iya bashi amsa ba sai lumshe ido da tayi tare da buɗewa.
Kana kallon Dr zaka iya fahimtar yana cikin zallar farin ciki, da kansa ya zuba mata abincin ya mika mata, amsa ta yi har a time ɗin bata daina kallonsa ba.
Haka dai a hankali sauki ke samuwa ga Ameesha har aka yi kwana uku, a lokacin Dr Ansar ya ce zai sallame su, tunda zuwa yanzu ta fara tuna wasu abubuwan a hankali zata tuna komai.
Suna zaune dukan su, kanta yana saman cinyar Nenne ta yi kamar tana bacci, su kam dama hira suke zumbur kamar an tsikare ta ta mik'e tana waige-waige
"Ummi Ina Najeeb?"
"Najeeb kuma? Wanne Najeeb ɗin?"
"Ummi Najeeb mana yaron Alhaji Mansur abokin Abba?" Ameesha ta fada tana gyara zama.
"Autar Ummi Najeeb yana Nigeria fa, nan muna CAIRO ne."
"Cairo kuma? To mai ya kawo mu?"
"Baki da lafiya ne aka kawo ki."
"Bani da lafiya? To mai ya sameni? To amma Ummi ai ko a ina nake ya kamata yazo, ya zama shi zan fara gani, tunda har Abba ya soma maganar aurenmu da shi."
Shiru suka yi suna sauraron maganar ta, cike da mamaki Meena ce ta yi karfin halin yin magana
"Meesha ya sunana?"
"Haba wannan wane irin tambaya ne? Meena mai kika mai dani?"
"Yi hakuri k'awata zaki iya lissafo min duk mutanen dake dakin nan?"
Harara ta watsawa Meena ta ce
"Eh! Duk na sansu *Ummina, Meena k'awata, ga Abbana* ke duk na sanku na tuna komai.
"Kin tuna komai fa kika ce?"
"Eh! Ta bata amsa kai tsaye.
"A ranar da Abba ya kai ki school, bayan kin fito lacca zaki koma me ya faru da ke a hanya?" Meena ta yi saurin jefa mata tambaya.
"Na fito daga school na je tsallaka titi naji karan wani abu, to nidai daga haka ban kuma sanin komai ba sai yanzu."
"Gud k'awata ta koma normal Alhamdulillah!
"Amma wadinnnan ne ban san ko su waye ba.
Ta nuna su Nenne da Bobbo
"Karki damu suma kin sansu domin su ɗin suna da matukar muhimmanci a rayuwar ki, a hankali zaki san matsayin su a gareki." Ummi ta bata amsa.
Shafa kanta Nenne ta yi ta ce
" karki damu 'yata, ki kwantar da hankalinki."
Gyada kai ta yi tana gyara kwanciya, sallamar Dr ne yasa ta buɗe ido, da mamaki take kallonsa bakinta har yana rawa ta ce
"Dr!
"Na'am Princess ya jikin naki?"
Harara ta aika masa tare da fadin
"Ni kam lafiyata lau."
"Au to yi hakuri lafiyar ki lau, Allah ya kara mana lafiya." Ko kafin ta yi magana ya riga ta
"Abba Dr Ansar fa ya bamu sallama, ko yanzu zamu iya barin asibitin tunda an samu nasara."
"Kai madallah! Yanzu to sai mu hada kayanmu, mu koma hotel zuwa gobe sai mu koma Nigeria."
Duk sun yi na'am da maganar Abba, don haka cikin sauri suka haɗa kayan su, hotel suka koma Ameesha sai zubawa Abba shagwaɓa take a hanya, shi kam biye mata yake domin dai yana cikin farin cikin dawowar ta dai dai.
Suna isa kowa ya shiga dakinsa, Ameesha kam cewa ta yi inda Nenne take nan zata zauna, domin kuwa lokaci ɗaya Allah ya daura mata son Nenne saboda ta kula Nenne tana da kyawun hali.
Suna shiga akan kujera ta zube tana furta
"Wash! Kallonta Nenne ta yi ta ce
"Lafiya?"
"Lafiya lau Nennena."
Da sauri Dr ya kalleta jin yadda ta ce wai Nennenta.
"To ai shi kenan yanzu dai bari na yi wanka, sai mu fita harabar hotel mu dan sha iska, wallahi na gaji da zaman waje daya." Nenne ce mai maganar tana shiga bedroom.
"A fito lafiya Nennena." Meesha ta faɗa tana gyara kwanciya, wayarta ta jawo dan kallon wayar ta yi, cikin phone ta shiga tana duba kiran da kai mata a hankali take sauke Number har ta isa kan wanda take tunanin lambar Dr ne.
Ta ɗan yi mamaki ganin 23 /june /2018, kenan a yadda Meena ta faɗa mata ta yi wata kusan uku tare da ciwon tunda yau dai 7/ August /2018, ikon Allah lallai Allah yana kaunata. Cikin zuciyarta take maganar.
Fita ta yi ta shiga contact, number din Ni'eema ta gani, murmushi ta yi tare da danna mata ki, ringing biyu ta dauka
"Meena ko Meesha?" Shi ne farkon tambayar da ta yi.
Murmushi Meesha ta yi ta ce "Meesha ce fatan kina lafiya?"
Cike da mamaki Ni'eema ta amsa
"Lafiya lau ya jikin?" Da yake Meena ta sanar mata da ciwon Meesha ɗin, kuma lokaci zuwa lokaci takan kira ta tambayi jikin Ameesha, shi yasa yanzu ta cika da mamakin ganin kiran Meesha.
"Na warke fa nikam, ina Fasmir da Yumna?"
"Duk suna lafiya, in sha Allah gobe zamu zo gaida ki."
"Bamu dawo ba, muna Egypt yanzu haka, amma gobe zamu dawo da yaddar Allah."
"Allah ya dawo da ku lafiya." Hira suka ci gaba da yi, ya yin da Dr ya zubawa Ameesha ido, shi dai a duniya tana matukar burgeshi, duk wani abu da zata yi kyau yake mata, yana jin sonta kota ina babu ma kamar yanzu da ya yi wani irin sabo da dumin jikinta.
Muryar Nenne ce ta dawo da shi daga tunanin da ya lula
"Wayar ce dai har yanzu bata kare ba?"
"Eh! Nenne da wata k'awata muke yi, wai gobe zata zo gaidani shi ne na ce mata bamu dawo ba."
"Ayya gaskiya tana da kirki."
"Sosai kam Ni'eema keda kirki, yawwa Nenne tunda kin fito bari na cewa Abba mu zaga gari tunda gobe zamu tafi."
"Babu inda zaki." Dr ne ya yi maganar yana ci gaba da danna wayarsa.
Wani irin juyowa Ameesha ta yi ta ce