Sashe 30
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asmad Abubakar ɗan Fullo, babban likita ne wanda duk faɗin garin kano aka san da shi, kawarrene a kan aikin sa, yana aiki a babban asbitin kano.
**********************************
Juyi tayi akan makaɗeɗan gadon ta, tare da kai hannu ta dauki wayar ta dake neman a gaji, idonta fal da bacci ta dubi screen din sunan wacce ta gani ne yasata ɗaukar wayar tare karawa a kunne
"Hello k'awata." Ameesha ta yi maganar tana lumshe ido
Daga ɗaya ɓangaren a ka amsa
"Meesha kina ina ne haka? gani a hospital, tun dazun kin san Dr ɗin da aka ce mana zai zo yi mana practical 8:30 zai shigo lab gashi yanzu 8:20."
Ya mutsa baki Ameesha tayi, kamar wacce ke mata maganar tana kusa da ita tace
"Kinsan Allah Meena na manta da maganar zuwan wani asbiti, yanzu haka da kikeji da gani cikin blanket nake, wayar ki ta tasheni daga bacci."
"Haba Meesha please ki tashi yanzu kiyi sauri ki shirya, kinsan fa irin mutanen nan basa tsayawa jira, kina gani hatta manyan malaman makarantar suna mugun bashi girma."
Tsaki taja tace "to uwar tsugudidi gani nan zuwa, tunda naga kina son takura ni."
Ta karasa maganar tana tashi zaune, Meena kam murmushi tayi, tana mamakin halin Meesha.
Toilet ta faɗa saida ta salle jikinta sannan ta fito, Kai tsaye gaban dress mirror ta nufa, inda kayan kwalliyar ta suke, zama ta yi ta tsantsara kwalliyar ta mai kyau, ta feshe jikinta da turaruka, shiryawa tayi cikin wani doguwar riga kalar blau da ratsin golden, sosai rigar ta k'arbi jikinta, gyale ta yawa fari, sannan ta ɗauki key na motarta, a hankali cikin ta kunta ta soma taka stair ɗin.
Har ta sauka babban falon, Abba da Ummi ne kaɗai a falon suna zaune, hira suke yi, ganin Ameesha ta fito sai Abba ya washe baki yana fad'in
"uwata an tashi?"
"Na tashi Abba Asbiti zan shiga, ina kwana? "
" Lafiya Lau Uwata fatan kin tashi lafiya? "
" Lafiya lau. "
" Ummi ina kwana? "
" Lafiya Ameesha, kin tashi lafiya? "
" Lafiya lau. "ta yi maganar ta na tafiya.
" a'a uwata ba zakiyi break bane? "
" Abba sauri nake yi, zanyi in na shiga."
"OK Allah ya bada sa'a."
"Ameen." ta amsa tana cigaba da tafiya.
Tana fita daga falon kai tsaye inda motocin gidan suke ta nufa, wata zafafaffiyar mota ta dauka, cikin kwarewa taba motar wuta, duk wanda yaga Ameesha cikin motar sai ya kalleta, don motar ta mugun da cewa da ita.
Kai tsaye Asbitin ta nufa, don suna practical ne a Asbitin Malam Aminu dake kano, Ameesha tana karantar Accident prevention and safety,Yau ce ranar da zasu fara practical d'in kuma da alama Dr da zai yi masu practical ɗin bashi da sauki, musamman in mutum ya yi duba da yadda Meena take mata magana.
Tana shiga daret ta nufi inda aka tana da don aje motoci, anan ta faka tata hand bag ɗinta ta ɗauka tare da ciro wayar ta, layin Meena ta soma kira, ringing biyu ta Meena ta dauka.
"Hello Meesha ya kin iso kuwa? "
" Eh gani cikin Asbitin kina ta wajen ina? "
" Please kiyi sauri ina wajen lab yanzu mutumin nan zai shiga, kuma yace koda minti biyu ya riga shiga bazai bar kowa ya shiga ba."
Kashe wayar kawai Ameesha tayi tare da nufa inda Meena take, Meena tana ganin Ameesha tace
"Wallahi Meesha kin kwafsa, yanzu ya shiga muje Allah yasa ya barmu."
Tsaki kawai tayi suka nufi hanyar shiga lab ɗin, gaban Ameesha ne ya faɗi ganin wasu yan class ɗin su a tsaye, suna isa wajen Ameesha ta cusa kai cikin lab ɗinn cikin dakewar zuciya.
Yana tsaye yana masu bayanin kansa sai ganin Ameesha ya yi ta shigo lab ɗin, k'ara bude ido ya yi da kyau ya tabbatar da ita ce dai wacce suka hadu jiya ta masa rashin kunya. Haɗa rai ya yi kamar bai taɓa dariya ba, dama fa shi ɗin ba gwanin dariyar bane, ko da yaushe fuskar sa a haɗe kamar ta sa............."
*Tofa ke Ameeshan Abba da wa Allah ya haɗa ki? Sai kun biyoni don jin ko waye.*
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:01 PM] Zulayheart Rano: *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
*(NWA)*
*SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*5*
"Heeee." ya daka mata wata irin tsawa, da yasa Meena rugawa waje, don Meena fa akwai tsoro.
"Get out side."
"Sorry sir! Wallahi makara dai ko mukayi."
Ameesha ta yi maganar ta na ci gaba da tafiya.
"Baki ba ki ji abinda na ceba ne? ki fita min a lab, tun kafin na shigo ai na faɗa maku doka ta, don haka yi waje ba karatun kike so ba, da har zaki ce Wai makara ku ka yi noises nonsense kawai."
Cikin daure fuska ya ke maganar, in ba kana cikin lab ɗin ba, sai ka rantse da Allah ka ce ba shi ya ke maganar ba, don ko kallon inda take bai yi ba.
Cikin sauri Ameesha ta d'ago da kai, jin yadda ya zageta karaf suka had'a ido da shi, don dama duk maganar da su ke yi ba ta kalle , Shi ba tana ganin shi, sai ta saki wani malalacin tsaki tare da juyawa. Gaba d'aya yan lab ɗin sakin baki suka yi tare da bin ta da kallo.
Dai dai lokacin da za ta fita taji ya na faɗa masu sunan sa.
Wato *Asmad Abubakar ɗan Fullo*
Yace amma anfi sanin sa da *Dr ɗan Fullo*
Maimaita sunan Ameesha ta yi a zuciyar ta wato *"Asmad Abubakar ɗan Fullo* lallai zaka gane kuranka."
Ta k'arasa maganar tana fita daga lab ɗin.
In da Meena ke zaune ta nufa ranta a matukar ɓace, kallon ta Meena tayi tare da fashewa da dariya tace
"Kai Meesha wannan irin abu haka, kinga yadda kika yi kuwa kamar fulawar da ta samu yis da rana? " Meena ta kai Karshen maganar tana ci gaba da dariyar ta.
Wani malalacin kallo Meesha ta watsawa Meena ta ce
" Ke fa Meena baki da kirki me nayi da har kike cewa wata fulawa da ta sami yis da rana? Ke bama wannan ba wai tsoron mutumin can kikaji ne?"
"Sosai ma kina jin irin tsawar da ya zabga mana, kamar an busa algaita taf ai wallahi ya firgita ni, amma ke naga ko a Jikinki ?"
"Kwarai kuwa ko a jikina, dama ina neman sa, kuma ga shi yau Allah ya haɗa ni da shi, don haka wallahi sai na rama marin da yamin jiya." ta kai K'arshen maganar tana huci.
Cikin rashin fahimta Meena ta ce "ban gane ba Meesha dama kin san shi ne?"
Sweet ta ɗauko cikin jakarta tare da jefawa cikin baki ta ce
"Jiya muka haɗu a Sahad naje yin shopping, shi ne fa ya yi min crossing hanya don nayi masa magana sai ya mareni."
Mamaki ya kama Meena, don haka sai kawai ta zubawa Ameesha ido tana kallon ta, zuwa can tace
"Amma Meesha da zaki yadda in na baki shawara, wallahi ki bar mutumin nan, don baki da yadda za ki yi ki rama........."
Hararar da Ameesha ta jefeta da ita, shi ne ya hanata k'arasa maganar da take yi.
"Meena kenan kin manta halina ne hala?"
"A'a shawara dai na ke baki."
"To bani son shawarar rik'e kayan ki, amma ramuwa kuwa babu fashi."
Meena ta buɗe baki da niyyar magana, Ameesha ta yi saurin katse ta tace
"Please karki ce min komai, tashi muje nayi break don ban yi ba na fito, wallahi da nasan wannan nonsense ɗin mutumin ne, to ba zan fito ba sai na yi break d'ina."
Tashi Meena ta yi suka kama hanyar inda Rastaurants d'in da Ameesha ke cin abinci. Dai dai lokacin da suka dawo shi kuma ya ke fitowa daga lab ɗin, harara Ameesha ta cilla masa, sai ko akayi sa'a ya gani, girgiza kai kawai ya yi ya nufi inda motarsa take, hannunsa rike da bag d'in laptop ɗin sa.
Don tsakanin lab ɗin da office ɗinsa da tazara, don haka cikin motarsa ya d'auki hanyar da zata sada shi ga office nashi.
Waje su Ameesha suka samu suka zauna "ta ciro hand out ɗin tana dubawa, don suna da test idan sun koma school, ita ma Meena karatun take yi."
Karfe ɗaya da rabi suka bar Asibitin ,daga nan school suka nufa don suna da test,ba su fito ba sai biyu da arba'in da biyar, lokacin da suka fito a gaji suke bama kamar Ameesha da gaba d'aya bacci takeji, don haka suna fitowa bata tsaya komai ba ta nufi motarta, Allah yasa ma sun gama da laccan yau, burin Ameesha ta isa gida, sai da ta sauke Meena sannan ta wuce.
************************************
Zaune yake cikin kayataccen office d'in sa, iya had'uwa ofis d'in ya yi komai na ciki kalar brown ne da milk, katon table ne a gabansa mai d'auka da file na mutanen da zai duba. gefen dama wani dan gadone irin na duba marasa lafiya, gefen haggu kuma, karamin firij ne mai kyau, ga wani lallausan kafet da ke shimfide a tsakiyar ofis d'in, kai masha Allah komai na ofis d'in abin sha'awa ne.
Kallo d'aya zaki yi masa kasan yana cikin damuwa, don kuwa hannunsa ne cushe cikin tsakiyar kyakkyawan sumar sa dake kwance luf da shi, don yana samun gyara sosai, tsaki kawai yake jerowa a fili, duk motsin da zaiyi sai fuskar Yarinyar can ta bayyana ya rasa dalili.
Dan murmushi ya saki wanda iya karsa leb'e, da ya tuno yadda take magana d'azun, bai tab'a ganin Yarinyar ba sai jiya, amma kuma tunda suka had'u sai matsala ake samu, kamar wasu dai wanda suke jin haushin juna, shifa Yarinyar burgeshi take, musamman in tana rashin kunya.
Wayarsa ya jawo, wacce ke kusa da shi ya soma dialing number
"Hello ku turo su yanzu in duba su, don ina son fita."
Iya abin da ya fad'a kenan ya datse kiran.
Mintina k'alilan ya kammala da duba jama'ar da zai duba, gajiya ya yi sosai ya k'osa ya dan gana da gida, kila in ya sakarwa kansa ruwa zai samu sauki
**********************************
Juyi tayi akan makaɗeɗan gadon ta, tare da kai hannu ta dauki wayar ta dake neman a gaji, idonta fal da bacci ta dubi screen din sunan wacce ta gani ne yasata ɗaukar wayar tare karawa a kunne
"Hello k'awata." Ameesha ta yi maganar tana lumshe ido
Daga ɗaya ɓangaren a ka amsa
"Meesha kina ina ne haka? gani a hospital, tun dazun kin san Dr ɗin da aka ce mana zai zo yi mana practical 8:30 zai shigo lab gashi yanzu 8:20."
Ya mutsa baki Ameesha tayi, kamar wacce ke mata maganar tana kusa da ita tace
"Kinsan Allah Meena na manta da maganar zuwan wani asbiti, yanzu haka da kikeji da gani cikin blanket nake, wayar ki ta tasheni daga bacci."
"Haba Meesha please ki tashi yanzu kiyi sauri ki shirya, kinsan fa irin mutanen nan basa tsayawa jira, kina gani hatta manyan malaman makarantar suna mugun bashi girma."
Tsaki taja tace "to uwar tsugudidi gani nan zuwa, tunda naga kina son takura ni."
Ta karasa maganar tana tashi zaune, Meena kam murmushi tayi, tana mamakin halin Meesha.
Toilet ta faɗa saida ta salle jikinta sannan ta fito, Kai tsaye gaban dress mirror ta nufa, inda kayan kwalliyar ta suke, zama ta yi ta tsantsara kwalliyar ta mai kyau, ta feshe jikinta da turaruka, shiryawa tayi cikin wani doguwar riga kalar blau da ratsin golden, sosai rigar ta k'arbi jikinta, gyale ta yawa fari, sannan ta ɗauki key na motarta, a hankali cikin ta kunta ta soma taka stair ɗin.
Har ta sauka babban falon, Abba da Ummi ne kaɗai a falon suna zaune, hira suke yi, ganin Ameesha ta fito sai Abba ya washe baki yana fad'in
"uwata an tashi?"
"Na tashi Abba Asbiti zan shiga, ina kwana? "
" Lafiya Lau Uwata fatan kin tashi lafiya? "
" Lafiya lau. "
" Ummi ina kwana? "
" Lafiya Ameesha, kin tashi lafiya? "
" Lafiya lau. "ta yi maganar ta na tafiya.
" a'a uwata ba zakiyi break bane? "
" Abba sauri nake yi, zanyi in na shiga."
"OK Allah ya bada sa'a."
"Ameen." ta amsa tana cigaba da tafiya.
Tana fita daga falon kai tsaye inda motocin gidan suke ta nufa, wata zafafaffiyar mota ta dauka, cikin kwarewa taba motar wuta, duk wanda yaga Ameesha cikin motar sai ya kalleta, don motar ta mugun da cewa da ita.
Kai tsaye Asbitin ta nufa, don suna practical ne a Asbitin Malam Aminu dake kano, Ameesha tana karantar Accident prevention and safety,Yau ce ranar da zasu fara practical d'in kuma da alama Dr da zai yi masu practical ɗin bashi da sauki, musamman in mutum ya yi duba da yadda Meena take mata magana.
Tana shiga daret ta nufi inda aka tana da don aje motoci, anan ta faka tata hand bag ɗinta ta ɗauka tare da ciro wayar ta, layin Meena ta soma kira, ringing biyu ta Meena ta dauka.
"Hello Meesha ya kin iso kuwa? "
" Eh gani cikin Asbitin kina ta wajen ina? "
" Please kiyi sauri ina wajen lab yanzu mutumin nan zai shiga, kuma yace koda minti biyu ya riga shiga bazai bar kowa ya shiga ba."
Kashe wayar kawai Ameesha tayi tare da nufa inda Meena take, Meena tana ganin Ameesha tace
"Wallahi Meesha kin kwafsa, yanzu ya shiga muje Allah yasa ya barmu."
Tsaki kawai tayi suka nufi hanyar shiga lab ɗin, gaban Ameesha ne ya faɗi ganin wasu yan class ɗin su a tsaye, suna isa wajen Ameesha ta cusa kai cikin lab ɗinn cikin dakewar zuciya.
Yana tsaye yana masu bayanin kansa sai ganin Ameesha ya yi ta shigo lab ɗin, k'ara bude ido ya yi da kyau ya tabbatar da ita ce dai wacce suka hadu jiya ta masa rashin kunya. Haɗa rai ya yi kamar bai taɓa dariya ba, dama fa shi ɗin ba gwanin dariyar bane, ko da yaushe fuskar sa a haɗe kamar ta sa............."
*Tofa ke Ameeshan Abba da wa Allah ya haɗa ki? Sai kun biyoni don jin ko waye.*
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:01 PM] Zulayheart Rano: *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
*(NWA)*
*SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*5*
"Heeee." ya daka mata wata irin tsawa, da yasa Meena rugawa waje, don Meena fa akwai tsoro.
"Get out side."
"Sorry sir! Wallahi makara dai ko mukayi."
Ameesha ta yi maganar ta na ci gaba da tafiya.
"Baki ba ki ji abinda na ceba ne? ki fita min a lab, tun kafin na shigo ai na faɗa maku doka ta, don haka yi waje ba karatun kike so ba, da har zaki ce Wai makara ku ka yi noises nonsense kawai."
Cikin daure fuska ya ke maganar, in ba kana cikin lab ɗin ba, sai ka rantse da Allah ka ce ba shi ya ke maganar ba, don ko kallon inda take bai yi ba.
Cikin sauri Ameesha ta d'ago da kai, jin yadda ya zageta karaf suka had'a ido da shi, don dama duk maganar da su ke yi ba ta kalle , Shi ba tana ganin shi, sai ta saki wani malalacin tsaki tare da juyawa. Gaba d'aya yan lab ɗin sakin baki suka yi tare da bin ta da kallo.
Dai dai lokacin da za ta fita taji ya na faɗa masu sunan sa.
Wato *Asmad Abubakar ɗan Fullo*
Yace amma anfi sanin sa da *Dr ɗan Fullo*
Maimaita sunan Ameesha ta yi a zuciyar ta wato *"Asmad Abubakar ɗan Fullo* lallai zaka gane kuranka."
Ta k'arasa maganar tana fita daga lab ɗin.
In da Meena ke zaune ta nufa ranta a matukar ɓace, kallon ta Meena tayi tare da fashewa da dariya tace
"Kai Meesha wannan irin abu haka, kinga yadda kika yi kuwa kamar fulawar da ta samu yis da rana? " Meena ta kai Karshen maganar tana ci gaba da dariyar ta.
Wani malalacin kallo Meesha ta watsawa Meena ta ce
" Ke fa Meena baki da kirki me nayi da har kike cewa wata fulawa da ta sami yis da rana? Ke bama wannan ba wai tsoron mutumin can kikaji ne?"
"Sosai ma kina jin irin tsawar da ya zabga mana, kamar an busa algaita taf ai wallahi ya firgita ni, amma ke naga ko a Jikinki ?"
"Kwarai kuwa ko a jikina, dama ina neman sa, kuma ga shi yau Allah ya haɗa ni da shi, don haka wallahi sai na rama marin da yamin jiya." ta kai K'arshen maganar tana huci.
Cikin rashin fahimta Meena ta ce "ban gane ba Meesha dama kin san shi ne?"
Sweet ta ɗauko cikin jakarta tare da jefawa cikin baki ta ce
"Jiya muka haɗu a Sahad naje yin shopping, shi ne fa ya yi min crossing hanya don nayi masa magana sai ya mareni."
Mamaki ya kama Meena, don haka sai kawai ta zubawa Ameesha ido tana kallon ta, zuwa can tace
"Amma Meesha da zaki yadda in na baki shawara, wallahi ki bar mutumin nan, don baki da yadda za ki yi ki rama........."
Hararar da Ameesha ta jefeta da ita, shi ne ya hanata k'arasa maganar da take yi.
"Meena kenan kin manta halina ne hala?"
"A'a shawara dai na ke baki."
"To bani son shawarar rik'e kayan ki, amma ramuwa kuwa babu fashi."
Meena ta buɗe baki da niyyar magana, Ameesha ta yi saurin katse ta tace
"Please karki ce min komai, tashi muje nayi break don ban yi ba na fito, wallahi da nasan wannan nonsense ɗin mutumin ne, to ba zan fito ba sai na yi break d'ina."
Tashi Meena ta yi suka kama hanyar inda Rastaurants d'in da Ameesha ke cin abinci. Dai dai lokacin da suka dawo shi kuma ya ke fitowa daga lab ɗin, harara Ameesha ta cilla masa, sai ko akayi sa'a ya gani, girgiza kai kawai ya yi ya nufi inda motarsa take, hannunsa rike da bag d'in laptop ɗin sa.
Don tsakanin lab ɗin da office ɗinsa da tazara, don haka cikin motarsa ya d'auki hanyar da zata sada shi ga office nashi.
Waje su Ameesha suka samu suka zauna "ta ciro hand out ɗin tana dubawa, don suna da test idan sun koma school, ita ma Meena karatun take yi."
Karfe ɗaya da rabi suka bar Asibitin ,daga nan school suka nufa don suna da test,ba su fito ba sai biyu da arba'in da biyar, lokacin da suka fito a gaji suke bama kamar Ameesha da gaba d'aya bacci takeji, don haka suna fitowa bata tsaya komai ba ta nufi motarta, Allah yasa ma sun gama da laccan yau, burin Ameesha ta isa gida, sai da ta sauke Meena sannan ta wuce.
************************************
Zaune yake cikin kayataccen office d'in sa, iya had'uwa ofis d'in ya yi komai na ciki kalar brown ne da milk, katon table ne a gabansa mai d'auka da file na mutanen da zai duba. gefen dama wani dan gadone irin na duba marasa lafiya, gefen haggu kuma, karamin firij ne mai kyau, ga wani lallausan kafet da ke shimfide a tsakiyar ofis d'in, kai masha Allah komai na ofis d'in abin sha'awa ne.
Kallo d'aya zaki yi masa kasan yana cikin damuwa, don kuwa hannunsa ne cushe cikin tsakiyar kyakkyawan sumar sa dake kwance luf da shi, don yana samun gyara sosai, tsaki kawai yake jerowa a fili, duk motsin da zaiyi sai fuskar Yarinyar can ta bayyana ya rasa dalili.
Dan murmushi ya saki wanda iya karsa leb'e, da ya tuno yadda take magana d'azun, bai tab'a ganin Yarinyar ba sai jiya, amma kuma tunda suka had'u sai matsala ake samu, kamar wasu dai wanda suke jin haushin juna, shifa Yarinyar burgeshi take, musamman in tana rashin kunya.
Wayarsa ya jawo, wacce ke kusa da shi ya soma dialing number
"Hello ku turo su yanzu in duba su, don ina son fita."
Iya abin da ya fad'a kenan ya datse kiran.
Mintina k'alilan ya kammala da duba jama'ar da zai duba, gajiya ya yi sosai ya k'osa ya dan gana da gida, kila in ya sakarwa kansa ruwa zai samu sauki