Sashe 25
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lafiya lau Asmad ya jikin naka?"
"Da sauki ." Asmad ya bashi amsa.
"Allah ya kara lafiya."
"Amin." Ina ji Asmad.
"Ka daure ka shirya zaka rakani wani waje."
Gaban Dr ya yi muguwar faduwa da sauri ya ce
"To Bobbo gani nan zuwa."
"Eh! Yanzu bari na shirya."
"Kai dawa kake magana? Har na ji kana ce wa kuna zuwa, kai da baka da lafiya?" Nenne ta yi tambayar tare da tsare Dr da ido.
"Nenne inji Bobbo wai in shirya zamu fita."
"A haka zaka fita kai da ba daɗi kake ji ba?"
"Ai zan iya tafiya." Dr ya yi maganar cikin karfin hali.
"Ok" kawai Nenne ta iya fada, cikin zuciyarta kuwa cike da mamaki ta ke fadi "oh! Dama don budurwarka tana aure shi ne har da yin ciwo? Lallai ba karamin so Asmad kewa wannan budurwar ba, da a ce tun-tuni tasan kallar son da Asmad kewa wannan budurwa kenan, to da tasan yadda ta yi har Asmad ɗin ya sameta, to an baro shiri tun rani, yanzu kam addu'a zata ke masa Allah ya daura masa hakuri da dangana." Domin dai ɗazun da Hafiz ya zo Ne ta ji hiranmu.
Shi ma Dr Nenne tana fita ya tashi ya shiga toilet, bai wani jima ba ya fito sam jikinsa babu kwari a haka ya fita falon ya samu Bobbo da Nenne
"Ya jikin naka? Bobbo ya kuma tambaya.
"Da sauki."
"Zaka iya tafiyar ma kuwa?"
"Eh! Zan iya." Asmad ya baya Bobbo amsa.
"To shi kenan mu tafi ko?"
"Eh! Kawai Asmad ɗin ya faɗa yana soma tafiya.
Cikin motar Bobbo suka shiga, Dr yasa hannu zai buɗe kenan sai ga Hafiz ya shigo, Bobbo ya yi murmushi ya ce
"Dama dai yanzu nake shirin kiranka ina ce ma mu haɗu a can."
"A'a kuma sai gani tanan."
"Ka kyauta, shiga mu je kawai." Shi Hafiz ya yi kamar yadda Bobbo ya bukata, sannan direba ya soma jan su.
Mamaki sosai ya kama Dr ganin sun nufi unguwar su Ameesha, bai gama yin mamakin ba sai da ya ga sun shiga cikin gidan. "To wai mai Bobbo da Hafiz suke nufi, sun dauko shi zuwa gidan su Ameesha bayan yau aka daura aurenta da wani, ko dai basu san sanadin ta ne ɗazun ciwo ya kama shi ba?" Ya yi wa kansa tambayar da babu amsa. A parking space direba ya faka sannan suka fita dai dai lokacin da ya Jaheed ke fitowa ganin Dr a da sauri ya k'arasa wajen, "a'a Dr Barka da zuwa ku zo lafiya?"
"Lafiya lau, an daura auren lafiya? Please ka yi hakuri wallahi yau ban wuni da lafiya ba ne." Dr ya yi maganar cikin sanyin murya.
"Haba Dr wallahi karka damu ai ciwo ya fi gaban wasa."
" Yi mana iso wajen Alhaji mana! Bobbo ya katse masu jiran da su ke yi.
Babu jimawa ya Jaheed ya dawo yana sanar masu da Abba ya ce su shiga, babban falo aka yi masu masauki zallar farin ciki ne ke tattare da Abba, duk sun zazzauna sannan Bobbo suka kara gaisawa da Bobbo.
Mamaki ya kama Abba ganin Dr tare Allhaji Abubakar ɗin
"A'a Dr yau kaine a gidan namu?"
"Eh! Abba." Dr ya amsa masa cikin girmamawa.
"Ashe kun ma san juna! To ai shi ne ɗan nawa."
"Eh! Mun san juna don shi yake kula da lafiyar yartawa." Domin dai Abba ya yi masa bayanin ciwon Ameesha ɗin.
"To ai shi kenan ma faduwa tazo dai dai da zama."
"Kai madallah! Wallahi wannan abu ya yi sai fatan Allah ya sama abin albarka,domin dai Dr mutumin kirki ne."
Duk wannan maganar suna yin tane bayan fitar su Asmad.
"Alhaji kun zo tafiya da ita ɗin?" Abba ya tambaya.
Murmushi kwance a fuskar Bobbo ya ce a'a ya zo dai ya gaidaka ne, har yanzu bai san abin da ke faruwa ba."
"To ai shi kenan."
"Yanzu abin da za'a yi kawai shi ne, Hafiz zai ɗauki ita Ameesha don shi Asmad gida zai tafi in ya so sai dai ya zo gida ya ganta ina ganin haka zai fi ko?"
"To ni ai bani da wani zaɓi da ya wuce yadda ka ce, fatan alheri zan yi masu da nasara, zuwa karshen sati za su tafi Egypt inda za'a duba Ameesha din."
"Allah ya kaimu, muna godiya da karamci Allah ya saka da Alhairi."
Haka su Bobbo da Abba suka yi ta hiransu.
Bangaren Asmad kuwa can lambun gidan suka koma shi da Hafiz da ya Jaheed hira suke, amma shi Dr daga eh sai a'a kawai ya ke faɗa, so yake ya tambayi ankai Ameesha ko ba'a kai ta ba amma ya kasa. Da ya gaji sai ya mik'e yana faɗin
"Ni kam na gaji da zaman nan, bari na tafi gida insha magani."
"Ayya to sannu Allah ya kara sauki." Suka hada baki wajen faɗa.
"Mu je sai na sauke ka a gidan." Ya Jaheed ya yi maganar yana tashi.
"Hafiz kai ba yanzu zaka tafi ba?"
"Eh! Zan jira Bobbo sai mu tafi." Hafiz ya bashi amsa.
"Ok." Dr ya faɗa yana tafiya.
"Allah ya kara sauki *angon Amee...*
Wani irin juyowa Dr ya yi cikin wani irin yanayi ya ce....
*YAR MUTAN RANO*
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*Na baki kyautar wannan shafin ki yi yadda za ki yi da shi, UMMYN YUSRAH ke ɗin ta daban ce, Ubangiji ya bar k'auna Allah ya raya mana su Yusrah bisa sunna.*
```Ina miko godiya a gareku masoya wannan buk ɗin hakika ina jin dadin yadda kuke gwada min k'aunar da kikewa wannan buk Rabbi ya barmu tare, ina sonku masoya```😍😍😍😍
*LAIFIN WA? & SANGARTA FANS* Ina yinku irin sosai ɗin nan, musamman yadda kuke comment.😘😘😘
*I hearttttt you my besty KHADIJAH S MUHAMMAD*💞
*25*
Sallama ya yi tare da shiga cikin falon, shirun da ya ji shi ya bashi damar sanin babu kowa a falon, don haka sai kawai ya kama hanyar bedroom ɗinsa, kasancewar tun a hanya ya ga an shiga sallah sai shima ya wu ce toilet ya dauro alwala, ba zai iya zuwa masallaci ba, don haka cikin bed din ya tada sallarsa, yana zaune har aka kirayi ishsha aka shiga, bayan ya idar da sallar sai ya koma falo yana mamakin rashin jin motsin Aneesa a gidan.
Bai zame ko ina ba sai bed ɗinta, yana tura kofar ta buɗe can kuryar gado ya ganta ta kudundune cikin bargo, duba ɗaya zaka mata ka tabbatar babu lafiya.
Ganin Dr ai da sauri ta ya ki ce bargon ta nufe shi da dan sassarfa, jikinsa ta faɗa ragafff, saurin tallafeta ya yi yana faɗin
"Subhanallah! My Anee mai ya sameki?"
Ɗago jajayen idanunta ta yi wanda kallo ɗaya zaka mata kasan ta ci kuka
"Hamma daga ina kake?" Ta yi tambayar dai dai da zubowar hawayen da ta ma'kale.
"Ina gidansu Nenne tun safe bana jin dadi." Ya bata amsa yana gyara mata zama a jikinsa.
"Sorry Hamma ai ban san kana gidansu Nenne ba da nazo, hankalina ya tashi da rashin ganinka na kira wayarka duk baka ɗauka ba!"
"Ban kula ba da yake wayoyin duk suna silent ne."
"Please Hamma karka kuma tafiya ka daɗe, ko baka da lafiya ka dawo gida zan fi son haka."
"An gama Madam." Dr ya yi maganar tare da ɗan sakin murmushi.
"Mu je falo ka ci abinci." Aneesa ta yi maganar tana tashi.
Tashi ya yi tana rike da hannunsa suka nufi dining inda ta shirya masa abinci
******
"Kai Alhamdulillah! Wallahi Alhaji na yi matukar farin ciki da jin wannan maganar, Allah ya amsa addu'a ta, ya haɗa Auta da miji na kwarai mai cikar mutunci da hankali." Cikin tsantsan farin ciki Ummi ke wannan maganar.
Shima ɗin Abba zama ya gyara ya ce "ai wato Hajiya wani hani daga Allah baiwa ce, kin ga yanzu babu wanda ya yi zaton haka, amma gashi Allah mai rahama da jin kai ya yi mana canji na Alhairi, addu'ar zaman lafiya kawai zamu ke yi masu."
"Haka ne Alhaji Allah ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyaba."
"Amin." Abba ya amsa.
Suna cikin hiran ne Meesha da Meena suka shigo, Meena zama ta yi a kasa tana gaida su Ummi ya yin da Meesha ta je kan kujerar ta yi kwanciyar ta, ko kallon su Ummi bata yi ba.
"Meena kin kuwa san dawa aka daura auren Auta?" Ummi ta tambaya.
"A'a Ummi" Meena ta bata amsa.
"Ai kin san Dr da yake dubata ko?"
Cikin sauri Meena ta amsa da "Eh!"
"To da shi aka daura auren, bayan rashin mutunci da Alhaji Mansur ya yi mana." Ummi ta k'arasa maganar cikin takaici.
Wani farin ciki ne ya ziyarci Meena jin da Dr aka daura auren Ameesha, wannan abu yana daga cikin burin Meesha sai gashi dama ya samu, sai dai kash Meesha bata san wainar da ake to yawa ba."
"Amma fa Ummi na yi farin ciki sosai Ubangiji ya sa hakane mafi Alhairi."
"Ameen." Ummi ta amsa.
Tashi Meena ta yi tana faɗin
"Ummi bari na tafi sai da safe."
"Allah ya tashemu lafiya."
Bayan tafiyar Meena, Ummi ta umarci Meesha ta shiga bedroom ɗinta. Kin tashi ta yi sai ma kallon Ummi da ta ke yi
"Uwata ta shi ki shiga ciki ki yi sallah sai ki kwanta." Abba ne ya yi maganar yana da ga inda ya ke zaune.
Tashi ta yi tana turo ƙaramin bakinta, mamaki ya kama Ummi ta ce
"Ikon Allah ko dai yarinyar nan da abun da ta ke bukata ne?"
"Babu komai rabu da ita, yanzu zata wuce."
"To Allah ya kyauta." Ummi ta yi maganar bayan wucewar Ameesha.
****
Da mamaki sosai Nenne ta ke kallo Bobbo jin maganar da yake faɗa mata. Wani jin dadi wanda rabonta da shi tun ranar haihuwar Asmad sai yau da ta ji wannan labari ta kuma jin irinsa.
"Alhaji dama ka taɓa zuwa nema masa aure ne?" Nenne ta yi tambayar cikin mamaki.
"Da sauki ." Asmad ya bashi amsa.
"Allah ya kara lafiya."
"Amin." Ina ji Asmad.
"Ka daure ka shirya zaka rakani wani waje."
Gaban Dr ya yi muguwar faduwa da sauri ya ce
"To Bobbo gani nan zuwa."
"Eh! Yanzu bari na shirya."
"Kai dawa kake magana? Har na ji kana ce wa kuna zuwa, kai da baka da lafiya?" Nenne ta yi tambayar tare da tsare Dr da ido.
"Nenne inji Bobbo wai in shirya zamu fita."
"A haka zaka fita kai da ba daɗi kake ji ba?"
"Ai zan iya tafiya." Dr ya yi maganar cikin karfin hali.
"Ok" kawai Nenne ta iya fada, cikin zuciyarta kuwa cike da mamaki ta ke fadi "oh! Dama don budurwarka tana aure shi ne har da yin ciwo? Lallai ba karamin so Asmad kewa wannan budurwar ba, da a ce tun-tuni tasan kallar son da Asmad kewa wannan budurwa kenan, to da tasan yadda ta yi har Asmad ɗin ya sameta, to an baro shiri tun rani, yanzu kam addu'a zata ke masa Allah ya daura masa hakuri da dangana." Domin dai ɗazun da Hafiz ya zo Ne ta ji hiranmu.
Shi ma Dr Nenne tana fita ya tashi ya shiga toilet, bai wani jima ba ya fito sam jikinsa babu kwari a haka ya fita falon ya samu Bobbo da Nenne
"Ya jikin naka? Bobbo ya kuma tambaya.
"Da sauki."
"Zaka iya tafiyar ma kuwa?"
"Eh! Zan iya." Asmad ya baya Bobbo amsa.
"To shi kenan mu tafi ko?"
"Eh! Kawai Asmad ɗin ya faɗa yana soma tafiya.
Cikin motar Bobbo suka shiga, Dr yasa hannu zai buɗe kenan sai ga Hafiz ya shigo, Bobbo ya yi murmushi ya ce
"Dama dai yanzu nake shirin kiranka ina ce ma mu haɗu a can."
"A'a kuma sai gani tanan."
"Ka kyauta, shiga mu je kawai." Shi Hafiz ya yi kamar yadda Bobbo ya bukata, sannan direba ya soma jan su.
Mamaki sosai ya kama Dr ganin sun nufi unguwar su Ameesha, bai gama yin mamakin ba sai da ya ga sun shiga cikin gidan. "To wai mai Bobbo da Hafiz suke nufi, sun dauko shi zuwa gidan su Ameesha bayan yau aka daura aurenta da wani, ko dai basu san sanadin ta ne ɗazun ciwo ya kama shi ba?" Ya yi wa kansa tambayar da babu amsa. A parking space direba ya faka sannan suka fita dai dai lokacin da ya Jaheed ke fitowa ganin Dr a da sauri ya k'arasa wajen, "a'a Dr Barka da zuwa ku zo lafiya?"
"Lafiya lau, an daura auren lafiya? Please ka yi hakuri wallahi yau ban wuni da lafiya ba ne." Dr ya yi maganar cikin sanyin murya.
"Haba Dr wallahi karka damu ai ciwo ya fi gaban wasa."
" Yi mana iso wajen Alhaji mana! Bobbo ya katse masu jiran da su ke yi.
Babu jimawa ya Jaheed ya dawo yana sanar masu da Abba ya ce su shiga, babban falo aka yi masu masauki zallar farin ciki ne ke tattare da Abba, duk sun zazzauna sannan Bobbo suka kara gaisawa da Bobbo.
Mamaki ya kama Abba ganin Dr tare Allhaji Abubakar ɗin
"A'a Dr yau kaine a gidan namu?"
"Eh! Abba." Dr ya amsa masa cikin girmamawa.
"Ashe kun ma san juna! To ai shi ne ɗan nawa."
"Eh! Mun san juna don shi yake kula da lafiyar yartawa." Domin dai Abba ya yi masa bayanin ciwon Ameesha ɗin.
"To ai shi kenan ma faduwa tazo dai dai da zama."
"Kai madallah! Wallahi wannan abu ya yi sai fatan Allah ya sama abin albarka,domin dai Dr mutumin kirki ne."
Duk wannan maganar suna yin tane bayan fitar su Asmad.
"Alhaji kun zo tafiya da ita ɗin?" Abba ya tambaya.
Murmushi kwance a fuskar Bobbo ya ce a'a ya zo dai ya gaidaka ne, har yanzu bai san abin da ke faruwa ba."
"To ai shi kenan."
"Yanzu abin da za'a yi kawai shi ne, Hafiz zai ɗauki ita Ameesha don shi Asmad gida zai tafi in ya so sai dai ya zo gida ya ganta ina ganin haka zai fi ko?"
"To ni ai bani da wani zaɓi da ya wuce yadda ka ce, fatan alheri zan yi masu da nasara, zuwa karshen sati za su tafi Egypt inda za'a duba Ameesha din."
"Allah ya kaimu, muna godiya da karamci Allah ya saka da Alhairi."
Haka su Bobbo da Abba suka yi ta hiransu.
Bangaren Asmad kuwa can lambun gidan suka koma shi da Hafiz da ya Jaheed hira suke, amma shi Dr daga eh sai a'a kawai ya ke faɗa, so yake ya tambayi ankai Ameesha ko ba'a kai ta ba amma ya kasa. Da ya gaji sai ya mik'e yana faɗin
"Ni kam na gaji da zaman nan, bari na tafi gida insha magani."
"Ayya to sannu Allah ya kara sauki." Suka hada baki wajen faɗa.
"Mu je sai na sauke ka a gidan." Ya Jaheed ya yi maganar yana tashi.
"Hafiz kai ba yanzu zaka tafi ba?"
"Eh! Zan jira Bobbo sai mu tafi." Hafiz ya bashi amsa.
"Ok." Dr ya faɗa yana tafiya.
"Allah ya kara sauki *angon Amee...*
Wani irin juyowa Dr ya yi cikin wani irin yanayi ya ce....
*YAR MUTAN RANO*
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*Na baki kyautar wannan shafin ki yi yadda za ki yi da shi, UMMYN YUSRAH ke ɗin ta daban ce, Ubangiji ya bar k'auna Allah ya raya mana su Yusrah bisa sunna.*
```Ina miko godiya a gareku masoya wannan buk ɗin hakika ina jin dadin yadda kuke gwada min k'aunar da kikewa wannan buk Rabbi ya barmu tare, ina sonku masoya```😍😍😍😍
*LAIFIN WA? & SANGARTA FANS* Ina yinku irin sosai ɗin nan, musamman yadda kuke comment.😘😘😘
*I hearttttt you my besty KHADIJAH S MUHAMMAD*💞
*25*
Sallama ya yi tare da shiga cikin falon, shirun da ya ji shi ya bashi damar sanin babu kowa a falon, don haka sai kawai ya kama hanyar bedroom ɗinsa, kasancewar tun a hanya ya ga an shiga sallah sai shima ya wu ce toilet ya dauro alwala, ba zai iya zuwa masallaci ba, don haka cikin bed din ya tada sallarsa, yana zaune har aka kirayi ishsha aka shiga, bayan ya idar da sallar sai ya koma falo yana mamakin rashin jin motsin Aneesa a gidan.
Bai zame ko ina ba sai bed ɗinta, yana tura kofar ta buɗe can kuryar gado ya ganta ta kudundune cikin bargo, duba ɗaya zaka mata ka tabbatar babu lafiya.
Ganin Dr ai da sauri ta ya ki ce bargon ta nufe shi da dan sassarfa, jikinsa ta faɗa ragafff, saurin tallafeta ya yi yana faɗin
"Subhanallah! My Anee mai ya sameki?"
Ɗago jajayen idanunta ta yi wanda kallo ɗaya zaka mata kasan ta ci kuka
"Hamma daga ina kake?" Ta yi tambayar dai dai da zubowar hawayen da ta ma'kale.
"Ina gidansu Nenne tun safe bana jin dadi." Ya bata amsa yana gyara mata zama a jikinsa.
"Sorry Hamma ai ban san kana gidansu Nenne ba da nazo, hankalina ya tashi da rashin ganinka na kira wayarka duk baka ɗauka ba!"
"Ban kula ba da yake wayoyin duk suna silent ne."
"Please Hamma karka kuma tafiya ka daɗe, ko baka da lafiya ka dawo gida zan fi son haka."
"An gama Madam." Dr ya yi maganar tare da ɗan sakin murmushi.
"Mu je falo ka ci abinci." Aneesa ta yi maganar tana tashi.
Tashi ya yi tana rike da hannunsa suka nufi dining inda ta shirya masa abinci
******
"Kai Alhamdulillah! Wallahi Alhaji na yi matukar farin ciki da jin wannan maganar, Allah ya amsa addu'a ta, ya haɗa Auta da miji na kwarai mai cikar mutunci da hankali." Cikin tsantsan farin ciki Ummi ke wannan maganar.
Shima ɗin Abba zama ya gyara ya ce "ai wato Hajiya wani hani daga Allah baiwa ce, kin ga yanzu babu wanda ya yi zaton haka, amma gashi Allah mai rahama da jin kai ya yi mana canji na Alhairi, addu'ar zaman lafiya kawai zamu ke yi masu."
"Haka ne Alhaji Allah ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyaba."
"Amin." Abba ya amsa.
Suna cikin hiran ne Meesha da Meena suka shigo, Meena zama ta yi a kasa tana gaida su Ummi ya yin da Meesha ta je kan kujerar ta yi kwanciyar ta, ko kallon su Ummi bata yi ba.
"Meena kin kuwa san dawa aka daura auren Auta?" Ummi ta tambaya.
"A'a Ummi" Meena ta bata amsa.
"Ai kin san Dr da yake dubata ko?"
Cikin sauri Meena ta amsa da "Eh!"
"To da shi aka daura auren, bayan rashin mutunci da Alhaji Mansur ya yi mana." Ummi ta k'arasa maganar cikin takaici.
Wani farin ciki ne ya ziyarci Meena jin da Dr aka daura auren Ameesha, wannan abu yana daga cikin burin Meesha sai gashi dama ya samu, sai dai kash Meesha bata san wainar da ake to yawa ba."
"Amma fa Ummi na yi farin ciki sosai Ubangiji ya sa hakane mafi Alhairi."
"Ameen." Ummi ta amsa.
Tashi Meena ta yi tana faɗin
"Ummi bari na tafi sai da safe."
"Allah ya tashemu lafiya."
Bayan tafiyar Meena, Ummi ta umarci Meesha ta shiga bedroom ɗinta. Kin tashi ta yi sai ma kallon Ummi da ta ke yi
"Uwata ta shi ki shiga ciki ki yi sallah sai ki kwanta." Abba ne ya yi maganar yana da ga inda ya ke zaune.
Tashi ta yi tana turo ƙaramin bakinta, mamaki ya kama Ummi ta ce
"Ikon Allah ko dai yarinyar nan da abun da ta ke bukata ne?"
"Babu komai rabu da ita, yanzu zata wuce."
"To Allah ya kyauta." Ummi ta yi maganar bayan wucewar Ameesha.
****
Da mamaki sosai Nenne ta ke kallo Bobbo jin maganar da yake faɗa mata. Wani jin dadi wanda rabonta da shi tun ranar haihuwar Asmad sai yau da ta ji wannan labari ta kuma jin irinsa.
"Alhaji dama ka taɓa zuwa nema masa aure ne?" Nenne ta yi tambayar cikin mamaki.