Sashe 26
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai ya yi ya ce "a'a ko ɗaya kawai zuwa wajen ɗaurin auren na yi, dama kafin na tafi sai da muka tattauna da Hafiz, yake sanar min halin da ake ciki, na tausaya ma Asmad sosai haka na tafi wajen ɗaurin auren bani da cikakken nutsuwa, bayan mun je sai baƙon lamari ya bullo, ganin uban yarinyar yana gaf da shiga wani hali sai kawai na yake shawarar a daura da Asmad ɗin, cikin karamin lokaci aka daura." Bobbo ya dire maganar murmushi kwance a fuskarsa.
"Masha Allah! Allah ya tabbatar da Alhairi, na yi farin ciki sosai."
"Ameen." Bobbo ya amsa.
"Amma fa har yanzu Asmad ɗin bai sani ba."
"Hhh! Ka ce *Auren bazatta* ka yi masa?"
"Sosai kuwa."
"To ai shi kenan, muna godiya da hakan, sai yaushe kuma zata tare?"
"Sai bayan sun dawo daga Egypt tukun, don ana son a kaita don duba lafiyarta."
"To Allah ya taimaka, amma ni dai gobe zan je ganinta."
"Allah ya kaimu."
*****
DR ne zaune a bakin gadonsa hannunsa a kan haɓarsa, tunda garin Allah ya wu ye sallah kawai ya yi ya zauna ya soma tunanin Meesha, duk lokacin da ya tuna ya rasata bugun zuciyarsa ke ƙaruwar, ƙaramin tsaki ya ja tare da cusa hannunsa cikin sumarsa.
Ƙaran wayarsa ta dawo da shi cikin nutsuwarsa, kallon wayar ya yi tare da sa hannu ya dauka
"Assalamu Alaikum Nenne ina kwana?"
"Wa'alaikumus salam Asmad lafiya lau ya ƙarfin jikin?"
"Alhamdulillah! Na samu sauki sosai, har masallaci na je."
"Madallah! Allah ya kara sauki, ina son anjima kazo kai da Aneesa."
"Ameen! Insha Allahu zamu zo."
Daga haka su ka yi sallama, Dr kwanciya ya yi tare da lumshe ido cikin wani yanayi mai wuyar fassara, a haka bacci ya dauke shi bai farka ba sai ƙarfe tara. Yana tashi toilet ya nufa wanka ya yi yana fitowa ya shirya cikin wani riga da wando kayan sun amshi jikinsa, ya yi kyau sosai falo ya fita inda ya ke tunanin Aneesa na ciki, ilai kuwa tana zaune a falon cikin kwalliyar ta mai kyau, tana ganin Dr ta saki murmushi ta ce
"Hamma ka yi kyau."
Murmushi ya mayar mata shi ma sannan ya amsa da "na gode."
"Mu je ka yi break kar ka makara." Aneesa ta yi maganar tana fara tafiya. Bin ta a baya ya yi har kan dining din ya zauna ta zuba masa abin da ta haɗa, sannan ita dinma ta zauna
"Ki yi break fa yanzu fita za mu yi mu je gidan su Nenne ." Yana maganar ne yana ci gaba da cin abincinsa.
"To." Aneesa ta amsa kirjinta yana bugawa, haka kawai ta ji hankalinta ya tashi. Sam jikinta babu kwari ta kammala break ɗin, gyale ta dauko suka kama hanya.
Suna shiga mota aka soma kiran Dr ana sanar masa akwai mara lafiya emergency, don haka cikin sauri ya k'arasa da su gidan, lokacin da suka isa gidan Bobbo ya fita, a gaggauce Dr ya gaida Nenne ya fita.
Bayan fitar Dr ne Nenne ta gyara zama tare da kallon Aneesa,
"Aneesa! Nenne ta kira sunanta.
"Na'am Nenne." Cikin nutsuwa ta amsa.
"Kina jina ko? Duk abin da zan sanar maki ki yi haquri domin ya zama dole ki sa ni, ki yi haquri ki dau dangana."
Gyada kai ta yi har yanzu kanta a kasa yake.
"Aneesa jiya aka daura auren Asmad, amma aurensa ba yana nufin cin mutuncin ki bane, babu wani cin zarafi tsakanin ki da Hamma ɗinki, in har wani abu ya biyo baya ki sanar min." Nenne ta fada cikin karfafawa Aneesa gwiwa.
Girgiza kai Aneesa ta ke yi cikin mummunan faduwar gaba, hankalinta ya yi mugun tashi da jin maganar Nenne, addu'a take Allah yasa ba gaske ne abin da ta ji Nenne ta faɗa ba, a fili ta bayyana
"No! Ba haka bane." Ta yi furucin cikin tashin hankali.
"Karki tada hankali ki hakuri Aneesa."
Da sauri Aneesa ta tattaro nutsuwarta, ta tuna a gaban Nenne take, murmushi ta yi wanda da gani kasan gara kuka da shi
"To Nenne Allah ya sa Alhairi." Allah kaɗai yasan ta yadda Aneesa ta haɗa wadannan kalmomin.
"Allah ya maki albarka ya zaunar da ku lafiya."
"Ameen." Kawai Aneesa ta amsa, sai ta mik'e kamar wacce aka tsikara.
"Ina kuma zaki je?"
"Umm Nenne dama zan yi baki ne, shi ne zan koma in dafa masu abinci."
"To ai shi kenan, amma da naso ki wuni mana tunda baƙi ne sai kin kuma zuwa."
Sam Aneesa bata wani tsaya sauraron abin da Nenne ke faɗa ba, kawai ta sa kanta ta yi waje.
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
_*wannan shafin sadaukarwa ne gareki AYSHA WARIZI ki yi yadda za ki yi da shi in yaso ma ki hana kowa ya karanta, indai gaisuwa ta ta sameki Alhamdulillah ina maki fatan Alhairi da nasara a rayuwar ki*_
*Hak'uri nake baku akan rashin ganin post ɗina kullum, hakan nada nasaba da halin da na tsinci kaina, ku taya ni da addu'a Please.*
*Masu kirana da masu yi min text message ina godiya da kulawa, Allah ya bar zumunci*
```Nafee Ankerh korafi```☹
*One in town my Besty, ke kam kin zama jinin jikina k'aunar da nake maki daga Allah ne, Allah ya barmu tare har karshen rayuwa*😍😍
*26*
Sallama ya yi tare da karasawa tsakiyar falon, abin da ya bashi mamaki shi ne yadda bai ji an amsa masa ba, duk da akwai mutum a falon bai damu ba don haka sai ya taka zuwa kan kujera tare da furta "wash! Madam na gaji fa."
Ko daga kai bata yi ba balle yasa ran zata masa magana, Zama ya yi kusan na minti uku yana kallonta tare nazari halin da ta ke ciki, a iya tunaninsa bai mata wani abu wanda har ya bata ranta ba, hasalima cikin farin ciki suka fita har ya barta gidan Nenne.
Tashi ya yi daga inda yake ya matsa kusa da ita yana faɗin
"My Anee me na yi ne? Ya yi tambayar yana kai hannunsa jikinta. Da sauri ta janye jikinta tare da watsa masa wani mugun kallo na tsana zallah
Ta ce "Kar ka taɓa min jiki Hamma.
Da kyar ta hado kalmar domin yadda zuciyarta ke wani irin tafasa, ji take kamar ta shakeshi ta huta.
Da mamaki ya ke kallonta ya ce
"Aneesa me ya faru? Me na yi maki da har zan kai hannuna jikinki ki goce?"
Buɗe ido ta yi tana kallonsa da mamaki mai cike da takaici "wato baka san me ka yi min ba, lallai ma Asmad ɗin nan ka mugun raina min hankali." A zuciyarta ta ke wannan maganar amma a fili sai cewa ta yi.
"Ba kai min komai." A takaice ta yi maganar.
"A'a Aneesa ban yi maki komai ba ki ke fushi da ni, dole akwai dalili Please me ya faru?"
Wannan tambayar tasa na rainin hankali ta bata ranta fiye da jin labarin aurensa, kwafa kawai ta yi ba tare da ta ce komai ba, sai ma mik'ewa da ta yi da niyyar shiga bedroom ɗinta.
Da sauri ya janyo ta ta faɗa jikinsa, hannu yasa ya rungume ta tsam kamar wani zai rabasu.
Kokarin fisge jikinta take tana faɗin "Please Hamma ka barni wallahi na tsaneka ni zaka ciwa amana, me kuma zaka faɗa min?"
Bai damu da maganganun da take faɗa masa ba, shi dai burinsa ya ji laifin da ya aikata mata har ta dauki zafi haka. "Aneesa ki nutsuwa ki faɗa min abin da na yi maki don ban san laifina ba."
Kuka ta rushe masa da shi ta ce
"Hamma ashe kaima kana cikin masu karya da cin amana, Hamma menene bana yi maka da zaka saka min da kishiya?" Da karfi ta k'arasa maganar.
Shi fa maganar ta ma dariya ta sashi amma sai ya dake ganin yadda ta ke kwararar da hawaye "anya kina cikin hankalinki kuwa? An yi maki kishiya? Kuma wa ya faɗa maki?
Dariya ta yi duk da akwai hawaye a idonta, domin dai maganar Hamman ɗinta ya bata mamaki "wato wa ya faɗa maki an yi maki kishiya?" A fili, ta maimaita kalmar ta ce
"Nenne ce ta sanar min kuma kasan dai ba zata min karya ba, ashe dama jiya kana can tare da Amarya ne shi ne da ka dawo ka shirga min karyar baka da lafiya hmmmm! Hamma kenan, yanzu ma kazo ka tsara ni ne bayan ka je wajen matarka, wallahi Hamma na tsaneka." Ta k'arasa maganar tare da rugawa da gudu ta shiga bedroom ɗinta.
Sororo Dr ya yi maganar Aneesa suna masa yawo a kunne "Aure kuma Nenne ta fada mata?" Ya yiwa kansa tambayar da babu amsa. Jagaf ya zauna akan kujera tare da dafe kansa, shi yama rasa tunanin da zai yi, wayarsa ce ta fara ruri don neman a gaji, jiki a saɓule ya kai hannu tare da dauko wayar ganin Number din Hafiz yasa shi ɗauka.
"Ango! Hafiz ya faɗa daga ɓangarensa.
Buɗe ido ya yi tare da gyara wayar a kunnensa ya ce
"Kai fa sai a hankali, wani irin Ango kuma?"
"Ango ka ke mana ko ka manta?" Hafiz ya k'arasa maganar cikin dariya.
Mtss ya ja tsaki ya ce
"Kai wallahi ka faye zolaya da yawa fa, angon Aneesa ba."
"A'a na Ameesha dai." Hafiz ya faɗa.
"Da a ce haka zata faru da nafi kowa murna, amma kash sai dai Ameesha ta min nisa tana karkashin wani." Cikin zuciyarsa ya ke maganar.
Amma a fili sai ya ce
"Please bar maganar nan karka sa na shiga wani ha..." Tun bai gama maganar ba Hafiz ya yi saurin katseshi da fadin
"Kai abokina kana nufin har yanzu baka san an daura auren ka da Ameesha ba?"
Wani irin mik'ewa ya yi daga zaunen da yake ya ce
"Me ka ce?"
"Yes an daura auren ka da Ameesha." Hafiz ya yi maganar kai tsaye.
"Please bana son haka, idan wasa kake min ka daina Ameesha dai ina sonta so na gaskiya, amma na hak'ura da ita." A zafafe Asmad ya k'arasa maganar.
"Masha Allah! Allah ya tabbatar da Alhairi, na yi farin ciki sosai."
"Ameen." Bobbo ya amsa.
"Amma fa har yanzu Asmad ɗin bai sani ba."
"Hhh! Ka ce *Auren bazatta* ka yi masa?"
"Sosai kuwa."
"To ai shi kenan, muna godiya da hakan, sai yaushe kuma zata tare?"
"Sai bayan sun dawo daga Egypt tukun, don ana son a kaita don duba lafiyarta."
"To Allah ya taimaka, amma ni dai gobe zan je ganinta."
"Allah ya kaimu."
*****
DR ne zaune a bakin gadonsa hannunsa a kan haɓarsa, tunda garin Allah ya wu ye sallah kawai ya yi ya zauna ya soma tunanin Meesha, duk lokacin da ya tuna ya rasata bugun zuciyarsa ke ƙaruwar, ƙaramin tsaki ya ja tare da cusa hannunsa cikin sumarsa.
Ƙaran wayarsa ta dawo da shi cikin nutsuwarsa, kallon wayar ya yi tare da sa hannu ya dauka
"Assalamu Alaikum Nenne ina kwana?"
"Wa'alaikumus salam Asmad lafiya lau ya ƙarfin jikin?"
"Alhamdulillah! Na samu sauki sosai, har masallaci na je."
"Madallah! Allah ya kara sauki, ina son anjima kazo kai da Aneesa."
"Ameen! Insha Allahu zamu zo."
Daga haka su ka yi sallama, Dr kwanciya ya yi tare da lumshe ido cikin wani yanayi mai wuyar fassara, a haka bacci ya dauke shi bai farka ba sai ƙarfe tara. Yana tashi toilet ya nufa wanka ya yi yana fitowa ya shirya cikin wani riga da wando kayan sun amshi jikinsa, ya yi kyau sosai falo ya fita inda ya ke tunanin Aneesa na ciki, ilai kuwa tana zaune a falon cikin kwalliyar ta mai kyau, tana ganin Dr ta saki murmushi ta ce
"Hamma ka yi kyau."
Murmushi ya mayar mata shi ma sannan ya amsa da "na gode."
"Mu je ka yi break kar ka makara." Aneesa ta yi maganar tana fara tafiya. Bin ta a baya ya yi har kan dining din ya zauna ta zuba masa abin da ta haɗa, sannan ita dinma ta zauna
"Ki yi break fa yanzu fita za mu yi mu je gidan su Nenne ." Yana maganar ne yana ci gaba da cin abincinsa.
"To." Aneesa ta amsa kirjinta yana bugawa, haka kawai ta ji hankalinta ya tashi. Sam jikinta babu kwari ta kammala break ɗin, gyale ta dauko suka kama hanya.
Suna shiga mota aka soma kiran Dr ana sanar masa akwai mara lafiya emergency, don haka cikin sauri ya k'arasa da su gidan, lokacin da suka isa gidan Bobbo ya fita, a gaggauce Dr ya gaida Nenne ya fita.
Bayan fitar Dr ne Nenne ta gyara zama tare da kallon Aneesa,
"Aneesa! Nenne ta kira sunanta.
"Na'am Nenne." Cikin nutsuwa ta amsa.
"Kina jina ko? Duk abin da zan sanar maki ki yi haquri domin ya zama dole ki sa ni, ki yi haquri ki dau dangana."
Gyada kai ta yi har yanzu kanta a kasa yake.
"Aneesa jiya aka daura auren Asmad, amma aurensa ba yana nufin cin mutuncin ki bane, babu wani cin zarafi tsakanin ki da Hamma ɗinki, in har wani abu ya biyo baya ki sanar min." Nenne ta fada cikin karfafawa Aneesa gwiwa.
Girgiza kai Aneesa ta ke yi cikin mummunan faduwar gaba, hankalinta ya yi mugun tashi da jin maganar Nenne, addu'a take Allah yasa ba gaske ne abin da ta ji Nenne ta faɗa ba, a fili ta bayyana
"No! Ba haka bane." Ta yi furucin cikin tashin hankali.
"Karki tada hankali ki hakuri Aneesa."
Da sauri Aneesa ta tattaro nutsuwarta, ta tuna a gaban Nenne take, murmushi ta yi wanda da gani kasan gara kuka da shi
"To Nenne Allah ya sa Alhairi." Allah kaɗai yasan ta yadda Aneesa ta haɗa wadannan kalmomin.
"Allah ya maki albarka ya zaunar da ku lafiya."
"Ameen." Kawai Aneesa ta amsa, sai ta mik'e kamar wacce aka tsikara.
"Ina kuma zaki je?"
"Umm Nenne dama zan yi baki ne, shi ne zan koma in dafa masu abinci."
"To ai shi kenan, amma da naso ki wuni mana tunda baƙi ne sai kin kuma zuwa."
Sam Aneesa bata wani tsaya sauraron abin da Nenne ke faɗa ba, kawai ta sa kanta ta yi waje.
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
_*wannan shafin sadaukarwa ne gareki AYSHA WARIZI ki yi yadda za ki yi da shi in yaso ma ki hana kowa ya karanta, indai gaisuwa ta ta sameki Alhamdulillah ina maki fatan Alhairi da nasara a rayuwar ki*_
*Hak'uri nake baku akan rashin ganin post ɗina kullum, hakan nada nasaba da halin da na tsinci kaina, ku taya ni da addu'a Please.*
*Masu kirana da masu yi min text message ina godiya da kulawa, Allah ya bar zumunci*
```Nafee Ankerh korafi```☹
*One in town my Besty, ke kam kin zama jinin jikina k'aunar da nake maki daga Allah ne, Allah ya barmu tare har karshen rayuwa*😍😍
*26*
Sallama ya yi tare da karasawa tsakiyar falon, abin da ya bashi mamaki shi ne yadda bai ji an amsa masa ba, duk da akwai mutum a falon bai damu ba don haka sai ya taka zuwa kan kujera tare da furta "wash! Madam na gaji fa."
Ko daga kai bata yi ba balle yasa ran zata masa magana, Zama ya yi kusan na minti uku yana kallonta tare nazari halin da ta ke ciki, a iya tunaninsa bai mata wani abu wanda har ya bata ranta ba, hasalima cikin farin ciki suka fita har ya barta gidan Nenne.
Tashi ya yi daga inda yake ya matsa kusa da ita yana faɗin
"My Anee me na yi ne? Ya yi tambayar yana kai hannunsa jikinta. Da sauri ta janye jikinta tare da watsa masa wani mugun kallo na tsana zallah
Ta ce "Kar ka taɓa min jiki Hamma.
Da kyar ta hado kalmar domin yadda zuciyarta ke wani irin tafasa, ji take kamar ta shakeshi ta huta.
Da mamaki ya ke kallonta ya ce
"Aneesa me ya faru? Me na yi maki da har zan kai hannuna jikinki ki goce?"
Buɗe ido ta yi tana kallonsa da mamaki mai cike da takaici "wato baka san me ka yi min ba, lallai ma Asmad ɗin nan ka mugun raina min hankali." A zuciyarta ta ke wannan maganar amma a fili sai cewa ta yi.
"Ba kai min komai." A takaice ta yi maganar.
"A'a Aneesa ban yi maki komai ba ki ke fushi da ni, dole akwai dalili Please me ya faru?"
Wannan tambayar tasa na rainin hankali ta bata ranta fiye da jin labarin aurensa, kwafa kawai ta yi ba tare da ta ce komai ba, sai ma mik'ewa da ta yi da niyyar shiga bedroom ɗinta.
Da sauri ya janyo ta ta faɗa jikinsa, hannu yasa ya rungume ta tsam kamar wani zai rabasu.
Kokarin fisge jikinta take tana faɗin "Please Hamma ka barni wallahi na tsaneka ni zaka ciwa amana, me kuma zaka faɗa min?"
Bai damu da maganganun da take faɗa masa ba, shi dai burinsa ya ji laifin da ya aikata mata har ta dauki zafi haka. "Aneesa ki nutsuwa ki faɗa min abin da na yi maki don ban san laifina ba."
Kuka ta rushe masa da shi ta ce
"Hamma ashe kaima kana cikin masu karya da cin amana, Hamma menene bana yi maka da zaka saka min da kishiya?" Da karfi ta k'arasa maganar.
Shi fa maganar ta ma dariya ta sashi amma sai ya dake ganin yadda ta ke kwararar da hawaye "anya kina cikin hankalinki kuwa? An yi maki kishiya? Kuma wa ya faɗa maki?
Dariya ta yi duk da akwai hawaye a idonta, domin dai maganar Hamman ɗinta ya bata mamaki "wato wa ya faɗa maki an yi maki kishiya?" A fili, ta maimaita kalmar ta ce
"Nenne ce ta sanar min kuma kasan dai ba zata min karya ba, ashe dama jiya kana can tare da Amarya ne shi ne da ka dawo ka shirga min karyar baka da lafiya hmmmm! Hamma kenan, yanzu ma kazo ka tsara ni ne bayan ka je wajen matarka, wallahi Hamma na tsaneka." Ta k'arasa maganar tare da rugawa da gudu ta shiga bedroom ɗinta.
Sororo Dr ya yi maganar Aneesa suna masa yawo a kunne "Aure kuma Nenne ta fada mata?" Ya yiwa kansa tambayar da babu amsa. Jagaf ya zauna akan kujera tare da dafe kansa, shi yama rasa tunanin da zai yi, wayarsa ce ta fara ruri don neman a gaji, jiki a saɓule ya kai hannu tare da dauko wayar ganin Number din Hafiz yasa shi ɗauka.
"Ango! Hafiz ya faɗa daga ɓangarensa.
Buɗe ido ya yi tare da gyara wayar a kunnensa ya ce
"Kai fa sai a hankali, wani irin Ango kuma?"
"Ango ka ke mana ko ka manta?" Hafiz ya k'arasa maganar cikin dariya.
Mtss ya ja tsaki ya ce
"Kai wallahi ka faye zolaya da yawa fa, angon Aneesa ba."
"A'a na Ameesha dai." Hafiz ya faɗa.
"Da a ce haka zata faru da nafi kowa murna, amma kash sai dai Ameesha ta min nisa tana karkashin wani." Cikin zuciyarsa ya ke maganar.
Amma a fili sai ya ce
"Please bar maganar nan karka sa na shiga wani ha..." Tun bai gama maganar ba Hafiz ya yi saurin katseshi da fadin
"Kai abokina kana nufin har yanzu baka san an daura auren ka da Ameesha ba?"
Wani irin mik'ewa ya yi daga zaunen da yake ya ce
"Me ka ce?"
"Yes an daura auren ka da Ameesha." Hafiz ya yi maganar kai tsaye.
"Please bana son haka, idan wasa kake min ka daina Ameesha dai ina sonta so na gaskiya, amma na hak'ura da ita." A zafafe Asmad ya k'arasa maganar.