Sashe 3
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haba dai My Anee ki dai daure kishi, ko kina son in shiga damuwa ce?"
Dan juya kai ta yi alamar a'a. "Ok zauna bani five minutes bana son ki wahalar min da kanki." Ya ida maganar yana zaunarta a kan kujera kamar wata kwai. Har ya kama hanya sai ya dawo ya sa hannunsa cikin nata ya marairaice fuska ya ce
"My Anee wai har yanzu ban baki ajiya bane?"
"Wane ajiyar?" Ta tambaya tana binsa da kallon rashin fahimta.
"To menene na zaro ido kuma? Nufi na fa shi ne har yanzu baki dauke da cikina?"
Wani irin faduwar gaba ta ji da jin da tambayar da Dr ya mata, ba karamin firgita ta yi ba, amma sai ta dake ta ce
"A'a Hamman har yanzu bani da komai." A tsorace ta bashi amsa.
Murmushi ya saki tare da safa gefen fuskarta ya ce
"Karki damu my Anee zan kokarta yau din nan in baki ajiya, ina son yara ko nawa kika haifa ina sonsu, su Nenne ma zasu sosu kema kin san irin son da Nennena kewa yara, Please Aneesa ki haifa min yara." Cikin sanyin murya ya gama maganar.
"To Hamman Allah ya bamu masu albarka, amma ina tsoron haihuwa akwai wahala."
"Babu wani wahala fa, kuma zan yi maki addu'a Allah ya baki mai sauki My Anee." Cikin kwarin gwiwa ya yi mata maganar.
Daga kai ta yi alamar "to" fuskarta ɗauke da murmushi. Shi kuma Dr ya nufi kicin ɗin ransa fes yana addu'a Allah ya ba Aneesar sa ciki, burinsa bai wuce ganin Aneesa ta dauke da cikinsa ba.
Bangaren Aneesa kuwa, wani farin ciki ne ya rufe ta, musamman yadda Dr ke lallaɓata tabbas ko yanzu tasan tana da wani matsayi a wajen sa, sai dai da wuya ta iya yadda ta zauna da cikinsa domin dai ita fa bata jin zata iya yadda da ciki har ta haihu don bata son ta tsufa da wuri. Duk da ta yadda da halayyar sa da tausayin sa, da wani ne da ko sauraron ta ba zai tsaya ya yi ba, amma Dr mai kyawun hali bai ko duba rashin mutuncin da ta masa ba sai lallashinta yake yi.
Ko minti biyar ɗin bai cika ba ya dawo hannunsa dauke da cup din tea da bread, da kansa ya bata har sai da ta koshi, da kasan ya gyara komai na kicin ɗin da falo sannan suka nufi bedroom ɗinsa, wannan rana dai Aneesa a jikin Dr ta kwana, duk da dai yaso ya kwana wajen bincike asbitin da za'a kai Ameesha, amma ganin yadda Aneesa ta rukungume shi yasa ya hakura.
Washe gari karfe bakwai Dr ya gama kammala shirin sa, har a lokacin Yar Mulkin tana ta sheka bacci, tunda yasan dama akwai sauran dramar jiya sai kawai ya fita da nufi zai biya gidan Nenne ya yi break.
*******
Ko da Dr ya isa asbitin bai samu zama ba don wata mata aka kawo haihuwa ranga ranga don haka cs ya shiga yi mata domin ceto ranta da na abin da ke cikinta. Ya yi nasarar ciro mata yarta lafiyayya katuwa itama matar ta samu lafiya.
Ko da ya fito haka ya ci gaba da kula da sauran mutanen da zai duba, bai samu kansa ba sai karfe biyu. Sallah ya yi sannan ya jawo laptop ɗinsa akan ya soma binciken da yake son yi. Yana son ya samu cikakkiyar information akan asbitin da zai kai domin duba lafiyar Ameesha.
*AS-SALAM INTERNATIONAL HOSPITAL* shi ne sunan asbitin da Abban Ameesha ya faɗa masa sunan, binciken ya soma cikin nutsuwa, sai ga wayar Hafiz ya shigo, ɗauka ya yi cikin sauri magana suka yi sannan ya katse kiran.
Sosai ya duk'ufa neman abin da yake son sani, domin kuwa gaba daya tafiyar tasu bata wuce satin sama. Hamdala ya yi tare da sauke nannauyan ajiyar zuciya alokacin da ya soma karo da abin da yake muradin gani, dan haka sai kawai ya tattara kayansa don zuwa gida domin dai ya gaji kuma yana son ya yi komai a nutse.
Gidan Nenne ya nufa domin ɗazun da safe bai wani zauna suka yi hira ba, sai da ya biya sahad store, lokacin da ya yi karo da inda suka soma haɗuwa da Ameesha wani irin yanayi ya tsinci kansa, sai yaga kamar alokacin abin ke faruwa, tausayin Ameesha na halin da ta samu kanta a ciki ya kuma baibaye shi.
Jiki a sanyaye ya yo masu shopping ɗin sannan ya ɗauki hanya, mintina ƙalilan ya isa gidan, parking ya yi a parking space sannan ya kwashi ledojin da ya saya guda biyu ya yi ciki da su, ya yin da ya bar wanda zai kai wa Aneesa a mota. Cikin falon ya shiga bakinsa dauke da sallama, Nenne dake zaune a falon ta amsa masa.
Dan waro ido ya yi ganin wacce ke zaune kusa da ita, kafin ya gama mamaki har ta iso inda yake, jikinsa ta faɗa kamar kullum tare da ɗago kai tana kallonsa bakinta na faɗin
"Sweety Asmad!
Yar yaji tsigar jikinsa ya tashi, jin Ameesha a jikinsa a yan kwanakin nan yana sashi shiga wani hali, da kyar ya iya dai dai ta nutsuwarsa sannan ya ce
"Princess yaushe kika zo?" Yana maganar ne yana dan janye ta daga jikinsa, don kunyar Nenne ya ji.
Da ido ta bishi har suka dan gana ga kujera, zama ya yi ya zaunar ta gefen sa.
"Ina yini Nenne!"
Asmad ya soma gaidata.
"Lafiya lau ya aiki?"
"Alhamdulillah! Ya bata amsa yana lumshe ido alamar gajiya.
"Nenne wa ya kawo Ameesha?"
"Ni ce naje gidan sai ta ce zata biyoni, sai na taho da ita."
"Ameesha rigima bata yadda da kowa sai ni, yau kuma ta yadda da Nennena." Ya yi maganar cikin farin ciki.
"Aikuwa da ka ganta tun da muka iso take bacci yanzu ba'a daɗe ba ta tashi."
"Eh! Ai dama tunda wannan matsalar ta samu a gare ta yawan bacci ne da ita, fatan ta ci abinci?"
"Eh! Amma fa da kyar da alama bata son cin abinci kam."
"Shi kenan tunda ta ci, dama biyowa na yi mu gaisa daga office nake."
"Madallah! Ai ka kyauta, bari a haɗa maka abinci kamar kana tare da yunwa." Nenne ta yi maganar tana mik'ewa.
Ameesha kam tana ma'kale jikinsa ko k'wak'waran motsi taki yi, lumshe ido kawai ta yi, a hankali ya juyo da fuskarsa gareta ya ce
"Princess!
Shiru ta masa sai dan buɗe ido da ta yi. "Tashi kije ki kwanta kamar baki gama bacci ba ko?"
Ma'kale kafada ta yi ma'ana bazata jeba. Hannu ya kai saman goshinta don yaga kamar batta jin dadi, aiko sai ya ji zafi zauu da sauri ya janye hannunsa yana furta
"Ya ilahi! Meesha baki da lafiya ne? A rude ya ke maganar, dai dai da zuwan Nenne.
"Lafiya kuwa?" Nenne ta tambaya.
"Zazzaɓi ne ya kama Meesha." Ya bata amsa.
"Subhanallah! Zazzaɓi kuma? Sannu Ameesha Allah ya sauwaka, bari na kawo mata magani." Nenne ta dire maganar tana nufa bedroom ɗinta.
Dr da kansa ya bata maganin zazzaɓin, tana gama sha ta soma rufe ido zata kwanta, amma Dr ya hanata sai ta yi minti goma bayan dasha sannan ta zame ta kwanta, kallonta ya yi cikin tausayi ya ce
"Sorry Meesha insha Allahu cikin kwanakin nan zaki warke ki koma kamar yadda kuke a da." Karshen maganar tasa sai da ta shi faduwar gaba, domin tuni Ameesha a watannin baya.
Girgiza kai Nenne ta yi ta ce
"Allah ya bada nasara Ubangiji ya sa a yi cikin nasara, hakika tana cikin yanayi a ce mutum ko ciwo yake yi bai san yadda zai faɗa ba! Kai Allah ya bata lafiya."
"Ameen." Ya amsa yana jawo ture ɗin abinci.
Sosai ya ci abinci ya koshi, yana kammalawa ya, ya zame Ameesha tare da gyara mata kwanciya, yana addu'ar Allah ya bata lafiya cikin zuciyarsa.
"Nenne zan wuce gida."
"To Allah ya kiyaye hanya, Ubangiji ya yi albarka ka gaida Aneesa."
"Amin Nenne zata ji." Ya amsa yana tafiya.
Ko da ya isa gida wanka ya faɗa sannan ya sanya kananun kaya, don kamar yanayin na zafi zafi ne, falo ya koma inda Aneesa ke zaune, kusa da ita ya zauna yana fadin
"Na shigo banji motsin ki ba?"
"Na dan kwanta ne, motsin ka yasa na fito."
"Ki daina kwanciyar yamma babu kyau."
"Na daina." ta bashi amsa tana shigewa jikinsa.
Remort ɗin TV ya dauka yana canza tasha, alokacin shida da minti goma "oh my Anee na manta akwai kayan za'kin da na shigo maki da su suna mota."
Gyara kwanciya ta yi ta ce
"Anjima ka dauko, ina son Jin dumin mijina."
Murmushi mai sauti Dr ya yi yana shafa gashin kanta Sannan ya ce
"Da gaskiyar ki yammata." Shi dai Dr biye mata kawai yake amma tunanin sa yana ga Ameesha musamman yadda ya barota yana son ya kira waya amma baya son ɓata ran Aneesa. Haka dai ya biye mata suka yi ta hiransu har aka kira yi magriba sannan Dr ya nufi masallaci, ita ma ta nufi bedroom ɗinta. Da dare suna zaune hira suke cikin kwanciyar hankali wayar Dr ta soma ruri da sauri ya dauka
Banji mai aka ce masa ba, kawai cewa ya yi "gani nan zuwa." Daga haka ya kashe wayar.
"Bari inje gidan Nenne bazan jima ba zan dawo." Yana maganar ne yana tafiya. Cikin mintina ƙalilan ya isa gidan ko kyakkyawan parking bai yi ba ya kutsa falon.
A tsaye ya samu Nenne "Lafiya kuwa?" Ya tambaya.
"Da sauki amma dai jikin nata sai a hankali yanzu zazzabin ya dawo sabo." Bai gama jin maganar da take faɗa masa ba ya kutsa bedroom din Nenne, kusan a tare suka shiga shi da Nennen.
Can a kan gado ya ga Ameesha kwance rufe da bargo, da sauri ya matsa yana yaye mata bargon, tare da ɗago ta yama manta da wata Nenne rungu...
```don Allah Fans KU yi hakuri da rashin ganin post kullum hakan yana faruwa dalilin bana samun isasshen lokaci, yanzu bana jin dadi ina barar addu'ar ku ```
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:08 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
Dan juya kai ta yi alamar a'a. "Ok zauna bani five minutes bana son ki wahalar min da kanki." Ya ida maganar yana zaunarta a kan kujera kamar wata kwai. Har ya kama hanya sai ya dawo ya sa hannunsa cikin nata ya marairaice fuska ya ce
"My Anee wai har yanzu ban baki ajiya bane?"
"Wane ajiyar?" Ta tambaya tana binsa da kallon rashin fahimta.
"To menene na zaro ido kuma? Nufi na fa shi ne har yanzu baki dauke da cikina?"
Wani irin faduwar gaba ta ji da jin da tambayar da Dr ya mata, ba karamin firgita ta yi ba, amma sai ta dake ta ce
"A'a Hamman har yanzu bani da komai." A tsorace ta bashi amsa.
Murmushi ya saki tare da safa gefen fuskarta ya ce
"Karki damu my Anee zan kokarta yau din nan in baki ajiya, ina son yara ko nawa kika haifa ina sonsu, su Nenne ma zasu sosu kema kin san irin son da Nennena kewa yara, Please Aneesa ki haifa min yara." Cikin sanyin murya ya gama maganar.
"To Hamman Allah ya bamu masu albarka, amma ina tsoron haihuwa akwai wahala."
"Babu wani wahala fa, kuma zan yi maki addu'a Allah ya baki mai sauki My Anee." Cikin kwarin gwiwa ya yi mata maganar.
Daga kai ta yi alamar "to" fuskarta ɗauke da murmushi. Shi kuma Dr ya nufi kicin ɗin ransa fes yana addu'a Allah ya ba Aneesar sa ciki, burinsa bai wuce ganin Aneesa ta dauke da cikinsa ba.
Bangaren Aneesa kuwa, wani farin ciki ne ya rufe ta, musamman yadda Dr ke lallaɓata tabbas ko yanzu tasan tana da wani matsayi a wajen sa, sai dai da wuya ta iya yadda ta zauna da cikinsa domin dai ita fa bata jin zata iya yadda da ciki har ta haihu don bata son ta tsufa da wuri. Duk da ta yadda da halayyar sa da tausayin sa, da wani ne da ko sauraron ta ba zai tsaya ya yi ba, amma Dr mai kyawun hali bai ko duba rashin mutuncin da ta masa ba sai lallashinta yake yi.
Ko minti biyar ɗin bai cika ba ya dawo hannunsa dauke da cup din tea da bread, da kansa ya bata har sai da ta koshi, da kasan ya gyara komai na kicin ɗin da falo sannan suka nufi bedroom ɗinsa, wannan rana dai Aneesa a jikin Dr ta kwana, duk da dai yaso ya kwana wajen bincike asbitin da za'a kai Ameesha, amma ganin yadda Aneesa ta rukungume shi yasa ya hakura.
Washe gari karfe bakwai Dr ya gama kammala shirin sa, har a lokacin Yar Mulkin tana ta sheka bacci, tunda yasan dama akwai sauran dramar jiya sai kawai ya fita da nufi zai biya gidan Nenne ya yi break.
*******
Ko da Dr ya isa asbitin bai samu zama ba don wata mata aka kawo haihuwa ranga ranga don haka cs ya shiga yi mata domin ceto ranta da na abin da ke cikinta. Ya yi nasarar ciro mata yarta lafiyayya katuwa itama matar ta samu lafiya.
Ko da ya fito haka ya ci gaba da kula da sauran mutanen da zai duba, bai samu kansa ba sai karfe biyu. Sallah ya yi sannan ya jawo laptop ɗinsa akan ya soma binciken da yake son yi. Yana son ya samu cikakkiyar information akan asbitin da zai kai domin duba lafiyar Ameesha.
*AS-SALAM INTERNATIONAL HOSPITAL* shi ne sunan asbitin da Abban Ameesha ya faɗa masa sunan, binciken ya soma cikin nutsuwa, sai ga wayar Hafiz ya shigo, ɗauka ya yi cikin sauri magana suka yi sannan ya katse kiran.
Sosai ya duk'ufa neman abin da yake son sani, domin kuwa gaba daya tafiyar tasu bata wuce satin sama. Hamdala ya yi tare da sauke nannauyan ajiyar zuciya alokacin da ya soma karo da abin da yake muradin gani, dan haka sai kawai ya tattara kayansa don zuwa gida domin dai ya gaji kuma yana son ya yi komai a nutse.
Gidan Nenne ya nufa domin ɗazun da safe bai wani zauna suka yi hira ba, sai da ya biya sahad store, lokacin da ya yi karo da inda suka soma haɗuwa da Ameesha wani irin yanayi ya tsinci kansa, sai yaga kamar alokacin abin ke faruwa, tausayin Ameesha na halin da ta samu kanta a ciki ya kuma baibaye shi.
Jiki a sanyaye ya yo masu shopping ɗin sannan ya ɗauki hanya, mintina ƙalilan ya isa gidan, parking ya yi a parking space sannan ya kwashi ledojin da ya saya guda biyu ya yi ciki da su, ya yin da ya bar wanda zai kai wa Aneesa a mota. Cikin falon ya shiga bakinsa dauke da sallama, Nenne dake zaune a falon ta amsa masa.
Dan waro ido ya yi ganin wacce ke zaune kusa da ita, kafin ya gama mamaki har ta iso inda yake, jikinsa ta faɗa kamar kullum tare da ɗago kai tana kallonsa bakinta na faɗin
"Sweety Asmad!
Yar yaji tsigar jikinsa ya tashi, jin Ameesha a jikinsa a yan kwanakin nan yana sashi shiga wani hali, da kyar ya iya dai dai ta nutsuwarsa sannan ya ce
"Princess yaushe kika zo?" Yana maganar ne yana dan janye ta daga jikinsa, don kunyar Nenne ya ji.
Da ido ta bishi har suka dan gana ga kujera, zama ya yi ya zaunar ta gefen sa.
"Ina yini Nenne!"
Asmad ya soma gaidata.
"Lafiya lau ya aiki?"
"Alhamdulillah! Ya bata amsa yana lumshe ido alamar gajiya.
"Nenne wa ya kawo Ameesha?"
"Ni ce naje gidan sai ta ce zata biyoni, sai na taho da ita."
"Ameesha rigima bata yadda da kowa sai ni, yau kuma ta yadda da Nennena." Ya yi maganar cikin farin ciki.
"Aikuwa da ka ganta tun da muka iso take bacci yanzu ba'a daɗe ba ta tashi."
"Eh! Ai dama tunda wannan matsalar ta samu a gare ta yawan bacci ne da ita, fatan ta ci abinci?"
"Eh! Amma fa da kyar da alama bata son cin abinci kam."
"Shi kenan tunda ta ci, dama biyowa na yi mu gaisa daga office nake."
"Madallah! Ai ka kyauta, bari a haɗa maka abinci kamar kana tare da yunwa." Nenne ta yi maganar tana mik'ewa.
Ameesha kam tana ma'kale jikinsa ko k'wak'waran motsi taki yi, lumshe ido kawai ta yi, a hankali ya juyo da fuskarsa gareta ya ce
"Princess!
Shiru ta masa sai dan buɗe ido da ta yi. "Tashi kije ki kwanta kamar baki gama bacci ba ko?"
Ma'kale kafada ta yi ma'ana bazata jeba. Hannu ya kai saman goshinta don yaga kamar batta jin dadi, aiko sai ya ji zafi zauu da sauri ya janye hannunsa yana furta
"Ya ilahi! Meesha baki da lafiya ne? A rude ya ke maganar, dai dai da zuwan Nenne.
"Lafiya kuwa?" Nenne ta tambaya.
"Zazzaɓi ne ya kama Meesha." Ya bata amsa.
"Subhanallah! Zazzaɓi kuma? Sannu Ameesha Allah ya sauwaka, bari na kawo mata magani." Nenne ta dire maganar tana nufa bedroom ɗinta.
Dr da kansa ya bata maganin zazzaɓin, tana gama sha ta soma rufe ido zata kwanta, amma Dr ya hanata sai ta yi minti goma bayan dasha sannan ta zame ta kwanta, kallonta ya yi cikin tausayi ya ce
"Sorry Meesha insha Allahu cikin kwanakin nan zaki warke ki koma kamar yadda kuke a da." Karshen maganar tasa sai da ta shi faduwar gaba, domin tuni Ameesha a watannin baya.
Girgiza kai Nenne ta yi ta ce
"Allah ya bada nasara Ubangiji ya sa a yi cikin nasara, hakika tana cikin yanayi a ce mutum ko ciwo yake yi bai san yadda zai faɗa ba! Kai Allah ya bata lafiya."
"Ameen." Ya amsa yana jawo ture ɗin abinci.
Sosai ya ci abinci ya koshi, yana kammalawa ya, ya zame Ameesha tare da gyara mata kwanciya, yana addu'ar Allah ya bata lafiya cikin zuciyarsa.
"Nenne zan wuce gida."
"To Allah ya kiyaye hanya, Ubangiji ya yi albarka ka gaida Aneesa."
"Amin Nenne zata ji." Ya amsa yana tafiya.
Ko da ya isa gida wanka ya faɗa sannan ya sanya kananun kaya, don kamar yanayin na zafi zafi ne, falo ya koma inda Aneesa ke zaune, kusa da ita ya zauna yana fadin
"Na shigo banji motsin ki ba?"
"Na dan kwanta ne, motsin ka yasa na fito."
"Ki daina kwanciyar yamma babu kyau."
"Na daina." ta bashi amsa tana shigewa jikinsa.
Remort ɗin TV ya dauka yana canza tasha, alokacin shida da minti goma "oh my Anee na manta akwai kayan za'kin da na shigo maki da su suna mota."
Gyara kwanciya ta yi ta ce
"Anjima ka dauko, ina son Jin dumin mijina."
Murmushi mai sauti Dr ya yi yana shafa gashin kanta Sannan ya ce
"Da gaskiyar ki yammata." Shi dai Dr biye mata kawai yake amma tunanin sa yana ga Ameesha musamman yadda ya barota yana son ya kira waya amma baya son ɓata ran Aneesa. Haka dai ya biye mata suka yi ta hiransu har aka kira yi magriba sannan Dr ya nufi masallaci, ita ma ta nufi bedroom ɗinta. Da dare suna zaune hira suke cikin kwanciyar hankali wayar Dr ta soma ruri da sauri ya dauka
Banji mai aka ce masa ba, kawai cewa ya yi "gani nan zuwa." Daga haka ya kashe wayar.
"Bari inje gidan Nenne bazan jima ba zan dawo." Yana maganar ne yana tafiya. Cikin mintina ƙalilan ya isa gidan ko kyakkyawan parking bai yi ba ya kutsa falon.
A tsaye ya samu Nenne "Lafiya kuwa?" Ya tambaya.
"Da sauki amma dai jikin nata sai a hankali yanzu zazzabin ya dawo sabo." Bai gama jin maganar da take faɗa masa ba ya kutsa bedroom din Nenne, kusan a tare suka shiga shi da Nennen.
Can a kan gado ya ga Ameesha kwance rufe da bargo, da sauri ya matsa yana yaye mata bargon, tare da ɗago ta yama manta da wata Nenne rungu...
```don Allah Fans KU yi hakuri da rashin ganin post kullum hakan yana faruwa dalilin bana samun isasshen lokaci, yanzu bana jin dadi ina barar addu'ar ku ```
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:08 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*