← Book details Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 54

Sashe 31

Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Motarsa ya ɗauka kai tsaye gida ya nufa, a babban falo ya iske Nanne da Bobbo, duk'awa ya yi tare da gaisar da iyayen nasa, baki Alhaji Abubakar ya washe cikin jin dadin ganin ɗan nasa, shima Asmad din farin cikin ganin mahaifin nasa ya rufe shi. Cikin ladabi yace

"Baffa awarti jam! noi kugal?" ("Bobbo ka lafiya ya aiki?")

"Jam kolon asmad, noi kugal ma ambo?" ("lafiya lau Asmad, kai ma ya naka aikin?")

“Yettore jaumirawo Bobbo, wallahi hande kam mi somi siutare tan mi mari haje hande". ("Alhamdulillah Bobbo wallahi yau kam a gajiye nake hutu kawai nake bukata.")

" Na alari naa jotta to ad'onno mari debbo ni nanon non noo, alari jotta no awarti d'oo o hakkan noo ma diyam yiwugo be yamdu jamun" ("Kaji ba ka gaji ai da kana da mata duk da haka bata faru ba, kaga yanzu yadda ka dawo d'in nan zata baka ruwan wanka da lafiyyen abinci.")

Murmushi Asmad ya yi don yasan dama dole ne Bobbo ya masa maganar aure, burin sa kenan har kullum.

"Asmad mosii tan, nane maa o andino ko baffa wi'ata hala bangal tan haje mako"

A'a a bangal kam ai wakkati on ,bo ammi aam d'on wad'ana amm komi yid'i fuu, gamman na saito mi banyi. ("Kai Babbo shi fa aure lokaci ne, kuma Bobbo na tana yi min komai da nake so, don haka ba zanyi wani aure ba.")

Aa bangal kam dole a bangan, mid'o rufini maa gite taan dikka a fudda taskugo. ('a'a aure kam yinsa zakayi ina dai rakakane, amma tun yanzu gara ka soma shiri.")

Tab minkam bangal na jotta gam milarai momi yid'i, amma mid'o d'abbita be hakkilo harmi heba momi yid'i. ("taf ni kam Bobbo har yanzu ban ga matar da tayi min ba, zan dai ci gaba da bincika har na samu.")

denden ammi wad'i hunduko der hala man.("in ma baka samu ba ni zan zaba maka wacce ta dace da kai, kuma nasan zakayi farin ciki da zab'ina.")

Owii!

Sai a nan Nanne ta sa baki tace.

Allah subune ko lati hairu, ummu ayaha ayama yamdu maa ta fewa

"Allah ya kawo tagari Asmad, tashi kaje kayi wanka abinci na jiran ka."

Yana tashi ko bangaren sa bai kai ba, Bobbo ya dubi Nanne ya ce "na yanke wani shawara game da auren yaron nan, don banga yana da niyyar yin auren ba, amma zan tuntub'i Alhaji Bashir don inji ko ya Amince."

"Kai Alhaji wa zaka had'a da Asmad d'in? Nifa bani son azo rayuwaka suna b'aci fa?"

"Kar dai ki damu insha Allah Alhairi nake hangowa don haka ki taya mu da Addu'a, kuma had'in da zanyi kema zakiyi farin ciki."

"Allah ya taimaka, nasan Asmad bashi da matsala, zanyi masu Addu'an fatan Alhairi."

*******************
Alhaji Mansur ne tsaye a falon shi, cikin wani irin yanayi, me wuyar fassarawa. Da alama, ya kai karshen tunani ne amma bai samo mafita ba.

Ya yi amfani da hannunshi na hagu wajen kwankwasar kanshi, sai kuma ya nufi window ( taga) falon ya yaye labulen ya leka tare da kwada ma Najeeb kira iya karfin shi. Sai da yaga fitowar Najeeb ɗin, sannan ya sake labulen ya koma ya tsaya kamar ya hadiyi tabarya.

"Ka san Ameesha?" Alhaji Mansur ya faɗa bayan Najeeb ya zauna.

Ido da baki Najeeb ya bude sannan ya ce...

_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:01 PM] Zulayheart Rano: *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
*(NWA)*

*SANGARTA*

©
*ZULAYHEART RANO*

``` Gaba ɗaya littafin nan naki ne my Cittah wato KHADIJAH A MUHAMMAD Allah ya bar k'auna ,inajinki har a zuciyata Kema kisa a ranki Zulayheart taki ce.```

*6*
" Bayan Najeeb ya rufe budadden bakin shi tun sa'adda ya ji sunan Ameesha a bakin mahaifinshi. Sai ya ce

" Na san ta. Akwai wani abu ne? Ko ba yar gidan Alhaji Taheer ba?" Shi ma Najeeb ya rufe maganar ta shi da tambayar mahaifin na shi.

"Eh itaa, to ka bude kunne ka jini da kyau."

Gyara zama Najeeb ya yi, tare da mai da hankalin sa kan Abban nashi. Sannan Alhaji Mansur ya ci gaba da maganar sa

"Kana jina ko Najeeb? so nake daga yau zuwa satin sama masu zuwa ka tabbatar ka cusa kanka gareta,so nakeyi nayi amfani da wannan damar don cimma burina."

Najeeb da kallo ya bi mahaifin nasa, don kwata kwata bai gane inda yasa gaba ba, kamar Alhaji Mansur yasan tunanin da Najeeb ya fad'a, don haka sai ya ce

"So nake kaje wajen ta da batun soyayya, ka san yadda zaka yi har ta soka wannan shi ne abin da nake umurtanka."

Zaro ido ya yi baki na rawa ya ce

"Abba kasan fa Yarinyar nan ba wata kunya ce da ita ba, kuma dai da kyar zata amince min don ba mutunci ne da ita ba."

Tun kafin ya kai karshen maganar Alhaji ke aika masa da wani mugun harara, wanda har ya firgita Najeeb din, cikin fushi ya soma magana

"Kai kam Najeeb anyi shashasha, yanzu kai a matsayin ka ka ce baka iya tsara wannan 'yar Yarinyar? To bari kaji dole sai kayi abin da na sanya ka."

Girgiza kai kawai ya yi, yana mamakin halin mahaifin nasa sosai.

"To naji Abba amma in ta amince ya zanyi da Rufaidat, kasan dai ita nake so."

Mtsww Alhaji Mansur ya ja wata doguwar tsaki, don takaici

"Kai fa Najeeb da alama kana son raina min hankali, ina ruwana da maganar Rufaida indai bukata ta zata biya, daga baya kasan yadda za'ayi da ita."

"Amma Abba baka tunanin a samu matsala, Yarinyar nan fa da wuya ta soni, kuma nima dai ba wani sonta nake yi ba. "

" Bani son rashin ta ido, kana jina koh? Maganar da ma fada maka dole ne kayi amafini da ita don abin da nake son yi kai zakayi Alfahari da shi ba ni ba."

" Yi hakuri Abba zan yi yadda kake so insha Allah."

Cikin ladabi Najeeb ya k'arasa maganar.

"Yawwa d'an Albarka haka nake so." Alhaji Mansur ya yi maganar cikin farin ciki.
Mik'ewa Najeeb ya yi yana mamakin halin mahaifin na shi.

Bayan fitar Najeeb, sai Alhaji Mansur ya manna bayan shi da kujera haka ya sauke wani numfashi me kauri.

Ya kai hannunshi yana shafa goshin shi, wannan ita ce hanya daya tilo da yake ganin zai yi amfani da ita don cikar wani buri na shi da ya dade a zuciyarshi.

Idan har wannan buri na shi ya cika, bai san irin kalar munan da zai yi ba.

Zumbur!Kamar Wanda ya tuna wani abu haka ya tashi, ya dauki key din motar shi ya nufi waje.

*****************
Nanne ce zaune a bedroom din Bobbo, magana yake fad'a mata kuma ga dukkan alamu maganar nada muhimmanci, cikin nutsuwa ta ce

"Amma kana ganin bamu shiga hakkin Yarinyar ba?"

"Maganar shiga hakki bata taso ba, tun da asalin maganar ba daga wajen mu take ba, abin da nake so kawai shi ne in samu Asmad din ya yadda."

"Kai ma Alhaji kasan bashi da matsala kuma yana kokarin yin biyayya, kar kayi tunanin haka, Ubangiji Allah ya sa haka shi ne Alhairi."

"Amin." Bobbo ya yi maganar cikin jin dadi.

" Yawwa da na manta Aneesa fa sun kusa komawa makaranta, don haka zata koma gida."

" Yaushe zata koma din?"

" Ranar Asabar zata koma."

"To Allah ya kaimu."

"Bobbo ya mike tare da fadin bari na leka wajen masu aikin gidan can."

A tare suka fita zuwa falon, suna shiga Shima Asmad na fitowa daga bedroom din sa, sauri yake yi don dama har ya fita mantawa ya yi shi ne ya dawo.

"Bobbo barka da rana. "

Asmad ya fada cike da ladabi.

" Lafiya lau Asmad har ka dawo ne?"

Bobbo ya amsa cike da kulawa.

"Eh amma yanzu zan koma, dama na danyi mantuwa ne."

Asmad ya karasa maganar yana nufa hanyar waje.

Najeeb ne a bangaren sa, ya na faman aikin kai kawo gaba daya kansa ya kulle ya rasa tunani d'aya da zaiyi. " shi damuwar sa Rufaida shin taya zata dauki maganar in har ta samu labari?"

Ya yiwa kansa tambayar da bashi da amsa, zuciyar sa tace " kawai kayiwa mahaifin ka biyayya tunda umurni ya baka."

Najeeb dai ya kasance d'ane mai biyayya sam baya tsallake maganar mahaifansa, don haka da sauri ya nufi toilet, wanka ya yo kana ya shirya cikin kananan kaya wanda suka amshi jikinsa, ya fashe jikinsa da turare mai sanyi kamshi, key na motarsa ya d'auka sannan ya yi waje."

Sai da ya isa bangaren mahaifiyar sa, bayan ya gaida ta sannan ya nufi parking space.

Tunda ya tada motar ya ke tunanin ta ina zai fara ne? Shi dai bai tab'a zuwa wajen wata budurwa da sunan soyayya ba Sai Rufaida, to yau gashi da rana tsaka Abban sa ya daura masa aiki, babban matsalar ma ita ce bashi ya ga Yarinyar yana so ba, da a ce shi ya ganta yana so to da da sauki, amma wannan umurnin da wuya in za'a ci nasara.

Rasa inda zai nufa yayi don haka kawai sai ya tsayar da shawarar zuwa makarantar su.

Bai zame ko ina ba sai makarantar su Ameesha, don yana tunanin tana school din, tunda yanzu sha d'aya ne na safe, parking ya yi a kusa da kofar makarantar yana jiran ganin fitowar Ameesha.

Najeeb na zaman jiran ganin Ameesha, ita kuwa tana Asbitin da take practical, suna zaune a karkashin wata itaciyar mangwaro hira suke ta sha da kawayenta.

Hira sukeyi hankali kwance, ita da Meena ce sai wasu 'yan class d'in su biyu, d'aya daga cikin wacce suke zaune ta kalle su gaba d'aya ta ce kunsan me?" ta ci gaba nifa wallahi Dr dan fullo burgeni da zai soni wallahi da na more..... "

Tun kan takai karshen maganar ta yi saurin katseta.

" Kina da aiki wannan mara mutunci ne zaki wani ce kina son sa? Taf lallai da babban aiki a gaban ki."

"Kai Meesha ke dai naga alamar ba zaku sha inuwa d'aya da Dr dan fullo ba, ko da yaushe akayi maganar sa sai ki soma wani hakikance wa."
Chapter 31 · 0% Book details