Sashe 5
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashi ya yi cikin sauri tare da kallon agogon da ke manne jikin bangon daki "subhanallah! Ya furta a fili ganin har bakwai da minti sha biyar, ya makara sosai sakamakon kwanan da ya yi wajen binciken asbitin da zai kai Ameesha, tun tun sha biyu yake aikin bai samu kansa ba sai karfe huɗu, bayan ya kammala alwala ya dauro ya soma gabatar da sallah sai da ya yi asbah kafin bacci ya dauke shi, da azama ya isa toilet din shaf shaf ya yi wankan ya fito ya soma shiryawa.
Bai jima ba ya kammala shirinsa, falon ya fita hannunsa dauke da wayoyinsa, babu kowa a falon da alama ma dai matar gidan bata tashi ba, don haka sai ya nufi bedroom ɗinta yana tura kofar ta buɗe can ya hangota cikin bargo tana sharar bacci ta, takawa ya yi har bakin gadon ya zauna tare da ambaton sunan ta
"Aneesa! Ya yi maganar yana dana buga kafadarta ta, ido ta buɗe cike da mayen bacci ta ba ta ce komai ba sai kallonsa da ta yi.
"Kin yi sallah kuwa?" Ya tambaye ta tare da tsare ta da ido.
Doguwar Hamma ta yi tare da girgiza kai alamar a'a, "ok tashi ki yi gari ya waye ras har bakwai da rabi, zuwa yanzu ya kamata ki gyara halinki ki daina wasa da ibadanki."
Harara ta bi shi da ita don haushi yake bata, sam ta tsani ko da ganinsa tashi ta yi bata ko ce masa komai ba, yana zaune har ta fito sannan ya tashi tsaye yana faɗin
"To nikam na tafi office sai na dawo." Bata ce masa kala ba ta tayar da sallar ta.
Girgiza kai ya yi tare da fita, cikin zuciyarsa yana mamakin halin Aneesa.
Duk da yasan ya yi latti amma hakan bai hana shi biyawa gidan Nenne ba, domin duba lafiyar Ameesha da jiki, sallama ya yi cikin falon ya ji shiru, a zuciyarsa yana tunanin kila suna ɗakin Nenne don haka sai ya nufi haryar motsin da ya ji a dining ne ya sashi lekawa zaune ya ganta a dining din tana juya cokali cikin cup
Murmushi ya saki yana faɗin " *Heartbeat* kina nan ke kaɗai?" Ya ida maganar yana zama a daya daga kujeran dining din.
Itama murmushi ta yi ta ce
"Sweety Asmad! Shi ne kaɗai kalmar da Ameesha ke iya faɗa.
Siririn dariya ya yi yana kallonta cikin wani yanayi mai wuyar fassara ya buɗe baki zai yi magana kenan ya ji muryar Nenne
"Maganar wa nakeji kamar ta Asmad?" Nenne ta yi maganar tana zama a dining din.
"Wallahi ni ne Nennena, na biyo duba jikin Ameesha ne."
"Ah! Ai jiki ya yi sauki ka ganta nan." Ta dire maganar tana kallon Ameesha da har yanzu take juya tea din. Mamaki ya kama Nenne ta ce
"A'a Ameesha wa ya haɗa maki tea din?"
"Au bake kika haɗa mata ba? Nima nazo naga tana juya abinda, madallah! Ashe Heartbeat ta Fara hada shayi da kanta." Cikin murmushi ya ida maganar.
"A'a bani na haɗa mata ba don na shiga ciki, ai haka ake so sauki ya rika samuwa." Nenne tana maganar ne tana haɗawa Dr tea, a lokacin kuma Ameesha ta daga kofin tea din tare da kaiwa bakinta da sauri ta furzo shi tare da bata rai, da kallo suka bita da mamaki, ba su gama mamakin ba sai suka ga ta mika hannu tare da dauko cup din da Nenne ta haɗawa Dr tea ta kai...
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:14 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
``` wannan page din kyauta na baki ZEETY MUM HANAN ki yi yadda zaki da shi domin jin dadin ki, ki daɗe ki yi karko uwargida sarautar mata, Allah ya kara maki lafiya da basira Ubangiji ya raya mana su Hanan rayuwa mai inganci ```
_*Hazika kuma Hamshaqiya fasihiya duk ke kaɗai kika amsa wannan sunan BESTYNA Khadija s Muhammad ke ɗin ta daban ce, fadan matsayin a wajena ba zai yiwu ba, sai ina kara tabbatar maki da Ina jinki har cikin jinina, Allah ya k'ara tsare min ke a duk inda kike amin ina jin dadin littafin LAFIN WA? Wannan Nagartacciyar marubuciya kina ɓarar da ilimi a cikin sa Allah ya kara basira*_
*31*
Bakinta da ta kurba sai ta saki murmushi tana kallon Dr, su dai mamaki kawai suke na Ameesha sai zuwa can Dr ya sauke ajiyar zuciya ya ce
"Heartbeat bani tea na in sha sauri nake yi." Ko kallonsa bata yi ba sai ci gaba da shan kayanta ta yi.
Murmushi Nenne ta yi ta ce "kai ka dauki nata kasha tunda ta dauki naka."
Ɗauka ya yi yana faɗin "wai Nenne Ameesha ta haɗa tea da kanta amma sai ta dauke wanda kika haɗa min, bayan nawa bai kai kaurin nata ba." Ya ida maganar ya kai cup bakinsa, da sauri ya zubar da wanda ya kurba tare da aje cup din.
Kallonsa Nenne ta yi ta ce
" Lafiya kuwa menene ka zubo da shi?
"Nenne tea din fa ɗaci yake saboda tsabar sugar da ta cika." Cikin dariya da mamakin yadda Ameesha ta iya wayon haka ya ida maganar.
"Au ho! Wato shi yasa ta kasa sha kenan? Ikon Allah wannan abu da mamaki fa."
"Yo ai bazai sha wu ba kam, hakan da ta yi ba karamin daɗi ya yi ba, domin in sha Allahu da alamar nasara."
"To Allah ya taimaka, bari na hada maka wani yaushe ne tafiyar taku?"
"Jibi ne zamu tafi, kawai Nenne ki bar shi idan na tsaya sha zan yi latti."
"Allah ya kaimu, fatan ka sanar da Aneesa?"
"A'a ban sanar mata ba."
"Sam haka bai kamata ba, idan ka koma ka sanar mata, Asmad ka kasance mai adalci tsakanin matanka fa."
"In sha Allahu zan kasance Nenne, walllahi abin ne ya ɗan shige min, amma yau da na koma zan sanar da ita." Ya dire maganar yana k'ok'arin tafiya.
"Allah ya baka iko amma ka dai daure ka sha sai ka ji dadin tafiyar."
Sam Dr ba ya son musu da Nennensa shi yasa ya zauna. Zuwa wannan lokacin tuni har Ameesha ta shanye tea din Dr har ta dire cup.
Nenne tana gama haɗa masa ta mike zata bar dining Dr ya ce
"Nenne inaga kamar fa gara ki sanarwa da Aneesa maganar tafiyar mu zai fi." Ya kai karshen maganar yana kurɓar tea.
Komawa Nenne ta yi ta zauna tare da zubawa Asmad ido, kamar tana son gano wani abu, zuwa can kuma sai ta girgiza kai ta ce
"Me ya sa ni zan sanar mata, kai ba zaka iya bane?"
"No! Ba wai bazan iya faɗa mata bane, kawai ina ga idan kika sanar mata zaifi."
"To shi kenan, zuwa anjima zan sa direba ya daukota sai in sanar mata, amma anya kuwa kuna zaman lafiya da Aneesa?"
"Me kika gani Nenne? lafiya lau muke zaman mu fa." Dr ya bata amsa.
"To ai shi kenan." Ta yi maganar tana mik'ewa, ta fita daga dining room din.
Shi kuma Dr yana ganin Nenne ta basu waje, sai ya kai duban sa kan Ameesha ya ce
"Allah ke Heartbeat ko wato kin iya mugunta, shi ne kika dauke nawa bayan kin cikawa naki sugar ko?"
Dan murmushi ta yi tare da kallonsa, zuwa can kuma sai ta fara hamma alamar bacci
"Oh! Lallai ma Heartbeat wato bacci ma za ki yi ko?"
Ita dai Ameesha bata ce masa komai ba, duk maganar da yake, sai ma k'ok'arin tashi don taje ta kwanta take yi, dakatar da ita ya yi ta hanyar rike mata hannu daya, bai sakar mata ba har sai da ya kammala break kafin ya mike
Yana rike da hannunta har cikin bed room din Nenne, kwantar da ita ya yi yana faɗin
"A tashi lafiya Yar Ummi." Lumshe ido ta yi batare da ta yi magana ba. Yana fita falo ya samu Nenne zaune tana karatun littattafin hisnul-muslim, dubanta ta kai ga Asmad ta ce
"A'a Asmad dama baka tafi ba?"
"Eh! Dama Ameesha ce take jin bacci shi ne na kai ta bedroom, na barta har ta fara baccin." Ya bata amsa yana sosa kai.
Harara ta zabga masa ta ce
"Ya yi kyau, amma bana son wannan shashancin."
"Yi hakuri Nennena." Dr ya yi magana cikin shagwaɓa. Murmushi ta yi ta ce
"To na hak'ura Allah ya taimaka."
"Amin." Dr ya amsa daga haka ya fita zuciyarsa fes, ko da ya isa office aiki sosai ya yi, da zai koma gida bai biya gidan Nenne ba domin dai yasan matukar ya je ba zai je wajen Aneesa a kan lokaci ba. Don haka sai kawai ya wuce gida.
A falo ya samu Gimbiyar kwance da waya a hannunta, ko sallamar da ya yi bata amsa ba, bai nuna ya ji haushi ba domin so yake su yi magana ta fahimta, don haka sai ya isa inda take kwanciya ya zauna yana faɗin
"Wai Aneesa har yanzu fushin ne?"
Ko ɗago kai ta kalleshi ba ta yi, sai ma ɗan matsar da jikinta da ta yi, tana taɓe baki, murmushi ya yi tare da jawota jikinsa yana fadin
"Gaskiya na gaji da fushin nan zuwa yanzu ya kamata a sarara min."
"Wa yake fushi da kai?" Ta yi tambayar kamar bata fahimci inda ya dosa ba
" Ke ce kike fushi da ni Aneesa."
"A kan me zan yi fushi da kai?" Ta yi maganar cike da rainin hankali.
"Ok shi kenan tunda baki fushi da ni, yanzu dai tashi mu yi wata magana dake mai muhimmanci."
"Kunne ke jin magana don haka ina jinka."
"A'a kinga ki tashi kawai kamar yadda na bukata, don ba maganar wasa za mu yi ba." Cikin daure fuska ya yi maganar.
"Mtsss" taja ƙaramin tsaki a zuciyarta tare da tashi ta zauna "ina jinka." Ta faɗa cikin karamin murya.
Ya bude baku zai yi magana ta yi saurin katse shi
"Dazun Nenne take sanar min da tafiyar ka Egypt, da gaske tafiyar zaka yi ka barni?" Ta kai karshen maganar tana gyara zama, sam fuska babu walwala.
Bai jima ba ya kammala shirinsa, falon ya fita hannunsa dauke da wayoyinsa, babu kowa a falon da alama ma dai matar gidan bata tashi ba, don haka sai ya nufi bedroom ɗinta yana tura kofar ta buɗe can ya hangota cikin bargo tana sharar bacci ta, takawa ya yi har bakin gadon ya zauna tare da ambaton sunan ta
"Aneesa! Ya yi maganar yana dana buga kafadarta ta, ido ta buɗe cike da mayen bacci ta ba ta ce komai ba sai kallonsa da ta yi.
"Kin yi sallah kuwa?" Ya tambaye ta tare da tsare ta da ido.
Doguwar Hamma ta yi tare da girgiza kai alamar a'a, "ok tashi ki yi gari ya waye ras har bakwai da rabi, zuwa yanzu ya kamata ki gyara halinki ki daina wasa da ibadanki."
Harara ta bi shi da ita don haushi yake bata, sam ta tsani ko da ganinsa tashi ta yi bata ko ce masa komai ba, yana zaune har ta fito sannan ya tashi tsaye yana faɗin
"To nikam na tafi office sai na dawo." Bata ce masa kala ba ta tayar da sallar ta.
Girgiza kai ya yi tare da fita, cikin zuciyarsa yana mamakin halin Aneesa.
Duk da yasan ya yi latti amma hakan bai hana shi biyawa gidan Nenne ba, domin duba lafiyar Ameesha da jiki, sallama ya yi cikin falon ya ji shiru, a zuciyarsa yana tunanin kila suna ɗakin Nenne don haka sai ya nufi haryar motsin da ya ji a dining ne ya sashi lekawa zaune ya ganta a dining din tana juya cokali cikin cup
Murmushi ya saki yana faɗin " *Heartbeat* kina nan ke kaɗai?" Ya ida maganar yana zama a daya daga kujeran dining din.
Itama murmushi ta yi ta ce
"Sweety Asmad! Shi ne kaɗai kalmar da Ameesha ke iya faɗa.
Siririn dariya ya yi yana kallonta cikin wani yanayi mai wuyar fassara ya buɗe baki zai yi magana kenan ya ji muryar Nenne
"Maganar wa nakeji kamar ta Asmad?" Nenne ta yi maganar tana zama a dining din.
"Wallahi ni ne Nennena, na biyo duba jikin Ameesha ne."
"Ah! Ai jiki ya yi sauki ka ganta nan." Ta dire maganar tana kallon Ameesha da har yanzu take juya tea din. Mamaki ya kama Nenne ta ce
"A'a Ameesha wa ya haɗa maki tea din?"
"Au bake kika haɗa mata ba? Nima nazo naga tana juya abinda, madallah! Ashe Heartbeat ta Fara hada shayi da kanta." Cikin murmushi ya ida maganar.
"A'a bani na haɗa mata ba don na shiga ciki, ai haka ake so sauki ya rika samuwa." Nenne tana maganar ne tana haɗawa Dr tea, a lokacin kuma Ameesha ta daga kofin tea din tare da kaiwa bakinta da sauri ta furzo shi tare da bata rai, da kallo suka bita da mamaki, ba su gama mamakin ba sai suka ga ta mika hannu tare da dauko cup din da Nenne ta haɗawa Dr tea ta kai...
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:14 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
``` wannan page din kyauta na baki ZEETY MUM HANAN ki yi yadda zaki da shi domin jin dadin ki, ki daɗe ki yi karko uwargida sarautar mata, Allah ya kara maki lafiya da basira Ubangiji ya raya mana su Hanan rayuwa mai inganci ```
_*Hazika kuma Hamshaqiya fasihiya duk ke kaɗai kika amsa wannan sunan BESTYNA Khadija s Muhammad ke ɗin ta daban ce, fadan matsayin a wajena ba zai yiwu ba, sai ina kara tabbatar maki da Ina jinki har cikin jinina, Allah ya k'ara tsare min ke a duk inda kike amin ina jin dadin littafin LAFIN WA? Wannan Nagartacciyar marubuciya kina ɓarar da ilimi a cikin sa Allah ya kara basira*_
*31*
Bakinta da ta kurba sai ta saki murmushi tana kallon Dr, su dai mamaki kawai suke na Ameesha sai zuwa can Dr ya sauke ajiyar zuciya ya ce
"Heartbeat bani tea na in sha sauri nake yi." Ko kallonsa bata yi ba sai ci gaba da shan kayanta ta yi.
Murmushi Nenne ta yi ta ce "kai ka dauki nata kasha tunda ta dauki naka."
Ɗauka ya yi yana faɗin "wai Nenne Ameesha ta haɗa tea da kanta amma sai ta dauke wanda kika haɗa min, bayan nawa bai kai kaurin nata ba." Ya ida maganar ya kai cup bakinsa, da sauri ya zubar da wanda ya kurba tare da aje cup din.
Kallonsa Nenne ta yi ta ce
" Lafiya kuwa menene ka zubo da shi?
"Nenne tea din fa ɗaci yake saboda tsabar sugar da ta cika." Cikin dariya da mamakin yadda Ameesha ta iya wayon haka ya ida maganar.
"Au ho! Wato shi yasa ta kasa sha kenan? Ikon Allah wannan abu da mamaki fa."
"Yo ai bazai sha wu ba kam, hakan da ta yi ba karamin daɗi ya yi ba, domin in sha Allahu da alamar nasara."
"To Allah ya taimaka, bari na hada maka wani yaushe ne tafiyar taku?"
"Jibi ne zamu tafi, kawai Nenne ki bar shi idan na tsaya sha zan yi latti."
"Allah ya kaimu, fatan ka sanar da Aneesa?"
"A'a ban sanar mata ba."
"Sam haka bai kamata ba, idan ka koma ka sanar mata, Asmad ka kasance mai adalci tsakanin matanka fa."
"In sha Allahu zan kasance Nenne, walllahi abin ne ya ɗan shige min, amma yau da na koma zan sanar da ita." Ya dire maganar yana k'ok'arin tafiya.
"Allah ya baka iko amma ka dai daure ka sha sai ka ji dadin tafiyar."
Sam Dr ba ya son musu da Nennensa shi yasa ya zauna. Zuwa wannan lokacin tuni har Ameesha ta shanye tea din Dr har ta dire cup.
Nenne tana gama haɗa masa ta mike zata bar dining Dr ya ce
"Nenne inaga kamar fa gara ki sanarwa da Aneesa maganar tafiyar mu zai fi." Ya kai karshen maganar yana kurɓar tea.
Komawa Nenne ta yi ta zauna tare da zubawa Asmad ido, kamar tana son gano wani abu, zuwa can kuma sai ta girgiza kai ta ce
"Me ya sa ni zan sanar mata, kai ba zaka iya bane?"
"No! Ba wai bazan iya faɗa mata bane, kawai ina ga idan kika sanar mata zaifi."
"To shi kenan, zuwa anjima zan sa direba ya daukota sai in sanar mata, amma anya kuwa kuna zaman lafiya da Aneesa?"
"Me kika gani Nenne? lafiya lau muke zaman mu fa." Dr ya bata amsa.
"To ai shi kenan." Ta yi maganar tana mik'ewa, ta fita daga dining room din.
Shi kuma Dr yana ganin Nenne ta basu waje, sai ya kai duban sa kan Ameesha ya ce
"Allah ke Heartbeat ko wato kin iya mugunta, shi ne kika dauke nawa bayan kin cikawa naki sugar ko?"
Dan murmushi ta yi tare da kallonsa, zuwa can kuma sai ta fara hamma alamar bacci
"Oh! Lallai ma Heartbeat wato bacci ma za ki yi ko?"
Ita dai Ameesha bata ce masa komai ba, duk maganar da yake, sai ma k'ok'arin tashi don taje ta kwanta take yi, dakatar da ita ya yi ta hanyar rike mata hannu daya, bai sakar mata ba har sai da ya kammala break kafin ya mike
Yana rike da hannunta har cikin bed room din Nenne, kwantar da ita ya yi yana faɗin
"A tashi lafiya Yar Ummi." Lumshe ido ta yi batare da ta yi magana ba. Yana fita falo ya samu Nenne zaune tana karatun littattafin hisnul-muslim, dubanta ta kai ga Asmad ta ce
"A'a Asmad dama baka tafi ba?"
"Eh! Dama Ameesha ce take jin bacci shi ne na kai ta bedroom, na barta har ta fara baccin." Ya bata amsa yana sosa kai.
Harara ta zabga masa ta ce
"Ya yi kyau, amma bana son wannan shashancin."
"Yi hakuri Nennena." Dr ya yi magana cikin shagwaɓa. Murmushi ta yi ta ce
"To na hak'ura Allah ya taimaka."
"Amin." Dr ya amsa daga haka ya fita zuciyarsa fes, ko da ya isa office aiki sosai ya yi, da zai koma gida bai biya gidan Nenne ba domin dai yasan matukar ya je ba zai je wajen Aneesa a kan lokaci ba. Don haka sai kawai ya wuce gida.
A falo ya samu Gimbiyar kwance da waya a hannunta, ko sallamar da ya yi bata amsa ba, bai nuna ya ji haushi ba domin so yake su yi magana ta fahimta, don haka sai ya isa inda take kwanciya ya zauna yana faɗin
"Wai Aneesa har yanzu fushin ne?"
Ko ɗago kai ta kalleshi ba ta yi, sai ma ɗan matsar da jikinta da ta yi, tana taɓe baki, murmushi ya yi tare da jawota jikinsa yana fadin
"Gaskiya na gaji da fushin nan zuwa yanzu ya kamata a sarara min."
"Wa yake fushi da kai?" Ta yi tambayar kamar bata fahimci inda ya dosa ba
" Ke ce kike fushi da ni Aneesa."
"A kan me zan yi fushi da kai?" Ta yi maganar cike da rainin hankali.
"Ok shi kenan tunda baki fushi da ni, yanzu dai tashi mu yi wata magana dake mai muhimmanci."
"Kunne ke jin magana don haka ina jinka."
"A'a kinga ki tashi kawai kamar yadda na bukata, don ba maganar wasa za mu yi ba." Cikin daure fuska ya yi maganar.
"Mtsss" taja ƙaramin tsaki a zuciyarta tare da tashi ta zauna "ina jinka." Ta faɗa cikin karamin murya.
Ya bude baku zai yi magana ta yi saurin katse shi
"Dazun Nenne take sanar min da tafiyar ka Egypt, da gaske tafiyar zaka yi ka barni?" Ta kai karshen maganar tana gyara zama, sam fuska babu walwala.