Sashe 29
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bubbuga bayanta Abba ya soma alamar rarrashi "Yi hakuri uwata karki bar wannan ya dame ki, insha Allah zan dau mummunan mataki akan koma waye, shi duk randa Allah ya had'a mu."
"Da dai kabi komai a hankali zaifi, amma wannan maganar da kake ba shine dai dai ba."
Hajiya Halima ta yi maganar tana zama kan kujera.
"ke Ummi kinga kuwa irin wulakacin da ya min?kike cewa a bi komai a hankali, wallahi Abba karka bi a hankali."
"To uwar rashin kunya, duk wannan abin da kuke yi wata rana sai kunyi nadama kuma ma mara amfani."
"Nifa wallahi Hajiya ban son irin maganar da kike yi, ke kullum baki mana fatan Alhairi sai mugun baki, to ta Allah ba ta kiba."
"Gaskiya ce baku so ni kuma dole sai na fad'a."
"Ki rike gaskiyar ki bamu so din"
"Yawwa Abba ina son duk lokacin da kuka had'ui, karka saurara masa ka nuna masa ni din yar gatan ka ce."
"An gama Uwata maza jeki daki ki dan watsa ruwa ko zakiji sanyi."
"To Abba sai nayi sallah zan fito, don a hanyata ta dawowa naji an kira."
"A fito lafiya diyar Abba."
Murmushi Ummin Ameesha ta yi, don wannan halin na Ameesha kadai ke burgeta, duk abin da take da zaran taji an kira sallah, bata bari lokaci ya wuce.
Kusa da Ummin ta matsa tace
"Ummi yau me kika dafa ne?"
"Tuwon shinkafa ne miyar wake."
"Wow Ummi kinyi abin da nake son ci."
Da fa kanta Ummin ta yi tace
"To ga yacan a dining komai is ready."
"Ok bari na fito." Ameesha tayi maganar yayin da take taka matakalar benan don hayewa sama.
Farin ciki ne ya kama Alhaji Taheer mahaifin Ameesha ganin yadda suka yi magana cikin walwala da farin ciki.
Shigarta bedroom din ke da wuya sai ta wurgar da Jakarta dake hannunta (hand bag) tare da cire gyalen da ta yafa, Kai tsaye toilet ta nufa ta sakarwa kanta ruwan sanyi, kila ko ta samu sassaucin abin da take ji a zuciyar ta, ta jima sosai sannan ta fito bayan ta dauro alwala, zanen da take sallah ta dauko tare da hijjab dinta sannan ta tayar da sallar.
Bayan ta idar da sallar, ta shirya cikin wani wando da riga wanda suka mata matukar kyau, wandon pencil ne kalar pink, rigar kuma body top ne kalar white, sun amshi jikinta, ta yi pakin kanta da ribbon kalar wandon ta, tsaf ta feshe jikin ta da turaruka masu kamshi.
Masha Allah, Gaskiya Allah ya yi halitta don Ameesha kam babu inda Allah ya rage ta, ta fannin halatta kyakkyawa ce wato (First Class) a jin farko, gata doguwa, bata da Kiba ko kadan, amma fa akwai ta da hips and braest, komai cif.
********************************
Cikin kwarewa yake driven motar, fuskar sa dauke da wani special smile, haka kawai in ya tuna Ameesha yake jin zuciyar sa fes, sai dai wani bangare na zuciyar sa tana fama da rad'ad'i tare da dana sanin marin da ya mata. A fili ya furta
"Shi is very beautiful girl, duk wanda ya samu wannan matsayin mata lallai ya more."
Wayarsa ce ta soma ruri a lamar tana neman agaji, da sauri ya dauki wayar ganin mai kiran yasa shi sakin murmushi, picking ya yi tare da karawa a kunne
"Hello Allah hokke sabbugo Nannena, mid'o a nyalli jam, noi sare? " (" Allah ya baki tsawon rai Nannena, fatan kina lafiya ya gida?)
" Jamni tawon Asmad mid'o yela wala billare fere kam.... " (" lafiya Lau Asmad fatan kaima baka da matsala?)
" A'a Nanne wala ko d'ume, jottama mid'o lawol Wartugo sare." ("a'a Nanne babu matsalar komai, yanzu haka ina hanyata ta dawowa gida")
"Allah wadde jam amma a hakkilina lawol anani naa barkantejo.... " (" Allah ya dawo min da kai lafiya Amma ka kula da kyau kaji dan Albarka.")
Murmushi ya yi lokacin da ya kammala waya da mahaifiyar nasa,yana jin farin cikin yadda Nannen shi ke bashi kula, cikin mintina k'alilan ya isa unguwar su, bakin wani makeken get naga ya nufa, hon ya yi cikin sauri mai gadin ya wangale masa get din, wow masha Allah wannan rantsatsen gida haka, gida ne babba ginin zamani, Kai da ganin gidan kasan an kashi kudi, da ka shigo gidan da dakin maigadi zaka soma karo, gefen dama kuma, wani dan dakine aka gina da alama na generator ne, sai wasu flowers da aka daddasa masu kyau, su suka kuma sa gidan ya had'u, gefe guda kuma parking space ne, motoci jere a ciki masu dan banzan kyau.
Sai mutum yayi dan tafiya kafin yasa da kansa da ainahin cikin gidan.
A parking space ya faka motar sa, sannan ya fito tare da d'aukan laidar da ya yi sayayya a Shahad din, kofar babban falon gidan ya shiga bakin sa dauke da sallama, wata kyakkyawan macece wacce bazata wuce shekaru 40 zuwa 42 zaune cikin hadadden falon, babban falo ne wanda aka kawata sa da wasu manya manyan kujeru na alfarma, ga wani carpet mai shegen kyau wanda ya fito da ainahin kyaun falon, kalarsa da kujerun d'aya, wato brown color, haka ma labulen, babban plasma TV ne manne a bangon falon.
Kallo daya zakiyi wa matar kasan bafulatana ce, fara ce fuskar ta kunshe da annuri, macece mai riko da Addini don hannunta rike yake da wani littafin Addu'oi tana karantawa, jin sallamar dan nata yasa tayi saurin d'agowa fuska d'auke da murmushi ta amsa masa sallamar.
Inda take zaune ya 'karasa, zama ya yi kusa da kafarta tare da lank'washe 'kafarsa, ya soma gaidata, shafa kansa tayi tace
"Ja66ama Asmad, awartii Jam... " (barka da zuwa Asmad ka dawo lafiya?)
" Jamni tawon Nanne, sai welo minanata... " (lafiya Lau Nanne sai dai ina jin matukar yunwa).
" Ta damu mitimmini nyamdu.... "(karka damu akwai abinci, ban dade da gamawa ba.)
" Yawwa Nanne 6ewaddina aam sudu aam, hiddeko mi wurta yiwugo..." (Yawwa Nanne a kawo min bedroom dina yanzu, kafin na fito wanka.)
"To ha ladidi waddine.... " (bari ladidi ta kawo maka.)
" A'a Nanne miyid'a 6ingel d'o nastimi sudu aam, toi aneesa ko'o huwata, hokku moo ne o wadda..." ( "a'a Nanne ban son wannan Yarinyar tana shigar min bedroom, ki dai Ba Aneesa ita aikin me takeyi?)
" To yahu hami hokka aneesa man waddine..." ("To jeka Aneesa zata kawo maka.")
"Yawwa Nanne hanju wad'i miyid'i Ma..." ("Yawwa Nanne shi yasa nake Kara sonki."
Asmad ya yi maganar yana Mika mata, d'aya daga cikin ledar da ya shigo da shi, amsa ta yi tare da sanya masa Albarka, shi kuma ya fita tare da nufa 'bangaren sa.
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:01 PM] Zulayheart Rano: [4/15, 4:00 PM] Zulaiha Rano: *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* *(NWA)*
*SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Please fans kuyi hakuri anyi mistake a pagen ɗin jiya amma gashi yanzu na gyara da fatan zakuyi min afuwa,ku cigaba da bibiyar littafi*
*Nice dai Zulayheart Rano*
*4*
Asmad na wucewa Nanne ta soma 'kwalawa Aneesa kira, cikin sanyin murya ta amsa da
"Na' am Nanne ga ni"
Aneesa ta fada lokacin da ta isa wajen Nannen.
"Yawwa yi sauri ki hada wa Hammanki Asmad abinci, ki kai masa bangaren sa."
Murmushi ta saki jin Nanne ta ambaci Asmad.
"To Nanne."
Ta yi maganar tana nufa hanyar kicin din, cikin kankanin lokaci har ta shirya masa duk wani abu da suka dafa ta nufi, bangaren da shi, a k'ofar falon ta tsaya tana sallama, Asmad dake fitowa daga toilet ya amsa, tare da buɗe mata ya dan matsa ta ida shiga bedroom ɗin.
Kallon sa ta yi cikin wani irin shauki, bayan ta aje tire ɗin tace
"Hamman Asmad Sannu da dawowa"
"Yawwa." ya amsa yana goge kanshi da karamin towel.
Tsayawa ta yi tana kallon sa, a rayuwarta tana mugun son Asmad sai dai tasan, ta makaro don bata cikin irin matan da Asmad yake so, domin duk wani hanya da zata bi don shawo hankalinsa ta yi amma a banza.
"Ke tunanin me kike yi da bazaki wuce ba, kin wani sani gaba kina kallo kamar na zamar maki bak'o?"
Dan murmushi ta yi ta ce
"Lah yi hakuri Hamman, dama so nake nace maka ina son zuwa wajen saloon."
"Anjima ki amsa kudi a wajen Nanne, jeki ina son gama shiryawa."
Jiki a sanyaye Aneesa ta bar ɗakin, ba don ranta ya so ba. Aneesa 'yar k'anwar Nanne ce ta zo daga Adamawa, da yake dama duk sanda ta samu hutun school to anan kano gidan su Asmad take yin hutun ta. Kamar ko yaushe wannan karon ma hutu ta samu, Aneesa budurwa ce kyakkyawar gaske, tana da dan jiki sai dai bata da tsawo, shekarun ta Ashirin da haihuwa, a fuska mutumiyar kirki ce sak, amma akwai ɓoyayyen hali a tattare da ita, tun tasowanta take son Asmad din, sai dai shi bata tata yake ba.
Falon Nanne ta koma, a inda ta barta na ta sameta, kasa tayi da murya tace
"Nanne inji Hamman wai ki bani kudi anjima zani saloon."
"Ba dai yau ba, sai gobe don yanzu kam yamma ta soma yi."
"To Nanne." Aneesa ta yi maganar cikin sanyi.
cikin kwanciyar hankali, Asmad ya gama shirin sa, sosai ya yi kyau, domin Asmad kyakkyawan bafulatanin garin Adamawa ne.
*Asmad Abubakar ɗan Fullo* shi ne cikakken sunan sa, mahaifinsa Alhaji Abubakar da mahaiyarsa Hajiya Binta duk haifaffun garin Adamawa ne, kasuwan ci ya kawo mahaifinsa kano.
Allah ya ba Alhaji Abubakar dukiya, sosai ɗa ɗaya Allah ya basu shine Asmad, ya taso cikin gata ta ko wane fanni, sai dai ya samu ingantaciyar tarbiya, duk da kasancewar sa shi ɗaya Allah ya ba iyayen sa, akwai shi da nutsuwa da hankali, shekaran sa ashirin da takwas da haihuwa,
Nanne takasance mece ce mai hankali da tunani, ko da yaushe fuskar ta a sake take, mace ce masaniyar Alkur'ani mai girma, Kuma mai aiki da shi, shi yasa sam bata yadda aka ɓata Asmad da wasu munanan d'abi'u ba, amma fa dai-dai da minti ɗaya in ka zauna da su zaka fahimci tsananin son da Nanne ke masa, don bata iya ɓoye son Asmad a gaban kowa, duk da kasance warta bafulatana.
"Da dai kabi komai a hankali zaifi, amma wannan maganar da kake ba shine dai dai ba."
Hajiya Halima ta yi maganar tana zama kan kujera.
"ke Ummi kinga kuwa irin wulakacin da ya min?kike cewa a bi komai a hankali, wallahi Abba karka bi a hankali."
"To uwar rashin kunya, duk wannan abin da kuke yi wata rana sai kunyi nadama kuma ma mara amfani."
"Nifa wallahi Hajiya ban son irin maganar da kike yi, ke kullum baki mana fatan Alhairi sai mugun baki, to ta Allah ba ta kiba."
"Gaskiya ce baku so ni kuma dole sai na fad'a."
"Ki rike gaskiyar ki bamu so din"
"Yawwa Abba ina son duk lokacin da kuka had'ui, karka saurara masa ka nuna masa ni din yar gatan ka ce."
"An gama Uwata maza jeki daki ki dan watsa ruwa ko zakiji sanyi."
"To Abba sai nayi sallah zan fito, don a hanyata ta dawowa naji an kira."
"A fito lafiya diyar Abba."
Murmushi Ummin Ameesha ta yi, don wannan halin na Ameesha kadai ke burgeta, duk abin da take da zaran taji an kira sallah, bata bari lokaci ya wuce.
Kusa da Ummin ta matsa tace
"Ummi yau me kika dafa ne?"
"Tuwon shinkafa ne miyar wake."
"Wow Ummi kinyi abin da nake son ci."
Da fa kanta Ummin ta yi tace
"To ga yacan a dining komai is ready."
"Ok bari na fito." Ameesha tayi maganar yayin da take taka matakalar benan don hayewa sama.
Farin ciki ne ya kama Alhaji Taheer mahaifin Ameesha ganin yadda suka yi magana cikin walwala da farin ciki.
Shigarta bedroom din ke da wuya sai ta wurgar da Jakarta dake hannunta (hand bag) tare da cire gyalen da ta yafa, Kai tsaye toilet ta nufa ta sakarwa kanta ruwan sanyi, kila ko ta samu sassaucin abin da take ji a zuciyar ta, ta jima sosai sannan ta fito bayan ta dauro alwala, zanen da take sallah ta dauko tare da hijjab dinta sannan ta tayar da sallar.
Bayan ta idar da sallar, ta shirya cikin wani wando da riga wanda suka mata matukar kyau, wandon pencil ne kalar pink, rigar kuma body top ne kalar white, sun amshi jikinta, ta yi pakin kanta da ribbon kalar wandon ta, tsaf ta feshe jikin ta da turaruka masu kamshi.
Masha Allah, Gaskiya Allah ya yi halitta don Ameesha kam babu inda Allah ya rage ta, ta fannin halatta kyakkyawa ce wato (First Class) a jin farko, gata doguwa, bata da Kiba ko kadan, amma fa akwai ta da hips and braest, komai cif.
********************************
Cikin kwarewa yake driven motar, fuskar sa dauke da wani special smile, haka kawai in ya tuna Ameesha yake jin zuciyar sa fes, sai dai wani bangare na zuciyar sa tana fama da rad'ad'i tare da dana sanin marin da ya mata. A fili ya furta
"Shi is very beautiful girl, duk wanda ya samu wannan matsayin mata lallai ya more."
Wayarsa ce ta soma ruri a lamar tana neman agaji, da sauri ya dauki wayar ganin mai kiran yasa shi sakin murmushi, picking ya yi tare da karawa a kunne
"Hello Allah hokke sabbugo Nannena, mid'o a nyalli jam, noi sare? " (" Allah ya baki tsawon rai Nannena, fatan kina lafiya ya gida?)
" Jamni tawon Asmad mid'o yela wala billare fere kam.... " (" lafiya Lau Asmad fatan kaima baka da matsala?)
" A'a Nanne wala ko d'ume, jottama mid'o lawol Wartugo sare." ("a'a Nanne babu matsalar komai, yanzu haka ina hanyata ta dawowa gida")
"Allah wadde jam amma a hakkilina lawol anani naa barkantejo.... " (" Allah ya dawo min da kai lafiya Amma ka kula da kyau kaji dan Albarka.")
Murmushi ya yi lokacin da ya kammala waya da mahaifiyar nasa,yana jin farin cikin yadda Nannen shi ke bashi kula, cikin mintina k'alilan ya isa unguwar su, bakin wani makeken get naga ya nufa, hon ya yi cikin sauri mai gadin ya wangale masa get din, wow masha Allah wannan rantsatsen gida haka, gida ne babba ginin zamani, Kai da ganin gidan kasan an kashi kudi, da ka shigo gidan da dakin maigadi zaka soma karo, gefen dama kuma, wani dan dakine aka gina da alama na generator ne, sai wasu flowers da aka daddasa masu kyau, su suka kuma sa gidan ya had'u, gefe guda kuma parking space ne, motoci jere a ciki masu dan banzan kyau.
Sai mutum yayi dan tafiya kafin yasa da kansa da ainahin cikin gidan.
A parking space ya faka motar sa, sannan ya fito tare da d'aukan laidar da ya yi sayayya a Shahad din, kofar babban falon gidan ya shiga bakin sa dauke da sallama, wata kyakkyawan macece wacce bazata wuce shekaru 40 zuwa 42 zaune cikin hadadden falon, babban falo ne wanda aka kawata sa da wasu manya manyan kujeru na alfarma, ga wani carpet mai shegen kyau wanda ya fito da ainahin kyaun falon, kalarsa da kujerun d'aya, wato brown color, haka ma labulen, babban plasma TV ne manne a bangon falon.
Kallo daya zakiyi wa matar kasan bafulatana ce, fara ce fuskar ta kunshe da annuri, macece mai riko da Addini don hannunta rike yake da wani littafin Addu'oi tana karantawa, jin sallamar dan nata yasa tayi saurin d'agowa fuska d'auke da murmushi ta amsa masa sallamar.
Inda take zaune ya 'karasa, zama ya yi kusa da kafarta tare da lank'washe 'kafarsa, ya soma gaidata, shafa kansa tayi tace
"Ja66ama Asmad, awartii Jam... " (barka da zuwa Asmad ka dawo lafiya?)
" Jamni tawon Nanne, sai welo minanata... " (lafiya Lau Nanne sai dai ina jin matukar yunwa).
" Ta damu mitimmini nyamdu.... "(karka damu akwai abinci, ban dade da gamawa ba.)
" Yawwa Nanne 6ewaddina aam sudu aam, hiddeko mi wurta yiwugo..." (Yawwa Nanne a kawo min bedroom dina yanzu, kafin na fito wanka.)
"To ha ladidi waddine.... " (bari ladidi ta kawo maka.)
" A'a Nanne miyid'a 6ingel d'o nastimi sudu aam, toi aneesa ko'o huwata, hokku moo ne o wadda..." ( "a'a Nanne ban son wannan Yarinyar tana shigar min bedroom, ki dai Ba Aneesa ita aikin me takeyi?)
" To yahu hami hokka aneesa man waddine..." ("To jeka Aneesa zata kawo maka.")
"Yawwa Nanne hanju wad'i miyid'i Ma..." ("Yawwa Nanne shi yasa nake Kara sonki."
Asmad ya yi maganar yana Mika mata, d'aya daga cikin ledar da ya shigo da shi, amsa ta yi tare da sanya masa Albarka, shi kuma ya fita tare da nufa 'bangaren sa.
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:01 PM] Zulayheart Rano: [4/15, 4:00 PM] Zulaiha Rano: *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* *(NWA)*
*SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Please fans kuyi hakuri anyi mistake a pagen ɗin jiya amma gashi yanzu na gyara da fatan zakuyi min afuwa,ku cigaba da bibiyar littafi*
*Nice dai Zulayheart Rano*
*4*
Asmad na wucewa Nanne ta soma 'kwalawa Aneesa kira, cikin sanyin murya ta amsa da
"Na' am Nanne ga ni"
Aneesa ta fada lokacin da ta isa wajen Nannen.
"Yawwa yi sauri ki hada wa Hammanki Asmad abinci, ki kai masa bangaren sa."
Murmushi ta saki jin Nanne ta ambaci Asmad.
"To Nanne."
Ta yi maganar tana nufa hanyar kicin din, cikin kankanin lokaci har ta shirya masa duk wani abu da suka dafa ta nufi, bangaren da shi, a k'ofar falon ta tsaya tana sallama, Asmad dake fitowa daga toilet ya amsa, tare da buɗe mata ya dan matsa ta ida shiga bedroom ɗin.
Kallon sa ta yi cikin wani irin shauki, bayan ta aje tire ɗin tace
"Hamman Asmad Sannu da dawowa"
"Yawwa." ya amsa yana goge kanshi da karamin towel.
Tsayawa ta yi tana kallon sa, a rayuwarta tana mugun son Asmad sai dai tasan, ta makaro don bata cikin irin matan da Asmad yake so, domin duk wani hanya da zata bi don shawo hankalinsa ta yi amma a banza.
"Ke tunanin me kike yi da bazaki wuce ba, kin wani sani gaba kina kallo kamar na zamar maki bak'o?"
Dan murmushi ta yi ta ce
"Lah yi hakuri Hamman, dama so nake nace maka ina son zuwa wajen saloon."
"Anjima ki amsa kudi a wajen Nanne, jeki ina son gama shiryawa."
Jiki a sanyaye Aneesa ta bar ɗakin, ba don ranta ya so ba. Aneesa 'yar k'anwar Nanne ce ta zo daga Adamawa, da yake dama duk sanda ta samu hutun school to anan kano gidan su Asmad take yin hutun ta. Kamar ko yaushe wannan karon ma hutu ta samu, Aneesa budurwa ce kyakkyawar gaske, tana da dan jiki sai dai bata da tsawo, shekarun ta Ashirin da haihuwa, a fuska mutumiyar kirki ce sak, amma akwai ɓoyayyen hali a tattare da ita, tun tasowanta take son Asmad din, sai dai shi bata tata yake ba.
Falon Nanne ta koma, a inda ta barta na ta sameta, kasa tayi da murya tace
"Nanne inji Hamman wai ki bani kudi anjima zani saloon."
"Ba dai yau ba, sai gobe don yanzu kam yamma ta soma yi."
"To Nanne." Aneesa ta yi maganar cikin sanyi.
cikin kwanciyar hankali, Asmad ya gama shirin sa, sosai ya yi kyau, domin Asmad kyakkyawan bafulatanin garin Adamawa ne.
*Asmad Abubakar ɗan Fullo* shi ne cikakken sunan sa, mahaifinsa Alhaji Abubakar da mahaiyarsa Hajiya Binta duk haifaffun garin Adamawa ne, kasuwan ci ya kawo mahaifinsa kano.
Allah ya ba Alhaji Abubakar dukiya, sosai ɗa ɗaya Allah ya basu shine Asmad, ya taso cikin gata ta ko wane fanni, sai dai ya samu ingantaciyar tarbiya, duk da kasancewar sa shi ɗaya Allah ya ba iyayen sa, akwai shi da nutsuwa da hankali, shekaran sa ashirin da takwas da haihuwa,
Nanne takasance mece ce mai hankali da tunani, ko da yaushe fuskar ta a sake take, mace ce masaniyar Alkur'ani mai girma, Kuma mai aiki da shi, shi yasa sam bata yadda aka ɓata Asmad da wasu munanan d'abi'u ba, amma fa dai-dai da minti ɗaya in ka zauna da su zaka fahimci tsananin son da Nanne ke masa, don bata iya ɓoye son Asmad a gaban kowa, duk da kasance warta bafulatana.