Sashe 15
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To." Ta amsa tana mik'ewa, bata jima ba ta fito kwanciya ta yi tana addu'ar bacci, bata daɗe da kwanciya ba bacci ya kwashe ta.
Murmushi Dr ya yi ganin har bacci ya kwashe Ameesha, lallai bata da wuyar bacci, sai a lokacin ya soma ci, sai da ya koshi sannan ya tattara kayan ya kai kicin, dawowa ya yi yana tofe ta da addu'a ya rufe ta da bargo tare da kara mata gudun AC sannan ya fita.
*YAR MUTAN RANO*
[10/8, 8:17 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga khadija s Muhammad My Besty*
*40*
Bedroom ɗinsa ya nufa, sai da ya soma rage kayan jikinsa sannan ya faɗa toilet ruwa ya watsawa jikinsa, bayan ya fito ya gabatar da sallah, jikinsa ya shafe da mai tare da feshe ko ina da turarr, kayan bacci ya sanya sai ya bi lafin gado bakin sa dauke da addu'a, bai wani dade ba bacci ya yi a won gaba da shi, mai cike da mafarkin Ameesha. Kiran sallar asuba ya farkar da shi, mika ya yi tare da addu'a kana ya nufi toilet ya dauro alwala, bai ta yar da sallah ba sai da ya je dakin Ameesha wacce ke sharar bacci, a hankali ya matsa inda take tare da kai lallausan hannunsa fuskarta yana mata waiwayi.
Buɗe idonta ta yi mai cike da bacci, ta zuba su bisa fuskar Dr.
"Lokacin sallah ya yi tashi ki yi."
Mika ta yi tare da hamma alamar dai bacci bai isheta ba, ta amsa da
"To."
Yana zaune har ta shiga ta fito, sannan ya jasu sallah suna idarwa Ameesha ta sanyaya murya ta ce
"Ina kwana Dr!"
"Lafiya lau Heartbeat fatan kin tashi lafiya ya sabon waje?"
Murmushi ta yi kanta a kasa ta ce "Alhamdulillah!"
"Madallah! Yanzu dai nasan kina da buk'atar hutu, je ki kwanta ki huta zuwa anjima."
Mik'ewa ta yi ta nufi gadon, shima Dr gadon ya nufa ya kwanta cikin hikima ya jawota jikinsa tare da rungumota, kamar zai mai da ta ciki duk da son jiki irin na Ameesha amma ganin yadda Dr ya cusata jikinsa sai ta fara k'ok'ari janye jikinta, shi kuma ya ki barinta, gajiya ta yi ta barshi a haka bacci ya kwashe su.
Basu farka ba sai karfe tara, Dr ne ya soma tashi sannan Ameesha bed ɗinsa ya nufa don yin wanka, shaf shaf Dr ya yi wanka ya fita, kai tsaye bangaren Aneesa ya nufa.
A hakimce ya ganta zaune kan kujera, ko sallamar da ya yi kin amsa masa ta yi
"Kin tashi lafiya?"
Banza ta kuma masa, bai yi zuciya ba ya kuma faɗin
"Kin yi break ne?"
Mtsss ta ja tsaki ta ce
"Ina ruwanka da break ɗin na? Kai dai ba kana can tare da matarka ba, kaga kenan rashin yin break na ba matsalar ka ba ce." Tana dire maganar ta yi shigewarta bedroom.
Tsayawa kawai Dr ya yi yana kallon Aneesa, tun yana mamakin halinta zuwa yanzu har ya daina, nannauyan ajiyar zuciya ya sauke tare da kaɗa kai ya fita.
Mota ya ɗauka ya fita, don nemo masu abin da za su ci, bai ta de ba ya dawo, wannan karon ma falonta ya shiga, mika mata tek away din ya yi ba tare da ya ce komai ba ya fita, yana jin lokacin da ja tsaki.
A bangaren Ameesha bayan Dr ya fita itama toilet ta shiga wanka ta sillo daure da towel gaban madubi ta yi masauki, duk ilahirin jikinta ta shafe da mai kafin ta nufi wordrop da niyyar dauko kayanta, sai jin sallamar Dr ta yi take wani irin kunya ta kamata, motsi ma kasawa ta yi don kunya.
"Heartbeat baki gama shiryawa ba?" Shiru ta yi ta kasa ko da ɗago kai.
Ganin taki magana yasa ya karasa inda take yana faɗin
"Kinga Wallahi yunwa nake ji fa kuma nasan kema haka Please bari na shirya ki." Ya yi maganar yana sa hannu cikin wordrop ɗin, kaya ya dauko mata riga da siket da pant and bra, aje su ya yi kan gado tare da riko hannunta.
"Please Dr ka barni zan iya sawa fa." A hankali ta yi maganar.
"No! Bana so ki wahala bari na shirya ki kawai."
"Please.. "
Ko sauraron maganar ta bai yi ba, sai ma fara sanya mata pant da bra, tsaf ya shirya ta har yana shafa mata hoda, ita kam sai turo baki take har da kukan sangarta, hannunta ya ja sai falo a dining ya yi mata masauki, don ya yi masu tek away, tsaf ya shirya masu komai a kan dining.
Da kansa ya zuba mata komai sannan ya soma bata shi ma yana ci, suna ci suna soyayyar su har suka gama, tashi Ameesha ta yi tare da kwashe duk wani kaya da suka bata ta yi kicin da su, bata fito ba sai da ta wanke tare da gyara kicin ɗin. Dr na zaune shi kadai a falon yana jiran ta fito amma ya ji shiru sai kawai ya bita kicin ɗin, zaro ido ya yi cikin mamaki ya ce
"Heartbeat aikin me kike yi kuma?"
Murmushi ta saki ta ce
"Dr gyara kicin nake yi."
"Me yasa baki kirani ba?"
"In kiraka ka yi min me?" Da mamaki ta yi tambayar.
"Aikin mana." ya bata amsa.
"Hmmm! Dr kenan ai wannan ba irin aikinka bane nawa ne don haka na hutace ka." Yadda take maganar kawai abin birgewa ce. Domin har kasala ta saukarwa Dr.
"Ni dai ban yadda da wayonki ba, Heartbeat kullum nafi so ki rika hutawa kinji ko?" Ya yi maganar yana jan hancinta.
Dariya suka yi gaba daya, ta ce
"Na daina Dr."
"Yawwa autar Ummi mu je mu gaida Aneesa."
"To." Ta amsa tana tafiya.
Yana rike da hannunta suka yi sallama a falon Aneesa, Aneesa wacce ke zaune ta buga uban tagumi saurin ɗago da kai ta yi, tana amsawa cikin murmushin karfin hali ganin Dr da Ameesha. Ji ta yi kamar ta tashi ta shake Ameesha, wani irin kishin Dr ke a zalzalar ta, da kyar ta yi control ɗin kanta ta tattaro nutsuwarta ta furta masu
"Sannun ku da zuwa."
"Yawwa." Yawwa Dr ya amsa .
Yana zama a kan kujera Ameesha kuwa a kasa kusa da kafar Dr.
"Hamman ina kwana?"
"Lafiya lau My Anee ya kika tashi?"
"Lafiya lau."
"Ina kwana?" Ameesha ta faɗa cikin sanyin murya.
"Lafiya." Shi ne amsar da Aneesar ta bata, bayan ta dauki kusan minti biyar kafin ta amsa tana aika mata harara.
Gyaran murya Dr ya yi, wanda yasa duk suka nutsu tare da maida hankali kansa, godiya ya soma yi ga Allah da ya nuna masa wannan rana, sannan ya soma masu nusiha cikin kwantar da murya akan su zauna lafiya da junansu baya son tashin hankali. Shiru suka masa har ya gama sannan ya tambaye su ko da mai wata matsala
"Babu." Ameesha ta ba shi amsa.
Aneesa kam banza ta masa sai jijjiga kai da hura hanci take yi, ko kallon inda suke bata yi ba.
"Don Allah ku zauna lafiya, matuk'ar kuka zauna lafiya to kwanciyar hankalina ne, haka in akasin zaman lafiya ta samu wallahi tashin hankalina ne, ku rika kai zuciya nesa ku yi koyi da kishin matan Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama."
"Allah ya bamu iko." Cikin siririyar murya ta yi maganar.
Aneesa kam ka sa cewa komai ta yi domin, ji ta yi wani kuka yana shirin zuwa mata, tana son Dr son da batawa kanta tana matukar kishinsa wanda har take jin kamar ba zata iya takwara zuciyarta ba, don haka ganin ya gama sai ta mik'e kamar dai wata kububuwa ta yi shigewarta bedroom
Ameesha kam hamma ta saki, don ta gaji da zaman, kallonta Dr ya yi ya ce
"Ya dai autar Ummi bacci ko?"
Kai ta gyaɗa alamar "eh."
"Ok tashi mu je ki kwanta." Ya yi maganar yana k'ok'arin tashi tsaye.
" *Wai Auta*! Aneesa ta maimaita sunan, wato ma ita ce Auta, sai wani narkewa ta ke masa, hmmmm! Zan yi maganin ku daga ke har shi, ganin yana niyyar tafiya yasa Aneesa ta ce
"Hamman ina son zuwa gidan Nenne, domin yau yan Adamawa zasu koma zan je masu sallama." Ta yi maganar ne tana maida kwallar da suke niyyar zubowa.
"Allah ya kiyaye hanya." Ya yi maganar yana mik'ewa tsaye rike da hannun Ameesha.
Kallonsa ta yi cikin wani irin yanayi, hankalinta ya tashi ganin yadda Dr ya mata, don haka suna fita ta saki wani irin kuka mai cin rai, tana bakin ciki da Auren Dr ta kula son da Dr kewa Ameesha ko kwansa baya mata, lallai sai ta mik'e tsaye domin ta samowa kanta yanci.
Dr kam suna fita daga falon ɗaga Ameesha ya yi sama tare da rungumeta, ita kuma sai ciccila kafa take alamar ya sauketa, bai sauketa ba sai ma ci gaba da tafiya da ya yi har suka shiga falonta, a nan ma bai sauketa ba sai juyata da yake kamar wata yar baby.
Kukan sangarta ta fashe masa da shi, ko hawaye babu tana ta bubbuga masa kirji
"Lalala autar Ummi an ya kuwa kina cin abinci?"
"Ni dai ka saukeni gaskiya Dr."
"Allah ba zan saukeki ba, tambayarki nake kina cin abinci kuwa?"
"Ina ci sosai ma, amma m e ka gani Dr?"
"Sam baki da nauyi kamar na ɗauki yar shila."
"Ni dai saukeni." Ta yi maganar tana turo baki.
Bai sauketa ba sai da ya gama shilla sama, sannan ya direta a kan kujera sai dariya suke yi abin su, kara rungumota jikinsa ya yi yana sinsinar sumar kanta, hannunsa na wasa da sassan jikinta jikin Ameesha duk ya gama saki da salon wasannin da Dr yake mata, a haka bacci ya kwashe su kar'ar wayar Dr e ta farkar da su.
Sunan Nenne ya gani a kan screen ɗin wayar, da sauri ya daga tare da sallama.
Bayan sun gaisa take tambayarsa ina Ameesha.
"Gata nan Nenne bari na bata." Da yake ta tashi har ta bude ido.
Mika mata wayar ya yi yana faɗin "Nenne ce ke son magana da ke."
Murmushi Dr ya yi ganin har bacci ya kwashe Ameesha, lallai bata da wuyar bacci, sai a lokacin ya soma ci, sai da ya koshi sannan ya tattara kayan ya kai kicin, dawowa ya yi yana tofe ta da addu'a ya rufe ta da bargo tare da kara mata gudun AC sannan ya fita.
*YAR MUTAN RANO*
[10/8, 8:17 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga khadija s Muhammad My Besty*
*40*
Bedroom ɗinsa ya nufa, sai da ya soma rage kayan jikinsa sannan ya faɗa toilet ruwa ya watsawa jikinsa, bayan ya fito ya gabatar da sallah, jikinsa ya shafe da mai tare da feshe ko ina da turarr, kayan bacci ya sanya sai ya bi lafin gado bakin sa dauke da addu'a, bai wani dade ba bacci ya yi a won gaba da shi, mai cike da mafarkin Ameesha. Kiran sallar asuba ya farkar da shi, mika ya yi tare da addu'a kana ya nufi toilet ya dauro alwala, bai ta yar da sallah ba sai da ya je dakin Ameesha wacce ke sharar bacci, a hankali ya matsa inda take tare da kai lallausan hannunsa fuskarta yana mata waiwayi.
Buɗe idonta ta yi mai cike da bacci, ta zuba su bisa fuskar Dr.
"Lokacin sallah ya yi tashi ki yi."
Mika ta yi tare da hamma alamar dai bacci bai isheta ba, ta amsa da
"To."
Yana zaune har ta shiga ta fito, sannan ya jasu sallah suna idarwa Ameesha ta sanyaya murya ta ce
"Ina kwana Dr!"
"Lafiya lau Heartbeat fatan kin tashi lafiya ya sabon waje?"
Murmushi ta yi kanta a kasa ta ce "Alhamdulillah!"
"Madallah! Yanzu dai nasan kina da buk'atar hutu, je ki kwanta ki huta zuwa anjima."
Mik'ewa ta yi ta nufi gadon, shima Dr gadon ya nufa ya kwanta cikin hikima ya jawota jikinsa tare da rungumota, kamar zai mai da ta ciki duk da son jiki irin na Ameesha amma ganin yadda Dr ya cusata jikinsa sai ta fara k'ok'ari janye jikinta, shi kuma ya ki barinta, gajiya ta yi ta barshi a haka bacci ya kwashe su.
Basu farka ba sai karfe tara, Dr ne ya soma tashi sannan Ameesha bed ɗinsa ya nufa don yin wanka, shaf shaf Dr ya yi wanka ya fita, kai tsaye bangaren Aneesa ya nufa.
A hakimce ya ganta zaune kan kujera, ko sallamar da ya yi kin amsa masa ta yi
"Kin tashi lafiya?"
Banza ta kuma masa, bai yi zuciya ba ya kuma faɗin
"Kin yi break ne?"
Mtsss ta ja tsaki ta ce
"Ina ruwanka da break ɗin na? Kai dai ba kana can tare da matarka ba, kaga kenan rashin yin break na ba matsalar ka ba ce." Tana dire maganar ta yi shigewarta bedroom.
Tsayawa kawai Dr ya yi yana kallon Aneesa, tun yana mamakin halinta zuwa yanzu har ya daina, nannauyan ajiyar zuciya ya sauke tare da kaɗa kai ya fita.
Mota ya ɗauka ya fita, don nemo masu abin da za su ci, bai ta de ba ya dawo, wannan karon ma falonta ya shiga, mika mata tek away din ya yi ba tare da ya ce komai ba ya fita, yana jin lokacin da ja tsaki.
A bangaren Ameesha bayan Dr ya fita itama toilet ta shiga wanka ta sillo daure da towel gaban madubi ta yi masauki, duk ilahirin jikinta ta shafe da mai kafin ta nufi wordrop da niyyar dauko kayanta, sai jin sallamar Dr ta yi take wani irin kunya ta kamata, motsi ma kasawa ta yi don kunya.
"Heartbeat baki gama shiryawa ba?" Shiru ta yi ta kasa ko da ɗago kai.
Ganin taki magana yasa ya karasa inda take yana faɗin
"Kinga Wallahi yunwa nake ji fa kuma nasan kema haka Please bari na shirya ki." Ya yi maganar yana sa hannu cikin wordrop ɗin, kaya ya dauko mata riga da siket da pant and bra, aje su ya yi kan gado tare da riko hannunta.
"Please Dr ka barni zan iya sawa fa." A hankali ta yi maganar.
"No! Bana so ki wahala bari na shirya ki kawai."
"Please.. "
Ko sauraron maganar ta bai yi ba, sai ma fara sanya mata pant da bra, tsaf ya shirya ta har yana shafa mata hoda, ita kam sai turo baki take har da kukan sangarta, hannunta ya ja sai falo a dining ya yi mata masauki, don ya yi masu tek away, tsaf ya shirya masu komai a kan dining.
Da kansa ya zuba mata komai sannan ya soma bata shi ma yana ci, suna ci suna soyayyar su har suka gama, tashi Ameesha ta yi tare da kwashe duk wani kaya da suka bata ta yi kicin da su, bata fito ba sai da ta wanke tare da gyara kicin ɗin. Dr na zaune shi kadai a falon yana jiran ta fito amma ya ji shiru sai kawai ya bita kicin ɗin, zaro ido ya yi cikin mamaki ya ce
"Heartbeat aikin me kike yi kuma?"
Murmushi ta saki ta ce
"Dr gyara kicin nake yi."
"Me yasa baki kirani ba?"
"In kiraka ka yi min me?" Da mamaki ta yi tambayar.
"Aikin mana." ya bata amsa.
"Hmmm! Dr kenan ai wannan ba irin aikinka bane nawa ne don haka na hutace ka." Yadda take maganar kawai abin birgewa ce. Domin har kasala ta saukarwa Dr.
"Ni dai ban yadda da wayonki ba, Heartbeat kullum nafi so ki rika hutawa kinji ko?" Ya yi maganar yana jan hancinta.
Dariya suka yi gaba daya, ta ce
"Na daina Dr."
"Yawwa autar Ummi mu je mu gaida Aneesa."
"To." Ta amsa tana tafiya.
Yana rike da hannunta suka yi sallama a falon Aneesa, Aneesa wacce ke zaune ta buga uban tagumi saurin ɗago da kai ta yi, tana amsawa cikin murmushin karfin hali ganin Dr da Ameesha. Ji ta yi kamar ta tashi ta shake Ameesha, wani irin kishin Dr ke a zalzalar ta, da kyar ta yi control ɗin kanta ta tattaro nutsuwarta ta furta masu
"Sannun ku da zuwa."
"Yawwa." Yawwa Dr ya amsa .
Yana zama a kan kujera Ameesha kuwa a kasa kusa da kafar Dr.
"Hamman ina kwana?"
"Lafiya lau My Anee ya kika tashi?"
"Lafiya lau."
"Ina kwana?" Ameesha ta faɗa cikin sanyin murya.
"Lafiya." Shi ne amsar da Aneesar ta bata, bayan ta dauki kusan minti biyar kafin ta amsa tana aika mata harara.
Gyaran murya Dr ya yi, wanda yasa duk suka nutsu tare da maida hankali kansa, godiya ya soma yi ga Allah da ya nuna masa wannan rana, sannan ya soma masu nusiha cikin kwantar da murya akan su zauna lafiya da junansu baya son tashin hankali. Shiru suka masa har ya gama sannan ya tambaye su ko da mai wata matsala
"Babu." Ameesha ta ba shi amsa.
Aneesa kam banza ta masa sai jijjiga kai da hura hanci take yi, ko kallon inda suke bata yi ba.
"Don Allah ku zauna lafiya, matuk'ar kuka zauna lafiya to kwanciyar hankalina ne, haka in akasin zaman lafiya ta samu wallahi tashin hankalina ne, ku rika kai zuciya nesa ku yi koyi da kishin matan Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama."
"Allah ya bamu iko." Cikin siririyar murya ta yi maganar.
Aneesa kam ka sa cewa komai ta yi domin, ji ta yi wani kuka yana shirin zuwa mata, tana son Dr son da batawa kanta tana matukar kishinsa wanda har take jin kamar ba zata iya takwara zuciyarta ba, don haka ganin ya gama sai ta mik'e kamar dai wata kububuwa ta yi shigewarta bedroom
Ameesha kam hamma ta saki, don ta gaji da zaman, kallonta Dr ya yi ya ce
"Ya dai autar Ummi bacci ko?"
Kai ta gyaɗa alamar "eh."
"Ok tashi mu je ki kwanta." Ya yi maganar yana k'ok'arin tashi tsaye.
" *Wai Auta*! Aneesa ta maimaita sunan, wato ma ita ce Auta, sai wani narkewa ta ke masa, hmmmm! Zan yi maganin ku daga ke har shi, ganin yana niyyar tafiya yasa Aneesa ta ce
"Hamman ina son zuwa gidan Nenne, domin yau yan Adamawa zasu koma zan je masu sallama." Ta yi maganar ne tana maida kwallar da suke niyyar zubowa.
"Allah ya kiyaye hanya." Ya yi maganar yana mik'ewa tsaye rike da hannun Ameesha.
Kallonsa ta yi cikin wani irin yanayi, hankalinta ya tashi ganin yadda Dr ya mata, don haka suna fita ta saki wani irin kuka mai cin rai, tana bakin ciki da Auren Dr ta kula son da Dr kewa Ameesha ko kwansa baya mata, lallai sai ta mik'e tsaye domin ta samowa kanta yanci.
Dr kam suna fita daga falon ɗaga Ameesha ya yi sama tare da rungumeta, ita kuma sai ciccila kafa take alamar ya sauketa, bai sauketa ba sai ma ci gaba da tafiya da ya yi har suka shiga falonta, a nan ma bai sauketa ba sai juyata da yake kamar wata yar baby.
Kukan sangarta ta fashe masa da shi, ko hawaye babu tana ta bubbuga masa kirji
"Lalala autar Ummi an ya kuwa kina cin abinci?"
"Ni dai ka saukeni gaskiya Dr."
"Allah ba zan saukeki ba, tambayarki nake kina cin abinci kuwa?"
"Ina ci sosai ma, amma m e ka gani Dr?"
"Sam baki da nauyi kamar na ɗauki yar shila."
"Ni dai saukeni." Ta yi maganar tana turo baki.
Bai sauketa ba sai da ya gama shilla sama, sannan ya direta a kan kujera sai dariya suke yi abin su, kara rungumota jikinsa ya yi yana sinsinar sumar kanta, hannunsa na wasa da sassan jikinta jikin Ameesha duk ya gama saki da salon wasannin da Dr yake mata, a haka bacci ya kwashe su kar'ar wayar Dr e ta farkar da su.
Sunan Nenne ya gani a kan screen ɗin wayar, da sauri ya daga tare da sallama.
Bayan sun gaisa take tambayarsa ina Ameesha.
"Gata nan Nenne bari na bata." Da yake ta tashi har ta bude ido.
Mika mata wayar ya yi yana faɗin "Nenne ce ke son magana da ke."