Sashe 24
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu musu Abba ya yadda, sai da suka fita can nesa da jama'a suka tsaya, sannan Abba ya bama ya Jaheed umarnin ya karanta, take ko ya buɗe ya karanta masu.
Hankalin Abba ba karamin tashi ya yi da jin abin da takardar ta kunsa ba, nazari ya yi kamar na minti biyu da ya ce
"Mu je kawai Alhaji a daura auren, ka zama wakilin amarya ni zan zama wakilin ango."
Aiko haka aka yi cikin karamin lokaci aka daura auren, ana gama ɗaura auren Abba ya saki ajiyar zuciya take wata ni'ima ta saukar masa, hankalinsa ya kwanta.
Sai dai kuma a waje mutane duk sun cika da mamakin yadda aka canza akalar daurin auran kamar yadda suka gani a kati, haka dai suka gama haɗa hadar su
Abba kam yana gama sallamar manyan bakin da ya gayyata cikin gida ya shiga, falonsa ya shiga tare da cire babbar rigarsa wayarsa ya ɗauka ya kira Ummi lokacin tana cikin jama'a babu wayar a kusa da ita sai Aunty Saude ta kawo mata.
Tana duba Number din ta yi saurin ɗauka
"Ki sameni a falona." Shi ne kaɗai abin da Abba ya faɗa ya kashe wayar, ya soma sintiri cikin dakin, yana jan tsaki. A haka Ummi ta isa falon bakinta dauke da sallama.
"Lafiya Alhaji?" ta faɗa bayan ta kammala karantar halin da ya ke ciki.
"Babu lafiya Halima." Ya bata amsa a takaice.
"Me ya faru? Ta kuma masa tambayar hankali tashe.
"Babu lafiya."
"Ba'a daura auren ba ne?"
"An daura sai dai an samu canji."
"Wani irin canji kuma Alhaji?"
"Canjin ango aka samu."
"Ango kuma? To dawa aka ɗaura auren?"
"Da ..."
_Ku biyo ni don jin dawa aka daura auren, ni ce dai_
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*24*
Zama ya yi akan kujera, don duk wannan maganar da suke yi a tsaye ya ke ya ce
"Wato Halima da mutuncina da komai aka so tozartani, babu komai domin Allah ya kawo canji mafi Alhairi."
"Alhaji ka fara maganar kuma yanzu ka dauko wata, wacce ban fahimci komai daga ciki ba."
"Haba menene abin saurin tambaya kuma? Ai gani gaki dole ne kisan komai da ke faruwa, Alhaji Mansur ya bani mamaki matuka ya dasa min bakin ciki a zuciyata."
Tagumi Ummi ta yi tare da zuba masa ido tana kallonsa,har zuwa wannan lokacin bata gane inda maganarsa tasa gaba ba. Ganin ta kosa ta san komai sai Abba ya mika mata takaddan ya ce karanta wannan.
Cikin sauri tasa hannu ta amsa tare da buɗewa ga abinda sakon ya kunsa.
*Malam Alhaji Taheer kenan, nasan ya zuwa yanzu kun riga da kun hallara wajen daurin aure ko? To kar kayi mamakin rashin ganina da jama'ata, don tuni aka daura auren Najeeb da matarsa lafiyayya, na faɗa maka maganar gaskiya shi ne ka nema wa mahaukaciyar yarka miji dai dai ita, amma fa ba dai Najeeb nawa ba, don shi lafiyayye ne kuma lafiyayyen mata zai aura.*
*Wato tun lokacin da ya kamata ka yi maganar zaka hada su aure ba ka yi ba sai da yarka ta haukace tukun ka ɓullo da maganar don kana son rabuwa da ita, sai ni kuma ka kwaso ka kawo min gida to ba zai yuwu ba, nima bani haɗa zuri'a da mara hankali, don haka ka sama mata miji dai dai da rashin hankalinta, in yaso sai su yi ta haifo maka jikoki marasa hankali sako daga ni ALHAJI MANSUR.*
"inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Shi ne kalmar da Ummi ke maimaitawa a fili.
"Ai dama wallahi jikina ya bani, an so shirya mana walak'anci baccin haka ta ya za'a ki kawo kayan da gidan ango suke kawowa? Tun farko abin da na guda kenan sai gashi ya afku yanzu Alhaji ya kenan za'a yi?"
Ta ci gaba "amma wallahi Alhaji Mansur ya bani kunya ban yi tunanin haka daga gareshi ba."
"Sosai kuwa, domin ko ni lokacin da wasikar ta same ni, gaskiya na yi mamaki don har kiran wayarsa na yi ya kuma tabbatar min da shi ya aikota."
"To ai shi kenan, tunda haka ne yanzu ya za'a yi kenan?"
"Kamar ya fa?" Abba ya tambaya.
"Game da ɗaurin auren mana. Ummi ta bashi amsa.
Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, tare da muskutawa ya ce
"Bayan Jaheed ya gama karantawa kuma na kira Mansur ya kuma tabbatar min da shi ya aiko da takadan."
"Shi ne Alhaji Usman ya ce sam haka ba zai yiwu ba, in samu wani ko da a cikin ya'yan yan'uwana ne a daura da shi, nan ma naga ba wata mafita kada a samu cin mutuncin da yafi na Mansur, sai ga wani mutum ya nufo inda muke tsaye, shi ne fa ya tambaya me yake faruwa take muka sanar sa, sai ya ce n ba damuwa a daura ɗansa duk da a farko na so bijirewa amma sai Alhaji Usman ya hana, nan take na amince amma fa can kasan zuciyata ina tunanin abin da zai je ya dawo."
"Take mahaifinsa ya biya kudin sadaki dubu hamsin kawai na amsa, don irin halarci da ya min duk da ban san kalar ɗan nasa ba, sai dai ina fatan ya kasance mutumin kwarai.
"Ɗazun aka daura auren *ASMAD ABUBAKAR DA MARYAM TAHEER*
"Masha Allah Alhaji Allah ya tabbatar da Alhairi, Ubangiji yasa haka shi ne mafi Alhairi a garemu da ita baki daya."
"Amin." Abba ya amsa
"Yanzu dai ki tashi ki je ki ci gaba da sallamar baki zuwa anjima sai mu kara shawartawa, ni ɗimma da sauran mutanen da zan sallama."
Da to Ummi ta amsa tana fita daga falon, a zuciyarta tana Allah wadai da halin Alhaji Mansur.
A daya bangaren kuma tana addu'a Allah yasa wanda Ameesha ya zame mata bango wajen jin gina. Haka dai a kai ta gudanar da biki har zuwa lokacin da bakin kusa suka tafi sai wanda suka zo daga nesa.
******
"Najeeb ne zaune a wata farfajiya duk da iskar dake kadawa amma shi Najeeb, jin iskar ya ke kamar hucin wuta, kallo ɗaya zaka masa kasan yana cikin muguwar damuwa." Tsaki ya ja mai karfi tare da jawo wayarsa, a gogon wayar ya kalla karfe 2:01a gogon kasar Faransa dai dai da agogo Nigeria karfe goma sha biyu.
Wani murmushi ya saki a fili ya furta "Alhamdulillah! Yau Ameesha ta zama tawa."
"Ya so da Abbansa bai turo shi garin nan ba, musamman da yau ne ranar da ta kasance ranar farin ciki a rayuwarsa, amma sai Abbansa ya turo shi akan wasu kaya wanda shi bai ga wani amfanin su ba." Mtsss ya ja tsaki.
Hankalin Alhaji Mansur kwance yana zaune akan kujerar falonsa, waya kawai yake amsawa daga abokan arzikinsa suna masa murnar daurin auran, Mummy ce ta k'araso falon cikin farin ciki bayan ta zauna ne ta ce
"Sannu Alhaji an daura aure lafiya?"
"Yawwa Hajiya lafiya lau."
"To yanzu Alhaji ina za'a kai yarinyar kasantuwarta mara lafiya, kaga dole tana bukatar masu kula da ita, inda zai yiwu kawai a kawo ta nan har ta samu lafiya."
"Wa ki ke nufi ne?"
"Matar Najeeb mana Ameesha."
"A'a gyara magana dai, ai matar Najeeb sunanta *RUFAIDA*."
Wani zabura Mummy ta yi ta ce
"Ban gane Rufaida ba, ina ce Ameesha ce yar gidan Alhaji Taheer?"
"Haba Hajiya ya ki ke son maida hannun agogo baya? kin san tuni na ce bana son auren nan ke da ɗan ki kuka na ce sai an yi, to da naga na rasa hanyar da zan bi don hanawa shi ne ai na tura Najeeb ɗin kasar Faransa da sunan ya kular min da wasu kaya, na yi haka ne don in samu in cika burina, to kuma Alhamdulillah don buri ya cika..."
"Alhaji an ya kana cikin hankalinka kuwa? Wai kasan abin da kake faɗa ma kuwa?"
"Ras na sani, ce wa na yi da Rufaida aka daura auren ba da wannan mara hankalin yar Taheer ba, don ina son ake haifa min jikoki masu hankali ba mahaukata ba." Ya ida maganar cikin izzah.
"Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Amma kam wallahil azeem Alhaji baka da imani, dama saboda ka tauye hakkin yaron nan ne ka tura shi can kasar? Allah sai ya maku hisabi da shi."
Harara kawai ya ke ta aika mata da shi sannan ya ce
"Kin gama zagina? To wallahi bari ki ji, ke kin yi kaɗan in zartar da hukunci ki ce zaki bijire min, ai tun farko sai da na ce bana son auren kuka na ce, don haka sai na bullo maku ta yadda baku tunani."
"Hmmmm! Wannan kuma matsalar ka ce, amma sam baka wa Najeeb da Alhaji Taheer adalci ba, kuma insha Allahu zaka ga abin da ka aikata masu."
"Ke wallahi ki yi a hankali akan wannan auren kina iya rasa na ki aurn." Yana gama faɗin haka ya tashi tare da barin mata wajen. Kuka Mummy ta fashe da shi domin kuwa abin ya ɓata ranta sosai, addu'a take Allah ya sawa Najeeb dangana akan Ameesha.
*******
Dr dai har yanzu sam jikin babu daɗi domin dai ya kasa cire tunanin Ameesha a zuciyarsa, Nenne ce ta shigo bedroom ɗin hannunta rike da cup, kallon Asmad ɗin ta yi ta ce
"Tashi kasha wannan shayin kana ciwo babu cin abinci!"
Girgiza za kai ya yi ya ce
"A'a Nenne bana jin dadin bakina ne, ki bar shi zuwa anjima zan sha."
"Ka daure dai ko kaɗan ne ka sha ka ji ko?"
Sam Asmad baya k'aunar yiwa Nennensa musu don haka sai ya tashi zaune tare da karbar cup din, kurba biyu ya yi ya ce ya koshi ya aje cup din.
"Ka kira Aneesa ka sanar mata baka da lafiya?"
"A'a Nenne."
"Tom ya kamata dai ka sanar mata, don karta ji shiru."
"To." ya amsa yana gyara kwanciya.
Girgiza kai Nenne ta yi kawai, wayar Asmad dake kan dressing mirror ta dauki kara, Nenne ce ta dauko wayar tare da mika masa.
Ganin Number din Bobbo ne yasa shi ɗauka tare da yin sallama.
"Assalamu Alaikum! Bobbo an wuni lafiya?"
Daga ɗaya bangaren Bobbo ya amsa
Hankalin Abba ba karamin tashi ya yi da jin abin da takardar ta kunsa ba, nazari ya yi kamar na minti biyu da ya ce
"Mu je kawai Alhaji a daura auren, ka zama wakilin amarya ni zan zama wakilin ango."
Aiko haka aka yi cikin karamin lokaci aka daura auren, ana gama ɗaura auren Abba ya saki ajiyar zuciya take wata ni'ima ta saukar masa, hankalinsa ya kwanta.
Sai dai kuma a waje mutane duk sun cika da mamakin yadda aka canza akalar daurin auran kamar yadda suka gani a kati, haka dai suka gama haɗa hadar su
Abba kam yana gama sallamar manyan bakin da ya gayyata cikin gida ya shiga, falonsa ya shiga tare da cire babbar rigarsa wayarsa ya ɗauka ya kira Ummi lokacin tana cikin jama'a babu wayar a kusa da ita sai Aunty Saude ta kawo mata.
Tana duba Number din ta yi saurin ɗauka
"Ki sameni a falona." Shi ne kaɗai abin da Abba ya faɗa ya kashe wayar, ya soma sintiri cikin dakin, yana jan tsaki. A haka Ummi ta isa falon bakinta dauke da sallama.
"Lafiya Alhaji?" ta faɗa bayan ta kammala karantar halin da ya ke ciki.
"Babu lafiya Halima." Ya bata amsa a takaice.
"Me ya faru? Ta kuma masa tambayar hankali tashe.
"Babu lafiya."
"Ba'a daura auren ba ne?"
"An daura sai dai an samu canji."
"Wani irin canji kuma Alhaji?"
"Canjin ango aka samu."
"Ango kuma? To dawa aka ɗaura auren?"
"Da ..."
_Ku biyo ni don jin dawa aka daura auren, ni ce dai_
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:07 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
*24*
Zama ya yi akan kujera, don duk wannan maganar da suke yi a tsaye ya ke ya ce
"Wato Halima da mutuncina da komai aka so tozartani, babu komai domin Allah ya kawo canji mafi Alhairi."
"Alhaji ka fara maganar kuma yanzu ka dauko wata, wacce ban fahimci komai daga ciki ba."
"Haba menene abin saurin tambaya kuma? Ai gani gaki dole ne kisan komai da ke faruwa, Alhaji Mansur ya bani mamaki matuka ya dasa min bakin ciki a zuciyata."
Tagumi Ummi ta yi tare da zuba masa ido tana kallonsa,har zuwa wannan lokacin bata gane inda maganarsa tasa gaba ba. Ganin ta kosa ta san komai sai Abba ya mika mata takaddan ya ce karanta wannan.
Cikin sauri tasa hannu ta amsa tare da buɗewa ga abinda sakon ya kunsa.
*Malam Alhaji Taheer kenan, nasan ya zuwa yanzu kun riga da kun hallara wajen daurin aure ko? To kar kayi mamakin rashin ganina da jama'ata, don tuni aka daura auren Najeeb da matarsa lafiyayya, na faɗa maka maganar gaskiya shi ne ka nema wa mahaukaciyar yarka miji dai dai ita, amma fa ba dai Najeeb nawa ba, don shi lafiyayye ne kuma lafiyayyen mata zai aura.*
*Wato tun lokacin da ya kamata ka yi maganar zaka hada su aure ba ka yi ba sai da yarka ta haukace tukun ka ɓullo da maganar don kana son rabuwa da ita, sai ni kuma ka kwaso ka kawo min gida to ba zai yuwu ba, nima bani haɗa zuri'a da mara hankali, don haka ka sama mata miji dai dai da rashin hankalinta, in yaso sai su yi ta haifo maka jikoki marasa hankali sako daga ni ALHAJI MANSUR.*
"inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Shi ne kalmar da Ummi ke maimaitawa a fili.
"Ai dama wallahi jikina ya bani, an so shirya mana walak'anci baccin haka ta ya za'a ki kawo kayan da gidan ango suke kawowa? Tun farko abin da na guda kenan sai gashi ya afku yanzu Alhaji ya kenan za'a yi?"
Ta ci gaba "amma wallahi Alhaji Mansur ya bani kunya ban yi tunanin haka daga gareshi ba."
"Sosai kuwa, domin ko ni lokacin da wasikar ta same ni, gaskiya na yi mamaki don har kiran wayarsa na yi ya kuma tabbatar min da shi ya aikota."
"To ai shi kenan, tunda haka ne yanzu ya za'a yi kenan?"
"Kamar ya fa?" Abba ya tambaya.
"Game da ɗaurin auren mana. Ummi ta bashi amsa.
Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, tare da muskutawa ya ce
"Bayan Jaheed ya gama karantawa kuma na kira Mansur ya kuma tabbatar min da shi ya aiko da takadan."
"Shi ne Alhaji Usman ya ce sam haka ba zai yiwu ba, in samu wani ko da a cikin ya'yan yan'uwana ne a daura da shi, nan ma naga ba wata mafita kada a samu cin mutuncin da yafi na Mansur, sai ga wani mutum ya nufo inda muke tsaye, shi ne fa ya tambaya me yake faruwa take muka sanar sa, sai ya ce n ba damuwa a daura ɗansa duk da a farko na so bijirewa amma sai Alhaji Usman ya hana, nan take na amince amma fa can kasan zuciyata ina tunanin abin da zai je ya dawo."
"Take mahaifinsa ya biya kudin sadaki dubu hamsin kawai na amsa, don irin halarci da ya min duk da ban san kalar ɗan nasa ba, sai dai ina fatan ya kasance mutumin kwarai.
"Ɗazun aka daura auren *ASMAD ABUBAKAR DA MARYAM TAHEER*
"Masha Allah Alhaji Allah ya tabbatar da Alhairi, Ubangiji yasa haka shi ne mafi Alhairi a garemu da ita baki daya."
"Amin." Abba ya amsa
"Yanzu dai ki tashi ki je ki ci gaba da sallamar baki zuwa anjima sai mu kara shawartawa, ni ɗimma da sauran mutanen da zan sallama."
Da to Ummi ta amsa tana fita daga falon, a zuciyarta tana Allah wadai da halin Alhaji Mansur.
A daya bangaren kuma tana addu'a Allah yasa wanda Ameesha ya zame mata bango wajen jin gina. Haka dai a kai ta gudanar da biki har zuwa lokacin da bakin kusa suka tafi sai wanda suka zo daga nesa.
******
"Najeeb ne zaune a wata farfajiya duk da iskar dake kadawa amma shi Najeeb, jin iskar ya ke kamar hucin wuta, kallo ɗaya zaka masa kasan yana cikin muguwar damuwa." Tsaki ya ja mai karfi tare da jawo wayarsa, a gogon wayar ya kalla karfe 2:01a gogon kasar Faransa dai dai da agogo Nigeria karfe goma sha biyu.
Wani murmushi ya saki a fili ya furta "Alhamdulillah! Yau Ameesha ta zama tawa."
"Ya so da Abbansa bai turo shi garin nan ba, musamman da yau ne ranar da ta kasance ranar farin ciki a rayuwarsa, amma sai Abbansa ya turo shi akan wasu kaya wanda shi bai ga wani amfanin su ba." Mtsss ya ja tsaki.
Hankalin Alhaji Mansur kwance yana zaune akan kujerar falonsa, waya kawai yake amsawa daga abokan arzikinsa suna masa murnar daurin auran, Mummy ce ta k'araso falon cikin farin ciki bayan ta zauna ne ta ce
"Sannu Alhaji an daura aure lafiya?"
"Yawwa Hajiya lafiya lau."
"To yanzu Alhaji ina za'a kai yarinyar kasantuwarta mara lafiya, kaga dole tana bukatar masu kula da ita, inda zai yiwu kawai a kawo ta nan har ta samu lafiya."
"Wa ki ke nufi ne?"
"Matar Najeeb mana Ameesha."
"A'a gyara magana dai, ai matar Najeeb sunanta *RUFAIDA*."
Wani zabura Mummy ta yi ta ce
"Ban gane Rufaida ba, ina ce Ameesha ce yar gidan Alhaji Taheer?"
"Haba Hajiya ya ki ke son maida hannun agogo baya? kin san tuni na ce bana son auren nan ke da ɗan ki kuka na ce sai an yi, to da naga na rasa hanyar da zan bi don hanawa shi ne ai na tura Najeeb ɗin kasar Faransa da sunan ya kular min da wasu kaya, na yi haka ne don in samu in cika burina, to kuma Alhamdulillah don buri ya cika..."
"Alhaji an ya kana cikin hankalinka kuwa? Wai kasan abin da kake faɗa ma kuwa?"
"Ras na sani, ce wa na yi da Rufaida aka daura auren ba da wannan mara hankalin yar Taheer ba, don ina son ake haifa min jikoki masu hankali ba mahaukata ba." Ya ida maganar cikin izzah.
"Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Amma kam wallahil azeem Alhaji baka da imani, dama saboda ka tauye hakkin yaron nan ne ka tura shi can kasar? Allah sai ya maku hisabi da shi."
Harara kawai ya ke ta aika mata da shi sannan ya ce
"Kin gama zagina? To wallahi bari ki ji, ke kin yi kaɗan in zartar da hukunci ki ce zaki bijire min, ai tun farko sai da na ce bana son auren kuka na ce, don haka sai na bullo maku ta yadda baku tunani."
"Hmmmm! Wannan kuma matsalar ka ce, amma sam baka wa Najeeb da Alhaji Taheer adalci ba, kuma insha Allahu zaka ga abin da ka aikata masu."
"Ke wallahi ki yi a hankali akan wannan auren kina iya rasa na ki aurn." Yana gama faɗin haka ya tashi tare da barin mata wajen. Kuka Mummy ta fashe da shi domin kuwa abin ya ɓata ranta sosai, addu'a take Allah ya sawa Najeeb dangana akan Ameesha.
*******
Dr dai har yanzu sam jikin babu daɗi domin dai ya kasa cire tunanin Ameesha a zuciyarsa, Nenne ce ta shigo bedroom ɗin hannunta rike da cup, kallon Asmad ɗin ta yi ta ce
"Tashi kasha wannan shayin kana ciwo babu cin abinci!"
Girgiza za kai ya yi ya ce
"A'a Nenne bana jin dadin bakina ne, ki bar shi zuwa anjima zan sha."
"Ka daure dai ko kaɗan ne ka sha ka ji ko?"
Sam Asmad baya k'aunar yiwa Nennensa musu don haka sai ya tashi zaune tare da karbar cup din, kurba biyu ya yi ya ce ya koshi ya aje cup din.
"Ka kira Aneesa ka sanar mata baka da lafiya?"
"A'a Nenne."
"Tom ya kamata dai ka sanar mata, don karta ji shiru."
"To." ya amsa yana gyara kwanciya.
Girgiza kai Nenne ta yi kawai, wayar Asmad dake kan dressing mirror ta dauki kara, Nenne ce ta dauko wayar tare da mika masa.
Ganin Number din Bobbo ne yasa shi ɗauka tare da yin sallama.
"Assalamu Alaikum! Bobbo an wuni lafiya?"
Daga ɗaya bangaren Bobbo ya amsa