Sashe 40
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To kuma me hadina da auran ka?"
Ta yi maganar tana hararan sa.
"Oh! Ashe fa ba ruwan ki da aurena? Amma ai yana da kyau ko murna ki ta ya ni."
Wani kallo ta watsa masa wanda ya kasa fahimtar ma'anar sa.
Yau dai yana son ya ga shin Ameesha ta na sonsa, in tana sonsa zai tabbatar ,don haka sai ya tashi daga kujerarsa ya matsa inda ta ke, hannun ta ya rik'o ya ce
"Maryam me yasa ki ke min rashin kunya baki ganin girma na, kullum kallon tsana ki ke min?"
Juyar da kai ta yi murya na rawa ta ce
"Please Dr ka sakar min hannu, sauri na keyi fa Ummi na jirana."
"Zan barki amma sai kin bani amsar tambayar da na yi maki."
"Babu komai."
Ameesha ta ba shi amsa, dai dai da zubowar hawayen da ta e ɓoyewa, hankalinsa ya tashi da ganin hawayen Ameesha, don haka cikin sauri ya ce
" Iya sani na na taɓa marin ki a Sahad store, kuma shi ɗin ma wallahi ke ki ka jawo, domin kuwa in da ban mareki ba, to fa babu shakka ni zaki mara, amma ki yi hakuri ga fuska ta ki rama marin."
Maimakon hawayen su tsagaita sai k'ara tsiyaya suke, a kan fuskar ta tama kasa furta komai, don abin da ta ke son ji daga gare shi bai furta mata ba, duk da tasan da kamar wuya ta samu wannan tsadadden kalmar daga gare shi.
Asmad kuwa zuba mata ido ya yi yana kallon ikon Allah, zuwa can yasa hannu cikin aljihu ya cire hankacif na shi ta re da mika mata.
"Sorry Maryam ki bar kuka, ga shi ki share hawayen ki."
Ya kai karshen maganar yana mik'a mata.
Amsa tayi tare da goge hawayen da hankerchief ɗin da ya mika mata, sai ya kuma jan hannunta kamar dai wata karamar yarinya, zuwa kan doguwar kujerar da ke office din, ya zaunar da ita sannan shi ma ya zama .
Sanyaya murya ya yi ya ce...
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:06 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija s Muhammad my Cittah*
*Alhamdulillah Ina godiya da Allah ya kawo mu wannan lokaci, ina son in dakata da typing wannan littafin har sai Allah ya kaimu bayan sallah lafiya, ina wa ɗauka cin musulmai murnar zuwan wannan wata mai alfarma Allah ya sada mu da Alhairin da ke ciki Ubangiji ka bamu rabauta da falalar da ke wannan wata na Ramadan*
_*Har lau dai korafi baya karewa? To duk kuyi hakuri Yar Mutan Rano tana kara ce wa kuyi hakuri ku kara akan na da, insha Allah bayan sallah ba za ku yi korafin rashin typing ba*_ i heart you irin totallyn ɗin nan😍😍
*16*
Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, tare da zubawa Ameesha ido cikin wani irin yanayin da shi kaɗai ke gane wa, cikin taushin murya ya ce
"Magana ta tasa ki kuka?"
Girgiza kai ta yi , ba tare da ta ce komai ba.
"No Maryam in muna magana ki rika buɗe baki Please."
"Ni fa Dr ba maganar ka ta sani kuka ba." A shagwaɓe ta karasa maganar.
Ji ya yi ta bala'in burgeshi,yana ɗaya daga cikin abin da yasa yake sonta kenan.
"To me ya saki kuka in ba maganar ba, na ce baki min Allah ya sanya Alhairin Aure na ba, sai na ga kin fara kuka ko?"
Harara ta watsa masa ta ce
"Ni fa kaina ke ciwo shi ne kawai."
"Hmm Maryam kenan kina da saurin daukar zafi, nifa banga abin tada hankali ba cikin abin nan, in ki ka bi a hankali to komai zai ta fi yadda ki ke mafarkin samu."
Ya yi maganar ta re da kashe mata ido ɗaya.
Saurin ɗago da kai ta yi tana kallon sa, tare da mamakin maganar da ya faɗa "kenan ya san tana sonsa?" Ta yi saurin kawar da tunanin don ta san ba haka ya ke nufi ba.
Mik'ewa ta yi tare da ɗaukar jakarta, ta kuma kallon kyakkyawar fuskasa ta ce
"Dr ni kam zan wu ce don yamma na yi."
Wani tsadadden murmushi ya bata, wanda ya kara wa fuskarsa kyau ya ce
"To Princess sai yaushe kenan?"
"Gobe school zan shiga zuwa sai jibi."
"Ok Allah ya kaimu, mu je na saukeki ko kin zo da mota ne?"
Wani irin daɗi ya ziyarci zuciyar ta , amma sai ta fuske ta ce
"A'a Dr ka barni kawai na hau nafef."
Ta ida maganar tana tafiya.
"Maryam." Ya kira sunan ta da wani irin murya.
Cak Meesha ta tsaya ba tare da ta juyo ba, don yadda ya ambaci sunan sai ta ji kamar duniya babu wanda ya iya fadar sunan kamar shi.
"Mu je na ce maki ko?"
Ya yi maganar yana daukan key.
"Dr ai baka duba petient na ka ba?"
"Dama ba su nazo gani ba, da abin da ya kawo ni, kuma na gani hankalina ya kwanta."
Yana bata amsa ne yana rufe kofar, a tare suke jerawa sun yi mugun da ce wa da juna, don duk wanda ya gansu sai ya yi tunanin miji da mata ne a haka har zuwa inda motarsa ya ke , buɗe mata kofa ya yi ta shiga sannan shima ya zaga.
Yana shiga wayar sa ta soma ringing, da sauri ya dauko don ganin me kiran ɗan murmushi ya saki tare da karawa a kunne
"Hello My Anee ya aka yi?"
Ameesha na jin haka tasan tabbas da matarsa ya ke waya, nan take sai ta ji hankalin ta ya tashi.
Maganar shi ta kuma tsinkaya ya na faɗin
"Haba Anee gani nan a hanyar dawowa, bani minti talatin."
Ya faɗa tare da kashe wayar. Juyo da fuska ya yi yana kallon Ameesha ya ce
"Kinji matata tana kirana wai na daɗe?"
Karamin tsaki ta ja ,ba ta ce masa komai ba, don gaba daya haushin shi da kishin sa suka rufe ta.
Shi ma shiru ya mata ya ci gaba da tukin sa, Ameesha tana nuna masa hanya har suka isa unguwar, a dai dai get din gidan ya faka, kallon sa ta yi ta ce
"Na gode Dr sai da safe."
Harara ya mata ya ce
"Kuma shi kenan iya sallamar da za mu yi?"
Dan ware ido ta yi cikin mamaki ta ce
"Dr wani irin sallama za mu yi wacce ta fi wannan?"
Har yanzu fuskarta ɗauke da mamaki.
Dan sosa keya ya yi ya ce " To ai naga har kin fita ne, ko fa Number din ki bani da?"
"Hmmmm! ta furta da da dai wannan yanayin mamaki ta ce "bani wayar ka nasa ma kafin Abba ya zo ya same ni."
Mik'a mata ya yi ta amsa cikin sauri sauri ta sanya masa, sannan ta nufi get din Asmad na kallonta har ta shige cikin gidan sannan ya saki ajiyar zuciya a fili ya furta
"Allah ka mallaka min Maryam matsayin mata amin." Ya kai karshen maganar yana ta yar da motarsa.
******** ********** *******
Ko da Ameesha ta shiga gidansu da ɗoki ta k'arasa falon, ganin motar Yaya Jaheed ta san shi ɗin ne ya zo, sallama ta doka tare da shiga, wani murmushi ta saki ganin sa zaune a falon da matarsa. Ai da sauri ta isa inda suke tana faɗin "barka da zuwa Yaya" murmushi ya saki cikin jin daɗi ya amsa mata maganar ta.
"A'a Ameesha autar Ummi sai yanzu aka shigo?"
Matar Ya Jaheed ne ta yi maganar. Matsawa kusa da ita ta yi ta ce
"Aunty ina yini?"
"Lafiya ya makarantar?"
"Alhamdulillah." Ameesha ta bata amsa tana nufa hanyar stair. Har ta soma taka matakalar ta tuna bata wa Ummi sannu da gida ba don haka sai ta sauka, bedroom din Ummi ta shiga bakin ta ɗauke da sallama.
Hajiya Halima da ke buɗe k'ofar toilet ta amsa mata cike da kulawa.
"Auta kin dawo?"
"Eh na dawo Ummi."
"To sannu da dawowa,je kiyi wanka abinci yana jiran ki."
"Ummi nifa a koshe na ke, wanka kawai zan yi."
"Ke abin da na ce kenan je ki yi, naga yanzu kwata kwata baki k'aunar cin abinci ko?"
Ummi ta k'arasa maganar tana hararan Ameesha.
Shagwaɓe fuska ta yi ta ce
"Allah Ummi ina ci fa, kawai yau na koshi ne."
"To je ki yi wankan."
"Yawwa Ummina." Ameesha ta faɗa tana fita daga bedroom din.
Bayan ta yi wanka ne ta koma falo inda su Ya Jaheed da matarsa suke, tana zama Meena ta shigo hira suka ci gaba da yi.
*******
"Alhaji wato kasan abin da yasa na nemeka a wannan rana?"
Alhaji Taheer ya yi maganar yana aje cup din da ya sha ruwa.
"Sai ka faɗa Alhaji."
Alhaji Mansur ya yi maganar cikin ɗan murmushi irin na ya ke.
"Dama kan maganar Najeeb ne da Ameesha, na ga soyayyar ta su kullum kara gaba ta ke , shi ne na ce gara asan matsaya."
Wani mummunan faduwar gaba ya ziyarci Alhaji Mansur ya ce "Na shiga uku ni Mansur, kenan burina ba zai cika ba? To wallahi ba zai yiwu ba dole sai na cika abin da na yi niyya, Taheer ba ka isa ba ba zai yiwu."
Amma a fili sai ya kakalo ya ke ya ce
"Yo Alhaji ban da abin ka ai kana iya zartar da hukuncin auren su gaba ɗaya, babu abin da zance sai fatan alheri."
Sosai Alhaji Taheer ya yi farin ciki da jin furucin Alhaji Mansur ɗin, don haka sai ya ce
"To zamu zauna nan da kwana kaɗan don asa rana."
"Allah ya kaimu."
Da wannan hirar suka ci gaba da hirar duniya, sun daɗe sosai ka ɗin su ka yi sallama ko wa ya kama hanyar gidan sa.
Lokacin da Meesha da Najeeb suka samu wannan labarin ba karamin daɗi su ka ji ba, babu kamar Meesha da ta ke murna zata huta da tunanin Dr ɗan fullo, tunda zata auri wanda ta ke so.
*******
"Um um Abba yau fa kai zaka kaini school." Meesha ta yi maganar tana zama kusa da Alhaji Taheer ɗin.
Murmushi ya saki tare da shafa kanta ya ce
Ta yi maganar tana hararan sa.
"Oh! Ashe fa ba ruwan ki da aurena? Amma ai yana da kyau ko murna ki ta ya ni."
Wani kallo ta watsa masa wanda ya kasa fahimtar ma'anar sa.
Yau dai yana son ya ga shin Ameesha ta na sonsa, in tana sonsa zai tabbatar ,don haka sai ya tashi daga kujerarsa ya matsa inda ta ke, hannun ta ya rik'o ya ce
"Maryam me yasa ki ke min rashin kunya baki ganin girma na, kullum kallon tsana ki ke min?"
Juyar da kai ta yi murya na rawa ta ce
"Please Dr ka sakar min hannu, sauri na keyi fa Ummi na jirana."
"Zan barki amma sai kin bani amsar tambayar da na yi maki."
"Babu komai."
Ameesha ta ba shi amsa, dai dai da zubowar hawayen da ta e ɓoyewa, hankalinsa ya tashi da ganin hawayen Ameesha, don haka cikin sauri ya ce
" Iya sani na na taɓa marin ki a Sahad store, kuma shi ɗin ma wallahi ke ki ka jawo, domin kuwa in da ban mareki ba, to fa babu shakka ni zaki mara, amma ki yi hakuri ga fuska ta ki rama marin."
Maimakon hawayen su tsagaita sai k'ara tsiyaya suke, a kan fuskar ta tama kasa furta komai, don abin da ta ke son ji daga gare shi bai furta mata ba, duk da tasan da kamar wuya ta samu wannan tsadadden kalmar daga gare shi.
Asmad kuwa zuba mata ido ya yi yana kallon ikon Allah, zuwa can yasa hannu cikin aljihu ya cire hankacif na shi ta re da mika mata.
"Sorry Maryam ki bar kuka, ga shi ki share hawayen ki."
Ya kai karshen maganar yana mik'a mata.
Amsa tayi tare da goge hawayen da hankerchief ɗin da ya mika mata, sai ya kuma jan hannunta kamar dai wata karamar yarinya, zuwa kan doguwar kujerar da ke office din, ya zaunar da ita sannan shi ma ya zama .
Sanyaya murya ya yi ya ce...
_*Yar Mutan Rano*_
[10/8, 8:06 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
*Sadaukarwa ga Khadija s Muhammad my Cittah*
*Alhamdulillah Ina godiya da Allah ya kawo mu wannan lokaci, ina son in dakata da typing wannan littafin har sai Allah ya kaimu bayan sallah lafiya, ina wa ɗauka cin musulmai murnar zuwan wannan wata mai alfarma Allah ya sada mu da Alhairin da ke ciki Ubangiji ka bamu rabauta da falalar da ke wannan wata na Ramadan*
_*Har lau dai korafi baya karewa? To duk kuyi hakuri Yar Mutan Rano tana kara ce wa kuyi hakuri ku kara akan na da, insha Allah bayan sallah ba za ku yi korafin rashin typing ba*_ i heart you irin totallyn ɗin nan😍😍
*16*
Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, tare da zubawa Ameesha ido cikin wani irin yanayin da shi kaɗai ke gane wa, cikin taushin murya ya ce
"Magana ta tasa ki kuka?"
Girgiza kai ta yi , ba tare da ta ce komai ba.
"No Maryam in muna magana ki rika buɗe baki Please."
"Ni fa Dr ba maganar ka ta sani kuka ba." A shagwaɓe ta karasa maganar.
Ji ya yi ta bala'in burgeshi,yana ɗaya daga cikin abin da yasa yake sonta kenan.
"To me ya saki kuka in ba maganar ba, na ce baki min Allah ya sanya Alhairin Aure na ba, sai na ga kin fara kuka ko?"
Harara ta watsa masa ta ce
"Ni fa kaina ke ciwo shi ne kawai."
"Hmm Maryam kenan kina da saurin daukar zafi, nifa banga abin tada hankali ba cikin abin nan, in ki ka bi a hankali to komai zai ta fi yadda ki ke mafarkin samu."
Ya yi maganar ta re da kashe mata ido ɗaya.
Saurin ɗago da kai ta yi tana kallon sa, tare da mamakin maganar da ya faɗa "kenan ya san tana sonsa?" Ta yi saurin kawar da tunanin don ta san ba haka ya ke nufi ba.
Mik'ewa ta yi tare da ɗaukar jakarta, ta kuma kallon kyakkyawar fuskasa ta ce
"Dr ni kam zan wu ce don yamma na yi."
Wani tsadadden murmushi ya bata, wanda ya kara wa fuskarsa kyau ya ce
"To Princess sai yaushe kenan?"
"Gobe school zan shiga zuwa sai jibi."
"Ok Allah ya kaimu, mu je na saukeki ko kin zo da mota ne?"
Wani irin daɗi ya ziyarci zuciyar ta , amma sai ta fuske ta ce
"A'a Dr ka barni kawai na hau nafef."
Ta ida maganar tana tafiya.
"Maryam." Ya kira sunan ta da wani irin murya.
Cak Meesha ta tsaya ba tare da ta juyo ba, don yadda ya ambaci sunan sai ta ji kamar duniya babu wanda ya iya fadar sunan kamar shi.
"Mu je na ce maki ko?"
Ya yi maganar yana daukan key.
"Dr ai baka duba petient na ka ba?"
"Dama ba su nazo gani ba, da abin da ya kawo ni, kuma na gani hankalina ya kwanta."
Yana bata amsa ne yana rufe kofar, a tare suke jerawa sun yi mugun da ce wa da juna, don duk wanda ya gansu sai ya yi tunanin miji da mata ne a haka har zuwa inda motarsa ya ke , buɗe mata kofa ya yi ta shiga sannan shima ya zaga.
Yana shiga wayar sa ta soma ringing, da sauri ya dauko don ganin me kiran ɗan murmushi ya saki tare da karawa a kunne
"Hello My Anee ya aka yi?"
Ameesha na jin haka tasan tabbas da matarsa ya ke waya, nan take sai ta ji hankalin ta ya tashi.
Maganar shi ta kuma tsinkaya ya na faɗin
"Haba Anee gani nan a hanyar dawowa, bani minti talatin."
Ya faɗa tare da kashe wayar. Juyo da fuska ya yi yana kallon Ameesha ya ce
"Kinji matata tana kirana wai na daɗe?"
Karamin tsaki ta ja ,ba ta ce masa komai ba, don gaba daya haushin shi da kishin sa suka rufe ta.
Shi ma shiru ya mata ya ci gaba da tukin sa, Ameesha tana nuna masa hanya har suka isa unguwar, a dai dai get din gidan ya faka, kallon sa ta yi ta ce
"Na gode Dr sai da safe."
Harara ya mata ya ce
"Kuma shi kenan iya sallamar da za mu yi?"
Dan ware ido ta yi cikin mamaki ta ce
"Dr wani irin sallama za mu yi wacce ta fi wannan?"
Har yanzu fuskarta ɗauke da mamaki.
Dan sosa keya ya yi ya ce " To ai naga har kin fita ne, ko fa Number din ki bani da?"
"Hmmmm! ta furta da da dai wannan yanayin mamaki ta ce "bani wayar ka nasa ma kafin Abba ya zo ya same ni."
Mik'a mata ya yi ta amsa cikin sauri sauri ta sanya masa, sannan ta nufi get din Asmad na kallonta har ta shige cikin gidan sannan ya saki ajiyar zuciya a fili ya furta
"Allah ka mallaka min Maryam matsayin mata amin." Ya kai karshen maganar yana ta yar da motarsa.
******** ********** *******
Ko da Ameesha ta shiga gidansu da ɗoki ta k'arasa falon, ganin motar Yaya Jaheed ta san shi ɗin ne ya zo, sallama ta doka tare da shiga, wani murmushi ta saki ganin sa zaune a falon da matarsa. Ai da sauri ta isa inda suke tana faɗin "barka da zuwa Yaya" murmushi ya saki cikin jin daɗi ya amsa mata maganar ta.
"A'a Ameesha autar Ummi sai yanzu aka shigo?"
Matar Ya Jaheed ne ta yi maganar. Matsawa kusa da ita ta yi ta ce
"Aunty ina yini?"
"Lafiya ya makarantar?"
"Alhamdulillah." Ameesha ta bata amsa tana nufa hanyar stair. Har ta soma taka matakalar ta tuna bata wa Ummi sannu da gida ba don haka sai ta sauka, bedroom din Ummi ta shiga bakin ta ɗauke da sallama.
Hajiya Halima da ke buɗe k'ofar toilet ta amsa mata cike da kulawa.
"Auta kin dawo?"
"Eh na dawo Ummi."
"To sannu da dawowa,je kiyi wanka abinci yana jiran ki."
"Ummi nifa a koshe na ke, wanka kawai zan yi."
"Ke abin da na ce kenan je ki yi, naga yanzu kwata kwata baki k'aunar cin abinci ko?"
Ummi ta k'arasa maganar tana hararan Ameesha.
Shagwaɓe fuska ta yi ta ce
"Allah Ummi ina ci fa, kawai yau na koshi ne."
"To je ki yi wankan."
"Yawwa Ummina." Ameesha ta faɗa tana fita daga bedroom din.
Bayan ta yi wanka ne ta koma falo inda su Ya Jaheed da matarsa suke, tana zama Meena ta shigo hira suka ci gaba da yi.
*******
"Alhaji wato kasan abin da yasa na nemeka a wannan rana?"
Alhaji Taheer ya yi maganar yana aje cup din da ya sha ruwa.
"Sai ka faɗa Alhaji."
Alhaji Mansur ya yi maganar cikin ɗan murmushi irin na ya ke.
"Dama kan maganar Najeeb ne da Ameesha, na ga soyayyar ta su kullum kara gaba ta ke , shi ne na ce gara asan matsaya."
Wani mummunan faduwar gaba ya ziyarci Alhaji Mansur ya ce "Na shiga uku ni Mansur, kenan burina ba zai cika ba? To wallahi ba zai yiwu ba dole sai na cika abin da na yi niyya, Taheer ba ka isa ba ba zai yiwu."
Amma a fili sai ya kakalo ya ke ya ce
"Yo Alhaji ban da abin ka ai kana iya zartar da hukuncin auren su gaba ɗaya, babu abin da zance sai fatan alheri."
Sosai Alhaji Taheer ya yi farin ciki da jin furucin Alhaji Mansur ɗin, don haka sai ya ce
"To zamu zauna nan da kwana kaɗan don asa rana."
"Allah ya kaimu."
Da wannan hirar suka ci gaba da hirar duniya, sun daɗe sosai ka ɗin su ka yi sallama ko wa ya kama hanyar gidan sa.
Lokacin da Meesha da Najeeb suka samu wannan labarin ba karamin daɗi su ka ji ba, babu kamar Meesha da ta ke murna zata huta da tunanin Dr ɗan fullo, tunda zata auri wanda ta ke so.
*******
"Um um Abba yau fa kai zaka kaini school." Meesha ta yi maganar tana zama kusa da Alhaji Taheer ɗin.
Murmushi ya saki tare da shafa kanta ya ce