Sashe 11
Sangarta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai kuma a suwa da zaka hana ni fita *Ji shiga uku takabar suruki*,To sai naje ɗin. Meesha ta faɗa tana fita daga dakin.
Nenne kam harara ta aika masa da shi ta ce
"Ina ruwan ko? Kana ganin yarinyar an samu da kyar Allah ya taimaka shi ne zaka ɓullo da wata maganar?
"Allah ya baku hakuri ne..."
Wai typing da wahala Yaseen.
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:16 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
Dedicated to _*RAHEENAT MAMOUDOU (HEENART)*_
```Betsy Allah ya baki lafiya, jin ciwon ki nake kamar a jikina yake 😭😭 sosai na yi missing ɗin ki, Allah yasa kaffara ne```👏
*36*
Nenne bata ce masa komai ba, sai ma zama da ta yi tana jiran zuwan Ameesha, bata fi minti biyar ba ta dawo da ganin yadda ta turo baki zaka san da magana, kusa da Nenne ta zauna cikin zallar SANGARTAR da ta saba.
" 'Yata lafiya kuwa?"
"Ba Abba bane wai inzo in tambayi Dr, idan ya bari sai mu tafi." Cike da shagwaɓa har da dira kafa kamar wata karamar yarinya ta ida maganar.
Wani irin murmushi Dr ya saki don tabbas ya ji dadin maganar Abba, ya kuma bashi wani matsayin na musamman, domin ya cika suruki na gaske.
Sosai ta cika da mamakin furucin Abba da ya ce sai da izinin Dr zata fita, to wani matsayi Dr ke da shi a wajenta da har Abba zai fadi wannan maganar?" Tambayar ta yiwa kanta wanda bata da amsar sa, ko kafin ta lalubo amsa sai jin maganar Nenne ta yi.
"To kai ka ji abin da ta ce ko?" Babu alamar dariya Nenne ta masa tambaya.
"Eh! Na ji Nenne a dawo lafiya, mu je nima ina son k'ara ganin garin."
Kusan a tare suka fito, domin su Meena ma yawon zaga garin zasu je, haka suka fita suna hira Ummi da Nenne suna taɓa hira, Meena da Meesha ma haka, sai su Jaheed da Dr, sun zaga gari sosai har sayayya suka yi, Dr ma ya sayawa Aneesa tsaraba domin ya faranta mata, washe gari jirjin karfe takwas suka bi.
*NIGERIA*
ko da jirgin su ya sauka kowa gidan sa ya nufa, Dr dai kin bin su Nenne ya yi domin cewa ya yi sai ya kai Ameesha har gida, Allah ya sani baya son rabuwa da ita don dai ya zama dole ne.
Yana cikin gidan sai wajen karfe shida ya fita, a lokacin tuni Aneesa ta shirya masa lafiyayyen girki, shi kadai take jira ganin har shida ta yi sai ranta ya soma ɓaci domin ta yi amanna yana tare da Ameesha shi yasa ya manta da ita.
Sallama ya yi tare da shiga cikin falon, Aneesa dake zaune ta watsa masa wani irin kallo tare da dauke kai
"My Anne mai nayi kuma daga dawowata?" Ya yi maganar tare da hugging ɗinta.
Bata fuska ta yi ta turo baki, tana mutsu-mutsu so take ta zame jikinta daga rikon da ya mata
"Sorry na yi laifi ko? Amma fa ba laifi na yi ba, kinsa tare da mara lafiya nake dole tana da buk'atar kulawa."
Kuka ta fashe masa da shi tana faɗin.
"Ai Ni bana buk'atar kulawa tunda har ka tafi kusan kwana goma." Da shashsheka take maganar.
Gyara rikonta ya yi ya ce
"Please ki yi hakuri bazan kuma ba, kin ji matata farin cikina?"
"Babu komai ya wuce."
"Da gaske?"
"Eh! Mu je ka yi wanka sai ka ci abinci."
"Yawwa matata yar albarka."
Aneesa ta taimaka masa ya yi wanka, jallabiya ya zira lokacin ana kiran sallar magriba, masallacin kofar gidan ya je lokacin da ya dawo bai taras da ita a falo ba, don haka sai ya nufi bedroom ɗinta, zaune ya ganta gaban dressing mirror tana fesa turare, shakar kamshin ya yi yana rungume ta jikinsa.
"My Anne kin yi kyau."
"Na gode." Ta faɗa fuskarta ɗauke da murmushi.
"Ranka ya daɗe mu je ka ci abinci."
"No! Barni in gama shakar kamshin matata."
"Please." Ta faɗa kamar zata yi kuka.
Sakinta ya yi ya riƙe hannunta, a haka suka isa dining room din. Da kanta take ciyar da shi har ya koshi, falo suka koma, ranar dai sosai Dr ya cika da mamakin canzawar Aneesa.
Washe gari tun wuri Dr ya shirya domin ziyartar asbiti, bai biya ko ina ba, domin baya son ya yi latti ya dai turawa Ameesha text message na barka da safiya, karfe takwas a asbiti ta yi masa da yake sun san ya dawo komai a gyare ya taras, aiki sosai Dr ya yi har bai samu kansa ba sai biyun rana.
****
"Sannu My Ruffy har yanzu amai ɗin bai tsaya ba?"
"Eh! Ta bashi amsa tana mai da numfashi, domin dai sosai ta galabaita, da kansa ya gyara wajen ya canza mata kaya, yana rike da ita har suka isa wajen motarsa, taimaka mata ya yi ta shiga, sannun da yake jero mata tunda ga bedroom ɗinta har nan sun kai hamsin.
Tsabar tausayin ta ke damunsa sosai, ba su yi wata tafiya mai nisa ba suka shiga wani karamin asbiti mai kyau, parking ya yi tare da riketa har cikin office din Dr, domin ya yi masa waya tun kafin su taho.
Dr Auyo sosai ya tausayawa Rufaida ganin halin da take ciki, tambayoyi ya fara mata tana bashi amsa, inda daga karshe ya kira Nurse tare da umurtanta da ta dibi jinin Rufaida da fitsarinta domin a yi test, ba'a wani dade ba ta dawo da result ɗin.
Gama karanta result ɗin ya yi fuskarsa ɗauke da murmushi, hannu ya mik'awa Najeeb yana faɗin
"Congratulations! Sir Allah ya inganta, Madam na dauke da juna biyu na sati biyar."
Wani irin farin ciki ne ya kama Najeeb, wanda har bai san lokacin da ya rungume Rufaida ba, ita kam kasa ta yi da kai cike da kunya, Najeeb fa ya manta a gaban Dr yake, da Dr Auyo da yaga haka sai ya fita ya bar masu office din.
Najeeb kuwa rungume Rufaida ya yi a jikinsa, yana gwada mata tsantsan farin ciki da murna na cikin dake jikinta, lokacin da ya ɗago bai ga Dr Auyo ba murmushi ya yi don yasan shi da kunya.
Mik'ewa ya yi ya leka waje inda ya ga Dr na magana da wasu, Nurse ya sanya ta yi masa magana, bai jima ba ya shigo, bakin Najeeb sam yaki rufuwa ya ce
"Dr da alama cikin zai bata wahala musamman ta yawan aman dake damunta, ko akwai maganin da za'a bata?"
"Eh! Akwai wani magani da mai ciki take amfani da shi sunan sa *Ancloxine tablet* sosai yake tsayar ma masu ciki amai matukar dai ya amshe ta, kasan laulayi ne kowa da irin yadda ya ke yi." Dr Auyo ya yi masa bayanin cikin kwantar da hankali.
"To Dr muna godiya sosai Allah ya bar zumunci."
"Amin." Dr ya amsa ya na mika masa takaddan da ya rubuta sunan maganin. Daga haka suka yi sallama, ko da suka fita ba su nufi gidan su ba sai kawai ya nufi gidan Mummy da ita.
A falo suka samu Mummy tana ganin Rufaida ta mik'e cikin sauri tare da kulawa tana kamo hannunta fadi take
'yata Barka da zuwa, kune a wannan lokacin?" Rufaida dai da kyar ta iya gaida Mummy sai wani sinne kai take ala dole tana kunya.
Shi kam uban tafiyar sai washe baki yake kamar gonar audiga
"Daga ina kuke?" Mummy ta tsinka shirun da falon ya yi na yan sakonni.
"Asbiti na kaita bata jin dadi."
"Ayya sannu'yata, ashe shi yasa na ganki a haka sannu Allah ya baki lafiya, mai yake damunta?" ta yi maganar tana kallon Najeeb.
Mika mata takaddan ya yi yana murmushi, "Alhamdulillah! Ta furta murya a bayyane, zuciyarta cike da farin ciki.
Sosai Mummy ta nuna farin cikinta, sai ririta Rufaida take sam bata son wani abu ya daga hankalinta, Najeeb dai gidan Mummy ya bar Rufaida da niyyar bayan magriba zai dawo ya dauketa.
****
Zaune suke cikin bedroom na Ameesha, Meena da Meesha ne suke hira, sannu a hankali har suka iso kan Dr, Meena sai fadan Alhairin sa da kirkinsa take yi.
Meesha tana sauraron.
Nannauyan ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗaura idonta a fuskar Meena ta ce
"Wai wa ya bama Dr Asmad damar shigowa gidan nan har cikin falo ne, ranar da zamu fita zaga gari a CAIRO wai Abba har da cewa in tambayi Dr na dade ina mamakin maganar fa?"
"Meesha kenan Dr ai yana da matsayin da kike da shi a gidan nan, ke kusan ya fiki ma."
Zaro ido ta yi jin maganar Meena ta ce
"Haba dai duka yaushe yasan nan gidan da har zai taka matsayin da nake ? Kema wallahi faɗa kawai kike yi."
"Allah da gaske Dr yana da matsayin da na sanar maki, wallahi da zaki san irin taimakon da ya yi wa rayuwar ki tabbas da sai kin ninka akan son da kike masa a da, Dr Asmad wani jigo ne a rayuwar ki."
"Hmmmm! Bana fahimtar bayanin ki fa, yi min dalla-dalla don nafi ganewa."
"Zan yi maki bayani amma ba yanzu ba." Meena tana gama fadin haka ta mik'e tare da fita daga bedroom din.
Cikin zallar jin dadi ya dauki hanyar gidan su Ameesha burinsa kawai ya ganta ko hankalinsa zai kwanta, lokacin da ya isa kofar gidan hon ya yiwa maigadin gidan da sauri ya wangale masa get, ciki ya cusa hancin motar a parking space ya yi parking, wayarsa ya kwasa sannan ya fita daga motar cikin kwanciyar hankali yake takusa mai firgita yan mata, hannunsa na juya keys din motarsa, kamar an ce ya dubi gefen haggunsa sai ko idon sa ya sauka kanta, cike da mamaki ya kara bude ido yana kallonta tabbas ita din ce, tsaye da wani mutum idan har ba gizo idonsa ke masa har murmushi ya hango kwance a kan kyakkyawar fuskanta.
Nenne kam harara ta aika masa da shi ta ce
"Ina ruwan ko? Kana ganin yarinyar an samu da kyar Allah ya taimaka shi ne zaka ɓullo da wata maganar?
"Allah ya baku hakuri ne..."
Wai typing da wahala Yaseen.
_*YAR MUTAN RANO*_
[10/8, 8:16 PM] Zulayheart Rano: *SANGARTA*
©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*
*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*
Dedicated to _*RAHEENAT MAMOUDOU (HEENART)*_
```Betsy Allah ya baki lafiya, jin ciwon ki nake kamar a jikina yake 😭😭 sosai na yi missing ɗin ki, Allah yasa kaffara ne```👏
*36*
Nenne bata ce masa komai ba, sai ma zama da ta yi tana jiran zuwan Ameesha, bata fi minti biyar ba ta dawo da ganin yadda ta turo baki zaka san da magana, kusa da Nenne ta zauna cikin zallar SANGARTAR da ta saba.
" 'Yata lafiya kuwa?"
"Ba Abba bane wai inzo in tambayi Dr, idan ya bari sai mu tafi." Cike da shagwaɓa har da dira kafa kamar wata karamar yarinya ta ida maganar.
Wani irin murmushi Dr ya saki don tabbas ya ji dadin maganar Abba, ya kuma bashi wani matsayin na musamman, domin ya cika suruki na gaske.
Sosai ta cika da mamakin furucin Abba da ya ce sai da izinin Dr zata fita, to wani matsayi Dr ke da shi a wajenta da har Abba zai fadi wannan maganar?" Tambayar ta yiwa kanta wanda bata da amsar sa, ko kafin ta lalubo amsa sai jin maganar Nenne ta yi.
"To kai ka ji abin da ta ce ko?" Babu alamar dariya Nenne ta masa tambaya.
"Eh! Na ji Nenne a dawo lafiya, mu je nima ina son k'ara ganin garin."
Kusan a tare suka fito, domin su Meena ma yawon zaga garin zasu je, haka suka fita suna hira Ummi da Nenne suna taɓa hira, Meena da Meesha ma haka, sai su Jaheed da Dr, sun zaga gari sosai har sayayya suka yi, Dr ma ya sayawa Aneesa tsaraba domin ya faranta mata, washe gari jirjin karfe takwas suka bi.
*NIGERIA*
ko da jirgin su ya sauka kowa gidan sa ya nufa, Dr dai kin bin su Nenne ya yi domin cewa ya yi sai ya kai Ameesha har gida, Allah ya sani baya son rabuwa da ita don dai ya zama dole ne.
Yana cikin gidan sai wajen karfe shida ya fita, a lokacin tuni Aneesa ta shirya masa lafiyayyen girki, shi kadai take jira ganin har shida ta yi sai ranta ya soma ɓaci domin ta yi amanna yana tare da Ameesha shi yasa ya manta da ita.
Sallama ya yi tare da shiga cikin falon, Aneesa dake zaune ta watsa masa wani irin kallo tare da dauke kai
"My Anne mai nayi kuma daga dawowata?" Ya yi maganar tare da hugging ɗinta.
Bata fuska ta yi ta turo baki, tana mutsu-mutsu so take ta zame jikinta daga rikon da ya mata
"Sorry na yi laifi ko? Amma fa ba laifi na yi ba, kinsa tare da mara lafiya nake dole tana da buk'atar kulawa."
Kuka ta fashe masa da shi tana faɗin.
"Ai Ni bana buk'atar kulawa tunda har ka tafi kusan kwana goma." Da shashsheka take maganar.
Gyara rikonta ya yi ya ce
"Please ki yi hakuri bazan kuma ba, kin ji matata farin cikina?"
"Babu komai ya wuce."
"Da gaske?"
"Eh! Mu je ka yi wanka sai ka ci abinci."
"Yawwa matata yar albarka."
Aneesa ta taimaka masa ya yi wanka, jallabiya ya zira lokacin ana kiran sallar magriba, masallacin kofar gidan ya je lokacin da ya dawo bai taras da ita a falo ba, don haka sai ya nufi bedroom ɗinta, zaune ya ganta gaban dressing mirror tana fesa turare, shakar kamshin ya yi yana rungume ta jikinsa.
"My Anne kin yi kyau."
"Na gode." Ta faɗa fuskarta ɗauke da murmushi.
"Ranka ya daɗe mu je ka ci abinci."
"No! Barni in gama shakar kamshin matata."
"Please." Ta faɗa kamar zata yi kuka.
Sakinta ya yi ya riƙe hannunta, a haka suka isa dining room din. Da kanta take ciyar da shi har ya koshi, falo suka koma, ranar dai sosai Dr ya cika da mamakin canzawar Aneesa.
Washe gari tun wuri Dr ya shirya domin ziyartar asbiti, bai biya ko ina ba, domin baya son ya yi latti ya dai turawa Ameesha text message na barka da safiya, karfe takwas a asbiti ta yi masa da yake sun san ya dawo komai a gyare ya taras, aiki sosai Dr ya yi har bai samu kansa ba sai biyun rana.
****
"Sannu My Ruffy har yanzu amai ɗin bai tsaya ba?"
"Eh! Ta bashi amsa tana mai da numfashi, domin dai sosai ta galabaita, da kansa ya gyara wajen ya canza mata kaya, yana rike da ita har suka isa wajen motarsa, taimaka mata ya yi ta shiga, sannun da yake jero mata tunda ga bedroom ɗinta har nan sun kai hamsin.
Tsabar tausayin ta ke damunsa sosai, ba su yi wata tafiya mai nisa ba suka shiga wani karamin asbiti mai kyau, parking ya yi tare da riketa har cikin office din Dr, domin ya yi masa waya tun kafin su taho.
Dr Auyo sosai ya tausayawa Rufaida ganin halin da take ciki, tambayoyi ya fara mata tana bashi amsa, inda daga karshe ya kira Nurse tare da umurtanta da ta dibi jinin Rufaida da fitsarinta domin a yi test, ba'a wani dade ba ta dawo da result ɗin.
Gama karanta result ɗin ya yi fuskarsa ɗauke da murmushi, hannu ya mik'awa Najeeb yana faɗin
"Congratulations! Sir Allah ya inganta, Madam na dauke da juna biyu na sati biyar."
Wani irin farin ciki ne ya kama Najeeb, wanda har bai san lokacin da ya rungume Rufaida ba, ita kam kasa ta yi da kai cike da kunya, Najeeb fa ya manta a gaban Dr yake, da Dr Auyo da yaga haka sai ya fita ya bar masu office din.
Najeeb kuwa rungume Rufaida ya yi a jikinsa, yana gwada mata tsantsan farin ciki da murna na cikin dake jikinta, lokacin da ya ɗago bai ga Dr Auyo ba murmushi ya yi don yasan shi da kunya.
Mik'ewa ya yi ya leka waje inda ya ga Dr na magana da wasu, Nurse ya sanya ta yi masa magana, bai jima ba ya shigo, bakin Najeeb sam yaki rufuwa ya ce
"Dr da alama cikin zai bata wahala musamman ta yawan aman dake damunta, ko akwai maganin da za'a bata?"
"Eh! Akwai wani magani da mai ciki take amfani da shi sunan sa *Ancloxine tablet* sosai yake tsayar ma masu ciki amai matukar dai ya amshe ta, kasan laulayi ne kowa da irin yadda ya ke yi." Dr Auyo ya yi masa bayanin cikin kwantar da hankali.
"To Dr muna godiya sosai Allah ya bar zumunci."
"Amin." Dr ya amsa ya na mika masa takaddan da ya rubuta sunan maganin. Daga haka suka yi sallama, ko da suka fita ba su nufi gidan su ba sai kawai ya nufi gidan Mummy da ita.
A falo suka samu Mummy tana ganin Rufaida ta mik'e cikin sauri tare da kulawa tana kamo hannunta fadi take
'yata Barka da zuwa, kune a wannan lokacin?" Rufaida dai da kyar ta iya gaida Mummy sai wani sinne kai take ala dole tana kunya.
Shi kam uban tafiyar sai washe baki yake kamar gonar audiga
"Daga ina kuke?" Mummy ta tsinka shirun da falon ya yi na yan sakonni.
"Asbiti na kaita bata jin dadi."
"Ayya sannu'yata, ashe shi yasa na ganki a haka sannu Allah ya baki lafiya, mai yake damunta?" ta yi maganar tana kallon Najeeb.
Mika mata takaddan ya yi yana murmushi, "Alhamdulillah! Ta furta murya a bayyane, zuciyarta cike da farin ciki.
Sosai Mummy ta nuna farin cikinta, sai ririta Rufaida take sam bata son wani abu ya daga hankalinta, Najeeb dai gidan Mummy ya bar Rufaida da niyyar bayan magriba zai dawo ya dauketa.
****
Zaune suke cikin bedroom na Ameesha, Meena da Meesha ne suke hira, sannu a hankali har suka iso kan Dr, Meena sai fadan Alhairin sa da kirkinsa take yi.
Meesha tana sauraron.
Nannauyan ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗaura idonta a fuskar Meena ta ce
"Wai wa ya bama Dr Asmad damar shigowa gidan nan har cikin falo ne, ranar da zamu fita zaga gari a CAIRO wai Abba har da cewa in tambayi Dr na dade ina mamakin maganar fa?"
"Meesha kenan Dr ai yana da matsayin da kike da shi a gidan nan, ke kusan ya fiki ma."
Zaro ido ta yi jin maganar Meena ta ce
"Haba dai duka yaushe yasan nan gidan da har zai taka matsayin da nake ? Kema wallahi faɗa kawai kike yi."
"Allah da gaske Dr yana da matsayin da na sanar maki, wallahi da zaki san irin taimakon da ya yi wa rayuwar ki tabbas da sai kin ninka akan son da kike masa a da, Dr Asmad wani jigo ne a rayuwar ki."
"Hmmmm! Bana fahimtar bayanin ki fa, yi min dalla-dalla don nafi ganewa."
"Zan yi maki bayani amma ba yanzu ba." Meena tana gama fadin haka ta mik'e tare da fita daga bedroom din.
Cikin zallar jin dadi ya dauki hanyar gidan su Ameesha burinsa kawai ya ganta ko hankalinsa zai kwanta, lokacin da ya isa kofar gidan hon ya yiwa maigadin gidan da sauri ya wangale masa get, ciki ya cusa hancin motar a parking space ya yi parking, wayarsa ya kwasa sannan ya fita daga motar cikin kwanciyar hankali yake takusa mai firgita yan mata, hannunsa na juya keys din motarsa, kamar an ce ya dubi gefen haggunsa sai ko idon sa ya sauka kanta, cike da mamaki ya kara bude ido yana kallonta tabbas ita din ce, tsaye da wani mutum idan har ba gizo idonsa ke masa har murmushi ya hango kwance a kan kyakkyawar fuskanta.