Sashe 9
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babbar motar Baban ce da ake amfani da ita idan za'a je kauye ko wani waje tare, driver ne yake tukata sai Baban a gefen sa, kujerar baya jidda da amira suka zauna Anty kuma ta zauna a ta tsakiya ita da Muhammad da Usman, maryam kamar zatayi kuka da ta rakosu dan dai kawai bata son fushin Mama ne amma da itama sai taje, ita da Safiyya kawai suka rage a gidan dan Mama ta sake fita da Ya Fauwaz da Umaima tun dazu kuma kila sai yamma likis zasu dawo.
Hanya suka dauka sosai bayan an tsaya an yi siyayyar abubuwan da zasu tafi dashi. Tafiya sukayi a hankali har suka isa, hakan ya kara zumudin jidda ganin an dauku hanyar gidan, ta zura hannunta ta window tana feeling sanyayyiyar iskar dake kadawa. Parking Baba Driver yayi a kofar gidan dan ba wannan ne karon farko na zuwan sa da Baba ba. Baffa na jin tsayuwar mota ya fito da sauri suka yi kicibis a waje. Fuskar sa tamkar gonar auduga, idanun sa suka hango masa Jiddan sa, wadda ta sauya masa tayi haske ta dan yi kiba kadan, wajen Baba ya nufa kai tsaye duk da dokin ganin Jiddan, suka shiga gaisawa da tambayar bayan saduwa,cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, akayi sa'a Lami bata nan tayi tafiya zata kuma kwana biyu, gidan a share yake tas tas, sai katuwar tabarmar da Baffa ya shinfida a tsakar gidan, suka zauna dukkan su aka shiga gaishe gaishe. Duk da zumudi da son ganin baffan nata amma sai ta makale a gefe cike da kunya, takasa cewa komai. Dariya duk ta basu Baba ya tsokane ta akayi dariya kafin ta gaida Baffan ya amsa sannan Amira ma ta gaishe shi.
Wajen awa biyu Baba sukayi, suka sha fura da nono sannan suka ci dambu da Innar su Saude ta aiko musu, sannan suka shirya komawa shi da Baba driver, Kwan zabi Baffa ya basu masu yawa ya rakasu har mota Baba ya dauko kudi ya bawa Baffan ya karba da kyar yayi godiya. Ya bude masa kofar ya shiga ya sauke glass din yace
"Yaya zan shiga siyasa in sha Allah, a tayamu da addua."
"Kai Masha Allah, Alhaji ai dama irin ku ake so a siyasar kasar nan,ka chanchanta"
"Kayya, zamu dai gwada jarrabawa mu gani."
"Toh Allah ya taimaka ya bada sa'a."
"Amin."
Suka sake sallama suka tafi Shi kuma ya koma cikin gidan, ya samu Anty a zaune suka shiga hirar yaushe gamo, ya dinga yi mata godiya akan jidda sannan ya bata labarin zuwan da Baba yayi aka kaishi wajen likatan kashi tun daga lokacin ya samu saukin kafar dan har gona zuwa yake. Ita bata ma san anyi ba,dan be fada ba, kuma dama tasan ba fada din zai yi ba, haka yake ko yayi abu baya so a yaba masa yafi son kawai a yi shiru.
***Kwanan su biyu sosai Amira taji dadin garin, yanayin weather din yayi mata ga fura da nono abinda take matukar so kenan, gobe zasu tafi shima da kyar Baba ya kara musu kwana daya,dan be samu me zuwa dauko su bane ba ma shiyasa, kanya suke je tare da Saude suka samo suka zauna a tsakar gidan su Sauden suna sha tana basu labarin abun dariya, tashi Jidda tayi ta ce zata dauko abu a gida ta dawo. Gidan su ta shiga ta tarar da Anty zata fita hankalin ta a tashe, da sauri tace mata.
"Jidda Muhammad yana wajen ku ne?"
Da sauri ta girgiza kanta
"A ah, tare muka bar su da Usman suna zaune."
"Na shiga uku!"
Tace tana yin gaba, da sauri jidda tabi bayan ta, suka hau neman sa, abu kamar wasa sai gashi an neme sa an rasa, iya kar tashin hankali Anty ta shiga. Sauran makota ne suka fito aka bazama nema, Usman dai yace yabi su Yaya Amira da Yaya jidda da suka fita, lokacin Anty tana sallah, su kuma sun ce be biyo su ba, kuka wiwi Anty take tana jin kamr ta hadiyi zuciya ta mutu, wannan wanne irin tashin hankali ne, ina ya shiga? Me zai faru? Yaya Mama zata ji idan wani abu ya same shi bayan da kyar ta yarda suka biyo ta, zata taba fita idan wani abu ya same shi? Ba zata fita ba ko a wajen mutane balle mahaifiyar sa. Har duhun magriba ya soma babu shi babu labarin sa, dukkan su kuka suke har Jidda da Amira da ta cika da tsoron abinnda zai faru da Muhammad din.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/25, 3:54 PM] Rano2: *__SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (8)
****Kasancewar karamin gari ya saka suke da yakinin ba zai bata a cikin sa ba, sai dai tabbas ana kyautata zaton ba lafiya ba, daga chan gaban gidan su Jiddan akwai wata babbar rijiya, da duk mazauna wajen suke amfani da ita. Kamar an tsikari Aunty haka ta mike da sauri duk suma suke mike
"A duba rijiyar nan, Allah ubangiji yasa ba fadawa yayi ba."
Ta fashe da kuka, jikinta na rawa sosai tamkar mazari, Baffa ne da Baffan su Saude da wasu maza biyu suka nufi rijiyar dan duk ciki babu wanda ya yi tunanin dubawar.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!"
Kalmar da aunty ta iya ji kenan daga bakin Baffa sanda ya leka kansa cikin rijiyar, saboda tsabar kaduwa ta yanke jiki ta fadi cikin wani irin yanayi. Nan da nan wajen ya cika makil da mutane aka samo masu shiga rijiya mutum hudu biyu suka shiga suka dauko shi, cikin yanayin firgici.
***Wani irin kuka aunty take, duk rashin imanin ka sai ka tausaya mata, Jidda da Amira ma sun ci kuka sun gode Allah, suna nannade a zaune gefen Aunty Usman na jikin Amira yana kuka shima duk da kukan be san na menene ba, waya Baffa ya dauka ya kira Baba, ya koma gefe ya sanar dashi abinda yake faruwa cikin yanayin dauriya dan sai da yayi da gaske sannan ya iya kiran Baban shima saboda kiran ya zama dole ne.
"Kullu nafsin za'ikatul maut Yaya, ko da Muhammad a gaban mu yake ni da mahaifiyar sa dole sai ya mutu, bani da jahilci dan ni musulmi ne kuma na yarda da kaddara, Allah ya sa me ceton mu ne, kayi mishi dukkan abinda ya kamata a kaishi gidan gaskiya."
Jiki a sanyaye Baffa ya dawo ciki, akayi duk abinda za'a yi, a daren aka kaishi.
****Sanda Baffa ya kira Baba yana daf da shiga gida, sosai mutuwar ta dake shi duka me zafin gaske, kansa a kasa kirjinsa na masa wani iri, juriya da jarumta irin ta namiji a haka suka karasa gidan, yana tunanin yadda zai sanar da Mama.
Dakin ta ya wuce kai tsaye wanda ya dade rabon shi da shiga har cikin dakin nata, tana zaune tana lissafi gabanta tray ne na abinci tana so ta kammala taci duk da tana jin kamar an dauke appetite din bakin ta ne, wani irin yanayi take jin zuciya da gangar jikin ta tamkar zatayi zazzabi, daurewa kawai take tana karfafa jikinta dan bata so ta bar aikin da take bata kammala ba. Sauri take taga ta gama dukka dan tana son kiran Tariq taji ko lafiya yake? Dan sai take jin kamar ba lafiya ba, ajiye takarda da biron hannun ta, tayi ta jawo wayarta dake saman gado ta hau dialing number sa.
Yana zaune a gajiya yake tikis bayan ya dawo daga motsa jikin sa, so yake ya watsa ruwa kafin ya duba wasu papers da zai, amma kuma ya gaza tashi yana kishingid'e kansa na dan sara masa wanda ya san stress ne na karatu da baya ko hutawa dan a sati weekends ne kawai yake samu ya huta kamar na awa hudu amma sauran ranakun sam bashi da hutu. Wayar sa dake yashe a saman dan madaidacin table dake cike da manyan text books dinsa ce tayi kara, duk da baya expecting Kira daga kowa amma sai ya mike yana dora idon sa akan table din har ya karasa ya dauki wayar ganin sunan Mama ya sakashi dagawa ya zaune a kujerar dake gaban table din yace
"Hello..."
"Hello Assalamu alaikum."
"Wa alaikisalam." Ya amsa yana dan motsa kafarsa kafin ya gaishe ta, ta amsa sannan ta dora
"Lafiya kake ko?"
"Me faru mah? Lafiya ta kalou."
"Naji muryar ka haka-haka, hope dai babu wata matsala."
"No, stress ne kawai, da na dan samu na watsa ruwa zan warware ."
"Ok!" Tace a gajarce, shigowar Baba dakin ya sakata rike maganar da zatayi, ta zuba masa ido tana karantar yanayin da ya shigo mata, zama yayi a gefen ta, sai taga kamar idanun sa sun kada
"Rike wayar Tariq."
Tace tana zare ta daga kunnenta, tashi yayi shima bayan ya cire wayar daga kunnen sa ya nufi wajen kayan sa, ya shiga cire kayan jikinsa.
"Me ya faru?" Tace tana kallon sa
"Aisha!" Sai gabanta ya ce ras jin ya ambace ta da sunan ta kai tsaye, kamar wadda aka zare wa laka haka taji, ta saddakar babu lafiya amma kuma ta gaza hasaso komai akai
Hanya suka dauka sosai bayan an tsaya an yi siyayyar abubuwan da zasu tafi dashi. Tafiya sukayi a hankali har suka isa, hakan ya kara zumudin jidda ganin an dauku hanyar gidan, ta zura hannunta ta window tana feeling sanyayyiyar iskar dake kadawa. Parking Baba Driver yayi a kofar gidan dan ba wannan ne karon farko na zuwan sa da Baba ba. Baffa na jin tsayuwar mota ya fito da sauri suka yi kicibis a waje. Fuskar sa tamkar gonar auduga, idanun sa suka hango masa Jiddan sa, wadda ta sauya masa tayi haske ta dan yi kiba kadan, wajen Baba ya nufa kai tsaye duk da dokin ganin Jiddan, suka shiga gaisawa da tambayar bayan saduwa,cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, akayi sa'a Lami bata nan tayi tafiya zata kuma kwana biyu, gidan a share yake tas tas, sai katuwar tabarmar da Baffa ya shinfida a tsakar gidan, suka zauna dukkan su aka shiga gaishe gaishe. Duk da zumudi da son ganin baffan nata amma sai ta makale a gefe cike da kunya, takasa cewa komai. Dariya duk ta basu Baba ya tsokane ta akayi dariya kafin ta gaida Baffan ya amsa sannan Amira ma ta gaishe shi.
Wajen awa biyu Baba sukayi, suka sha fura da nono sannan suka ci dambu da Innar su Saude ta aiko musu, sannan suka shirya komawa shi da Baba driver, Kwan zabi Baffa ya basu masu yawa ya rakasu har mota Baba ya dauko kudi ya bawa Baffan ya karba da kyar yayi godiya. Ya bude masa kofar ya shiga ya sauke glass din yace
"Yaya zan shiga siyasa in sha Allah, a tayamu da addua."
"Kai Masha Allah, Alhaji ai dama irin ku ake so a siyasar kasar nan,ka chanchanta"
"Kayya, zamu dai gwada jarrabawa mu gani."
"Toh Allah ya taimaka ya bada sa'a."
"Amin."
Suka sake sallama suka tafi Shi kuma ya koma cikin gidan, ya samu Anty a zaune suka shiga hirar yaushe gamo, ya dinga yi mata godiya akan jidda sannan ya bata labarin zuwan da Baba yayi aka kaishi wajen likatan kashi tun daga lokacin ya samu saukin kafar dan har gona zuwa yake. Ita bata ma san anyi ba,dan be fada ba, kuma dama tasan ba fada din zai yi ba, haka yake ko yayi abu baya so a yaba masa yafi son kawai a yi shiru.
***Kwanan su biyu sosai Amira taji dadin garin, yanayin weather din yayi mata ga fura da nono abinda take matukar so kenan, gobe zasu tafi shima da kyar Baba ya kara musu kwana daya,dan be samu me zuwa dauko su bane ba ma shiyasa, kanya suke je tare da Saude suka samo suka zauna a tsakar gidan su Sauden suna sha tana basu labarin abun dariya, tashi Jidda tayi ta ce zata dauko abu a gida ta dawo. Gidan su ta shiga ta tarar da Anty zata fita hankalin ta a tashe, da sauri tace mata.
"Jidda Muhammad yana wajen ku ne?"
Da sauri ta girgiza kanta
"A ah, tare muka bar su da Usman suna zaune."
"Na shiga uku!"
Tace tana yin gaba, da sauri jidda tabi bayan ta, suka hau neman sa, abu kamar wasa sai gashi an neme sa an rasa, iya kar tashin hankali Anty ta shiga. Sauran makota ne suka fito aka bazama nema, Usman dai yace yabi su Yaya Amira da Yaya jidda da suka fita, lokacin Anty tana sallah, su kuma sun ce be biyo su ba, kuka wiwi Anty take tana jin kamr ta hadiyi zuciya ta mutu, wannan wanne irin tashin hankali ne, ina ya shiga? Me zai faru? Yaya Mama zata ji idan wani abu ya same shi bayan da kyar ta yarda suka biyo ta, zata taba fita idan wani abu ya same shi? Ba zata fita ba ko a wajen mutane balle mahaifiyar sa. Har duhun magriba ya soma babu shi babu labarin sa, dukkan su kuka suke har Jidda da Amira da ta cika da tsoron abinnda zai faru da Muhammad din.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/25, 3:54 PM] Rano2: *__SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (8)
****Kasancewar karamin gari ya saka suke da yakinin ba zai bata a cikin sa ba, sai dai tabbas ana kyautata zaton ba lafiya ba, daga chan gaban gidan su Jiddan akwai wata babbar rijiya, da duk mazauna wajen suke amfani da ita. Kamar an tsikari Aunty haka ta mike da sauri duk suma suke mike
"A duba rijiyar nan, Allah ubangiji yasa ba fadawa yayi ba."
Ta fashe da kuka, jikinta na rawa sosai tamkar mazari, Baffa ne da Baffan su Saude da wasu maza biyu suka nufi rijiyar dan duk ciki babu wanda ya yi tunanin dubawar.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!"
Kalmar da aunty ta iya ji kenan daga bakin Baffa sanda ya leka kansa cikin rijiyar, saboda tsabar kaduwa ta yanke jiki ta fadi cikin wani irin yanayi. Nan da nan wajen ya cika makil da mutane aka samo masu shiga rijiya mutum hudu biyu suka shiga suka dauko shi, cikin yanayin firgici.
***Wani irin kuka aunty take, duk rashin imanin ka sai ka tausaya mata, Jidda da Amira ma sun ci kuka sun gode Allah, suna nannade a zaune gefen Aunty Usman na jikin Amira yana kuka shima duk da kukan be san na menene ba, waya Baffa ya dauka ya kira Baba, ya koma gefe ya sanar dashi abinda yake faruwa cikin yanayin dauriya dan sai da yayi da gaske sannan ya iya kiran Baban shima saboda kiran ya zama dole ne.
"Kullu nafsin za'ikatul maut Yaya, ko da Muhammad a gaban mu yake ni da mahaifiyar sa dole sai ya mutu, bani da jahilci dan ni musulmi ne kuma na yarda da kaddara, Allah ya sa me ceton mu ne, kayi mishi dukkan abinda ya kamata a kaishi gidan gaskiya."
Jiki a sanyaye Baffa ya dawo ciki, akayi duk abinda za'a yi, a daren aka kaishi.
****Sanda Baffa ya kira Baba yana daf da shiga gida, sosai mutuwar ta dake shi duka me zafin gaske, kansa a kasa kirjinsa na masa wani iri, juriya da jarumta irin ta namiji a haka suka karasa gidan, yana tunanin yadda zai sanar da Mama.
Dakin ta ya wuce kai tsaye wanda ya dade rabon shi da shiga har cikin dakin nata, tana zaune tana lissafi gabanta tray ne na abinci tana so ta kammala taci duk da tana jin kamar an dauke appetite din bakin ta ne, wani irin yanayi take jin zuciya da gangar jikin ta tamkar zatayi zazzabi, daurewa kawai take tana karfafa jikinta dan bata so ta bar aikin da take bata kammala ba. Sauri take taga ta gama dukka dan tana son kiran Tariq taji ko lafiya yake? Dan sai take jin kamar ba lafiya ba, ajiye takarda da biron hannun ta, tayi ta jawo wayarta dake saman gado ta hau dialing number sa.
Yana zaune a gajiya yake tikis bayan ya dawo daga motsa jikin sa, so yake ya watsa ruwa kafin ya duba wasu papers da zai, amma kuma ya gaza tashi yana kishingid'e kansa na dan sara masa wanda ya san stress ne na karatu da baya ko hutawa dan a sati weekends ne kawai yake samu ya huta kamar na awa hudu amma sauran ranakun sam bashi da hutu. Wayar sa dake yashe a saman dan madaidacin table dake cike da manyan text books dinsa ce tayi kara, duk da baya expecting Kira daga kowa amma sai ya mike yana dora idon sa akan table din har ya karasa ya dauki wayar ganin sunan Mama ya sakashi dagawa ya zaune a kujerar dake gaban table din yace
"Hello..."
"Hello Assalamu alaikum."
"Wa alaikisalam." Ya amsa yana dan motsa kafarsa kafin ya gaishe ta, ta amsa sannan ta dora
"Lafiya kake ko?"
"Me faru mah? Lafiya ta kalou."
"Naji muryar ka haka-haka, hope dai babu wata matsala."
"No, stress ne kawai, da na dan samu na watsa ruwa zan warware ."
"Ok!" Tace a gajarce, shigowar Baba dakin ya sakata rike maganar da zatayi, ta zuba masa ido tana karantar yanayin da ya shigo mata, zama yayi a gefen ta, sai taga kamar idanun sa sun kada
"Rike wayar Tariq."
Tace tana zare ta daga kunnenta, tashi yayi shima bayan ya cire wayar daga kunnen sa ya nufi wajen kayan sa, ya shiga cire kayan jikinsa.
"Me ya faru?" Tace tana kallon sa
"Aisha!" Sai gabanta ya ce ras jin ya ambace ta da sunan ta kai tsaye, kamar wadda aka zare wa laka haka taji, ta saddakar babu lafiya amma kuma ta gaza hasaso komai akai