← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 76

Sashe 72

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

***Wajen cin abinci suka wuce sukayi order Chicken Mandi Rice da salad suka wuce gida. Shi kadai yaci dan ita cikin ta a cike yake daga gidan su Safeera. Bayan sallar magriba suka bar gida zuwa airport duk da sai da suka biya wani waje ya karbi sako. Suna shiga Abuja direct gidan su suka wuce dan sai after 10 suka shigo garin ma saboda delay din da aka samu kafin jirgin ya tashi.

#Ranooooo

***❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO KISHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*

              Page (58)

***Tun da suka dawo Tariq ya daina zama saboda shirye-shiryen tafiya dan a cikin satin zasu tafi saura be fi kwana uku ba, gashi da shirin tafiyar sa shi kadai yayi da intention din idan yaje zai zo da wuri amma yanzu yasan idan suka shilla suka tafi shikenan kuma sai dai idan haihuwa Jiddan zatayi su zo gida duk da be riga yasan yanayin commitment din da zai shiga achan din ba amma yasan aikin su yana cin time sosai.
Maryam da Amira sun zo gidan sau biyu suna wuni duk sanda suka zo tare da sakon gaisuwar Mama suke zuwa duk da jin su kawai take amma kuma hakan na mata dadi matuka, bata san halin da ake ciki tsakanin Baba da Maman ba dan yayi fushi sosai akan Maman shine take neman hanyar da zata samu ya sakko kuma a kasan ranta tana jin nutsuwa idan ta tuna Jiddan ce matar Tariq dinta ba irin Salma ba. Akan case dinta dasu Anty Nafin sai da taje Kano tayi mata tatas hakan ya jawo suka dauke kafa ma daga zuwa gidan Hajiya Babban gaba daya dan sosai Anty Nafin ta kullaci abinda Maman tayi mata.
Ana gobe zasu tafi Anty tazo ita da Usman, kamar Jidda ta zuba ruwa a k'asa tasha saboda murnar ganin Antyn. Dama lokacin tana karasa hada kayan ta waje daya ne sai ga Antyn aikuwa ta tayata suka karasa tare suna aikin tana shigar da sakon da take son nunawa Jiddan cikin hikima da yadda zata kula da mijin ta, ta sake samun fada a wajen sa. Jiddan naji duk tana daukewa dan dama Antyn ce mirror dinta ita take dubawa a abubuwa da yawa saboda tasan babu abinda ya zaunar da Antyn a gidan har ta kawo yanzu sai hakuri da iya zama amma ba dan haka ba da tuni ba wannan labarin ake ba.
Ya Tariq ne ya kirata bayan yaji komai lafiya sai take fada masa Antyn tazo shineyace kawai ta bita su tafi tare idan ta tashi tafiya saboda su yiwa Baba, Yaya da Mama sallama dan fitar asubah zasuyi gobe daga nan shima idan ya gama gidan zai wuce sai su dawo tare. Toh tace ta ajiye wayar ta fadawa Antyn abinda yace.

"Hakan yayi." Tace.

"Tunda tare zamu tafi ai sai mu hau shiri, komai ya riga ya shiga jaka sannan wadannan abubuwan da na nuna miki su karki wasa dasu wallahi."

"In sha Allah ba zan ba Anty."

"Yawwa, Allah dai ya kaiku lafiya, idan mun koma kika je part din Maman Fauwaz ki zauna sosai kinji? Karki ce zaki taso daga zuwa."

"Sau biyu da su amira suka zo sai suce wai Mama tana gaishe ni."

"Kai haba? Da gaske ko wasa?"

"Allah haka suka ce, na karshen ma Amira tace wai Mama tace mu fadi me muke bukata na tafiyar, shine sai yace tace mata zai zo gidan dan dama yana nan."

"Toh Allah yasa addu'ar mu ce taci ta, hakan ai kinga yafi, a kalla zamu fi samun kwanciyar hankali, kuma kinsan Allah? Maman Fauwaz bata da damuwa ita dai barta da kishi da duk mace kuma tana dashi sai dai kowa da irin yadda yake bayyana nasa, amma ko bayan wannan ba ruwanta da rayuwar ka, ko a sanda nake mata aiki bata da irin takurar nan magana ma bata cika son yi ba shiyasa ake mata kallon mara kirki, amma kishi ne kawai ya sakata yin duk abinda take amma sam babu cutarwa."

"Haka ne gaskiya."

"Allah ya kyauta yasa sakkowar tata kenan tunda dai yanzu ta zame miki dole tunda kika auri dan ta, ba'a kuma san karshen zaman da kuma yayan da za'a haifa ba."

"Ni ba zan haihu ba Anty."

"Saboda me?" Tace da sauri

"Tsoro nake ji fa."

"Kin jiki, ai sakin jiki zakiyi ki haifo mana babies Masha Allah, yadda bamu da yawan nan kinga ai ma kara yawa a daina mana gori."

"Kai Anty."

"Allah gori mana,ni da Yaya duk haihuwar daya ce kuma dama kinga mu biyu ne, dangi da yawa na da dadi wallahi sai baka dasu zaka gane, kuma dai haihuwar ce ke sawa a yi yawan."

"Tou haka ne."

"Tashi kinga kar lokaci ya kara ja mu tafi."

"Toh."

Ta mike taje ta dauko Hijab dinta ta saka suka fito, Sam na zaune suna ta hira da su Faisal sai ya taso da yaga sun fito yazo suka tafi.
Bata shiga wajen Antyn ba direct wajen Yaya ta wuce daga nan sai ta je ta gaida maman ta zauna kamar yadda Anty tace.
Dambu nama Yaya take ci da lemo Jiddan ta shigo, ta zata Fauwaz ne har da saurin ta zata boye Jiddan ta ganta.

"Auw ashe ba al'murin chan bane nake saurin boyewa."

"Rowa dai Yaya,."

"Allah ba rowa ba, in dai yagani sai ya dumbuza nan da nan sai kiga ya kare."

"Ai Yaya ke da Ya Fauwaz kamar Tom and Jerry kuke,ina wuni?"

"Lafiya lou, bismillah ci kad'an."

"A ah Yaya, nagode tsautsayi yasa naci ki zo kina yin mafarki na."

"Kin wa kanki yarinya."

Ta rufe robar ta tura shi gefen kujera tana karkade hannun ta

"Babar ku ce tayi min da kanta, naga kwana biyu shiri take nema da kowa a gidan nan, inaga dai tasu ce ta hado shi da Baban naku."

"Kai Yaya, saboda haka aka yi miki dambun?"

"Allah kuwa ai ina lura da komai, ina kuma shan kallo na..."

"Kuma tunda dai ina cin riba sai su karata chan." Ta dora

"Hajiya Yaya kenan."

"Uhum, ya akayi da magana ne?"

"A ah babu, zuwa nayi na ganki kuma mu tafi tare ki kwana mu raba dare muna hirar bankwana."

"Allah ya tsareni da zuwa gidan ku wallahi, Allah ya kiyaye ya kaiku lafiya."

"Yanzu ba zaki zo muje ki kwana ba?"

"Ba zani ba wallahi, kar kuma ki ishen da iyayi bayan ba har zuciyarki kike maganar tafiyar ba."

"Allah Yaya har zuciya ta nake yi."

"Toh naji, zuwa ne ba zan ba,ehe."

"Toh shikenan Yaya, amma zaki rakamu airport din ko?"

"Ko gaban gate din gidan nan ba zan rakaku ba bari kiji, salon a hada baki dake a sani a jirgin haka kurum."

"Kai Yaya ana tafiya ne ba visa ba komai?"

"Oho na sani?"

"Toh kuma ai naji zaku je Umrah wannan azumin sannan kuje hajji da babbar sallah, yanzu ya za'a yi kenan?"

"A mota zamu ko a jaki."

Tace tana gimtse fuska, dariya sosai Jidda tayi har da rike ciki. Tsinken sakace Yaya ta dauka tana sakacen tana hararar Jiddan da take mata dariya

"Jakin ne ya ban dariya Yaya, afuwan!"

"Kece da kayan haushi ai."

"Nayi shiru toh, kinga kar muyi fada tunda dai tafiya zan."

"Ba zamuyi ba ai, ya kike fama da dan dunkum din mijin ki kuwa?"

"Kai Yaya."

"Yo Allah ai sai hakuri irin su."

"Na yanzu ba haka suke ba fa Yaya."

"Toh ya suke? Ban labari."

"A ah, kawai dai suna da kirki da dadin zama in dai ka iya zama dasu."

"Ni rashin iya zama da su ne yasa nasha wuya wajen Malam kenan kike so kice."

"Ni? Bance ba Yaya, a bar maganar toh."

"A barta, dan ni ko Qurani za'a dafa ace min masu irin halin Malam na da dadin zama ba lallai na yarda ba, karshen magana kenan."

"Hahaha, karshen magana kenan kuwa Yaya."

"Ah toh "

"Bari na je na gaida Mama toh, zamu dawo muci dambun naman ni da su Amira."

"Wallahi kika gayyato min su tamu ce ni dake."

"Dan kad'an zaki sammana." Tace tana ficewa

"Karfa ki fara na gaya miki." Ta daga murya, sai kuma ta mike ta dauke robar ta shiga da ita daki ta bud'e cikin kayan ta, ta tura a ciki ta rufe har da saka key sannan ta dawo falon tana sababi.

Mama ce kadai a falon da ta shiga, tana zaune cikin ado amma kuma fuskar ta, ta nuna tana dan cikin damuwa, kallon Jiddan tayi sanda ta shigo duk sai taji kunya kafarta ta hau harhadewa ta samu ta karaso ta zube a k'asan carpet cikin tsananin girmanawa ta gaida Maman

"Lafiya lou, kuna lafiya?" Ta dora akan amsar gaisuwa

"Lafiya kalou alhamdulillah."

Jiddan ta amsa cike da mamaki doguwar amsar lafiya lou din da Maman ta baya hade da tambayar lafiyar su bayan a dah lafiya kawai take cewa shima a gajarce tana kin kallon Jiddan

"Goben da karfe nawa zaku tafi?"

"Da asubah yace."

Gid'a kai tayi

"Ga kayan ku chan da yace kuna bukata idan kun tashi sai ku tafi dasu."

"Ok tam, mun gode Allah ya saka da Alkhairi."

"Amin."
Chapter 72 · 0% Book details