← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 76

Sashe 3

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da kai ta amsa tana kallon dakin, fita tayi taje ta sallami Abun sannan ta dawo tace tayi alwala, itama taje dakin ta, tayi alwala sukayi sallar a tare, sannan ta kunna mata kallo tace tana zuwa.
Part din Maigidan ta nufa bayan ta dora ruwa a saman gas din dake kitchen din bangaren nata, ta gyara masa dakin duk da kafin ta tafi ma sai da ta gyara amma tasan da gayya Maman zata bata musamman toilet, haka ko yaushe take sake gyarawa idan zata shiga ta bata sau dubu bata kuma taba tanka mata ba, yau din ma sai da ta sake gyarawa ta kunna turare sannan ta fito, ta dawo ta samu ruwan ya tafasa ta cika flask sannan tayi masa tuwon alkama wanda zai ci yanzu da kuma safe, ta zubawa Saudah a ciki ta kirawo ta kitchen din duk dan ta sake da ita, ta karba ta fita, Usman da ya gama zaman falon ya shigo ya haye kafar Jidda yana mata magana

"Kece Yayarmu da Anty tace zata kawo mana ke?"

Gid'a masa kai Jidda tayi, sannan tayi masa murmushi

"Zaka ci tuwo?" Tace masa tana kallon plate din dake gabanta.

"Naci tare da Muhammad, amma zan kara naki."

"Toh muci."

Ta tankwashe kafarta shima sai yayi yadda tayi, suka shiga cin tuwon a tare, har suka gama Anty na ta kaiwa da komowa a tsakankanin bangaren Maigidan da nata, sai da ta gama hada masa komai sannan ta nutsu ta zauna taci abincin ta watsa ruwa dan a gajiye take jin ta sosai dan ba wani zama tayi ba tunda suka shigo. Wajen takwas da arba'in Baban ya dawo, sun idar da Isha Usman yayi bacci, Antyn tace itama Jiddan taje ta kwanta, ta rakata har daki ta nuna mata duk abinda zata bukata ta kawo mata ruwa saboda dare sannan ta dauko Usman ta dawo dashi dakin tayi musu addua sannan ta kashe musu wutar dakin ta nufi bangaren Baba.

***A zaune ta samesu da Mama, ta bararraje tamkar kwananta ne ranar, ta bude masa abincin har ya soma ci yana bata labarin kasuwa, wani banzan kallo maman ta watsa mata, tayi tsaye ranta na sosuwa da abinda ake mata, dagowa yayi ya kalle ta,

"Halima, karaso mana kika ja tunga anan, kinga yayarki ko? Wai kin sha wahalar hanya shine take taimaka miki da wannan babban aikin."

Yake tayi ta karaso ta zauna daga kubin damar sa, ta gaishe shi a ladafce ya amsa mata yana tambayar yadda ta baro su

"Ina fatan dai kafar Yaya da sauki."

"Alhamdulillah dai toh.

"Allah ya bashi lafiya, zan yi kokari a weekend din nan naje na sake dubo sa, ina yar taki? Kin taho da ita ice ko?"

"Eh tayi bacci."

"Ok madallah, na ganta gobe idan Allah ya kaimu."

"Amin." Tace sai ta mike ta shige bedroom din ta zauna a sanyaye, sama-sama take jiyo hirar su har wajejen goma na dare sannan taji tafiyar Maman. Kwanciya kawai tayi dan babu kuma bukatar ta sake komawa falon.

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
[11/25, 3:54 PM] Rano2: Sanadin
             Labarina

                   Free Page ( 3)

©®Hafsat Rano

***

***Kiran farko akan kunnen ta, saboda yadda jikinta ya saba da tashin wuri, dan tun bata iya tashi ba har ya zame mata jiki, ko bata ji kira ba zata mike, wataran ko sallah Lami bata barin ta tayi zata fara sakata aiki, itace dauko itace, itace debo ruwa da sharar gidan baki daya dan duk sai tayi su kafin ta tafi makaranta wadda take da yar tafiya tsakanin su, haka ta saba ta goge tun shekarun ta basu kai haka ba, babu wani aiki da yake bata wahala sai dai idan ba sunan sa aiki ba. Zama tayi jugum tana kallon yanayin dakin, ta kalli Usman da yake bacci a gefenta, tana matukar son yara, haka take ko a gida bata da aiki sai jajibo yaran makota kafin Lami ta hanata. Turo kofar akayi, Anty ta shigo sanye da Hijabi, ganin ta a zaune ya bata maki

"Har kin tashi Jiddah?" Tace tana karasowa cikin dakin

"Tun dazu na tashi."

"Toh maza tashi kije kiyi alwala muyi sallah, Usman be yi kuka ba ko?"

"A ah be yi ba."

"Toh yi alwalar maza kizo muyi sallah."

"Toh." Tace ta sakko, taje tayo alwala suka fara yin raka'atanil fajr sannan sukayi subh. Al'kurani ta dauko suka fara daga Falak da Nasi, zuwa in da Jiddan ta tsaya a karatun, ta yaba sosai da yadda take karatun dan batayi tunanin hakan ba duk da baffa ba daga nan ba wajen riko da addini. Suna zaune tare har garin yayi sha, tace mata ta koma ta kwanta, ita kuma ta fita zuwa shashen Baban dan tasan zuwa lokacin ya dawo daga masallaci. Tana fita ta fito itama ta je kitchen ta dauko tsintsiya da faka dan ko ta kwanta ba wai iya baccin zatayi ba, bata saba ba, ta share falon tas ta gyara kitchen ta wanke kwanukan da suka bata jiya da daddare sannan ta wanke toilet, bayan ta gama usman ya tashi, ta rakashi bandakin tayi masa alwala da brush sannan tace yayi sallah, be iya ba tunda karami ne haka yayi tana kallon sa.
  Wajen takwas Antyn ta dawo shashen sai dai tsananin mamaki ya kamata, ganin yadda ta gyara ko ina kamar ba ita ba, murmushi kawai ta dinga yi tana wa Allah godiya da ya duba ta ya bata 'ya me taimaka mata. Kunun da Abu ta dama tazo kawo wa kawai taga yadda ta gyara ko ina, albarka ta dinga saka mata sannan tace taje tayi wanka zata je ta gaida Baba idan sun gama karyawa.
   A babban falon suke karyawa gaba dayan su, har Baban dan yace cin abinci a tare yana kara shakuwa, shiyasa suke zama kowa yaci da dan uwansa musamman weekend da baya fita da wuri sai rana ta daga. Fitowar ta kenan daga wanka ta gama saka kayanta tana goge ruwan da yake akan fuskar ta Amira da ta sato hanya ta leko dakin fuskarta a sake,

"Kawata." Tace tana sako jikinta cikin dakin

"Amira." Ta kira sunan ta da taji Antyn ta fada jiya, hakan yayi ma Amiran dadi

"Jiddah ko?" Kai ta daga Mata

"Kizo muje mu karya, kinsan gaba daya muke yin breakfast har Baba."

"Hadda ni?"

"Eh, kema kin zama yar gidan nan ai, taho muje."

Ta ja hannun ta suka fito, bata so ba dan tana da jin kunya sosai da rashin saurin sabo, bata kuma saba da mutane da yawa ba daga ita sai baffanta sai Inna Lami. Sun firfito dukkan su kowa na zaune wasu a kasa wasu a saman kujera, su biyu ne mata a zaune Maryam, sai Safiyya wajen su Amiran ta jasu, tace

"Ya Sofy, Mero, ga Jiddah."

"Sannun ta."

Safiyyan tace tana danna wayarta, babba ce dan da alama duk ta girme su,  murmushi sauran sukayi mata hakan ya sakata sakin jikinta kadan ta zauna a gefen Amiran ta makale. Maman su ce ta fito ta wata kofa taci ado sosai, kamar wadda zata tafi gasar kyau, babba ce dan akalla shekarun ta zasu kai arba'in da biyar amma ba zaka taba cewa ta kai ba saboda gyara da kyawun jiki. Duk suka gaishe ta ta amsa idon ta akan Jiddan, da sauri tace

"Ina kwana?"

"Lafiya lou bararoji."

Tace tana wucewa kujerar da Muhammad da Usman suke zaune,
Suka tashi ta zauna tana hararar Amira. Bararojin ne ya dinga yawo a kwakwalwarta har akayi sallama aka shigo falon. Baba ne ya shigo Anty na biye dashi itama tayi wanka sai dai shigarta very simple ba kamar Mama ba, gaishe da Maman tayi da yake a gaban Baba ne ta amsa a sake, zama sukayi dukka sauran yaran suka gaida Antyn da Baban itama sai tabi sahun su ta gaida Baban.

"Zo 'yata,yanzu nake shirin tambayar ki dama."

Tashi tayi a kunyace taje gabansa ta durkusa ya shafa kanta

"Ki saki jikinki kinji, nan gidanku ne ga yan uwanki nan dukkansu,duk abinda kike bukata ki sanar dani kinji?"

Daga kanta tayi alamar toh, ya sake shafa kanta yace

"Yawwa, Allah yayi muku albarka baki dayan ku."

"Amin."

Suka amsa gaba daya, ran Mama ya baci sosai amma bata so ta nuna ta danne tana kallon Safiyya da itama ita take kallo.

"Maryama jeki kira yayanku, bansan me suke ba na kuma fada musu da wuri zamu fita."

"Wani wajen zaku ne?"

"Eh zamu je a dauko Yaya, hutun ya isa haka gashi lokacin komawa ganin likitan ta yayi."

"Gaskia."

Tace a kasan ranta kamar ta kurma ihu, bata san zaman Yayan tare dasu musamman tun bayan da ta tirsasawa Baban ya kara aure tun daga sannan ta tsane ta, dan tun asali dama Yaya bata son ta, shiyasa sai da tayi yadda tayi ta saka ya auro mata wadda ko a mafarki bata taba kawo ta a matsayin kishiyar ta ba,yar kauye kuma yar talakawa, ita din yar masu kudi ce sannan tana business dinta tana samun kudi sosai, tun daga sannan ta kullaci Yayan, tafiyar da tayi tsawon wata guda ya bata damar sakewa a cikin gidan, jin zata dawo yanzu ya saka ta kasa ko sakewa taci abincin, ta tashi tace zata tafi, Safiyya ce ta rike mata jaka suka fice tare.
A harabar gidan ta hadu dasu, Fauwaz ne a gaba sai shi a baya yana nannade hannun rigar sa zuwa sama, kansa kasa fuskar sa babu yabo babu fallasa Safiyya ta kira sunan sa ganin zai wuce su

"Ya Tariq!" Tsayawa yayi yana kallon ta, kafin yace

"Mah, fita zakuyi?"

"Eh, zamu je cikin gida."

"This early?"

"Past 9 fa, kai kake ganin yayi wuri."

"Ok a gaida su."
Chapter 3 · 0% Book details