Sashe 42
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da ya fita sai ya rasa abinda yake masa dadi, ko giyar wake yasha ba zai iya aikata abinda Maman take so ba, dan ba itace akan gaskiya ba, Baba yafi ta gaskiya dan haka dole ne yasan yadda zai yi be bata wa daya daga cikin su ba.
Iyaye dole ne ka bisu kayi musu biyayya kuma mahalifiya tafi karfin wasa shiyasa yake matukar yi mata biyayya domin samun rabauta. Amma kuma a wannan gabar be san me yasa ba, baya jin yana tare da Maman.
Zaman sa yayi a waje tare da masu gadin gidan lokaci zuwa lokaci yana dan saka musu baki a hirar dan yadda gidan yake cike da mutane bazai sake shiga ciki ba, tunda dai hankalin Maman ya kwanta for now zai tafi da ita a haka kafin yasan abun yi.
Sai da akayi la'asar sannan ya tashi daga wajen, ya shiga cikin dakin su ya hau tattare muhimman takardun sa waje daya, ya zuba su a yar karamar jaka ya saka a bayan mota, sannan ya tafi kiran Yayan da ta turo tana neman sa. Chan cikin dakin ta, ta kule dan ba kowa take so yasan maganar da zasuyi ba. Mamakin ganin ta a nutse a zaune yasa shi shan jinin jikin sa
"Lafiya Yay?"
"Lafiya ta kalou wallahi."
"Menene ya faru?"
"Takardr jidda zaka ban?"
"Takarda kuma Yaya?"
"Eh, tunda baka son ta ba, ka sakar musu 'ya taje ta auri wanda yake son ta."
"Wanene?" Ya bata fuska
"Ina ruwan ka? Wani ne yazo tun kafin ma ayi maganar ka, wai mu masu shishigi da son gwaninta muka ce gida be koshi ba,ashe zaka zo ka watsa mana ido?"
"Aina yake shi din?"
"Oho ba zaka ji ba, ka bata takardar ta ba sai ta sake kwana da igiyoyin auren ka akanta ba."
"Kuma ita ma tana son shi?"
"Kaji mun yaro, ina ruwanka da wannan kuma? Kai tunda ba da gaske kake ba, ai sai kawai ka yanke hukunci Amma ba zai yiwu ka hanata kula kowa ba kai kuma baka so."
Mikewa yayi ransa a baci ya fice be sake cewa komai ba, dariya suka kwashe da ita, Fauwaz dake makale ya fito suka tafa da Yaya
"Kinsan ta kan tsiya Yaya."
"Ni din ta wasa ce? Sai shegen kishi amma girman kai ya hana shi gane halin da yake ciki."
"Ya sani fa Yaya, kawai yana hana kansa yarda da hakan ne, bari muga abinda zai yi kuma, bari naje naji yadda ake ciki."
"Karka manta kazo ka fesa min."
"Akwai amaana ai ni dake tawan."
"Amanar kad'an ce, tunda ka kusa kashe ni na dawo daga rakiyar ka, bakin mugu."
"Ai ya wuce sai zamu Kano sallah, da kafarki zaki taka ki shiga jirgin ma Hajiya Yaya."
"Bana so, babu kuma shegen da zai saka ni shiga."
"Zamu gani dai, bari naje nagano."
"Munafuki." Tace tana kallon sa, be ji me tace ba, ya fice dan da yaji sai ya dawo sun yi ta da ita.
Kai tsaye part din Aunty Tariq ya nufa ransa a bace fuskar nan tasa a hade tamau, babu kowa a part din Aunty na side din Baba, ita kadai ce sai Usman da yake wasa a falo yana kallon Disney World, tasowa yayi da sauri yayi hugging din Tariq din, ya d'aga shi sama yana kokarin daidaita fuskar sa
"Wasa kake?" Yace yana sauke shi k'asa
"Eh tare muke yi da Yaya Jidda tace zatayi sallah."
"Ina Aunty?"
"Ta fita."
"Ok zauna kayi wasanka ko? Ina zuwa."
Yace ya nufi dakin Jiddan, ta idar da sallah kenan taji rigar dake jikin ta, ta takura mata, sai kawai tayi deciding ta cire ta, data raka Safeera ne ta sakata amma dama bata iya zaman gida da ita, riga da wandon ta ciro na bacci masu dan kauri rigar iya guiwa sai dogon wando, ta saka tana gyara gashin kanta da ya barbazu akan nata ya murd'a kofar ya shiga da sallama muryar sa a chunkushe kamar wanda ya saka wani abu a makoshin sa ya tokare wajen. Kasa dagowa tayi tayi tsam a wajen da take ya shiga takowa yana karewa dogon gashin nata kallo. A daf da ita ya tsaya ta kalli kafarsa dake sanye da takalmi sau ciki. Muryar tasa a ciki-ciki yayi magana
"Ina Hijab dinki?"
Bata amsa ba, dan bata ga amfanin tambayar ba, wurwurga idanun sa yayi tayi a cikin dakin ya taka zuwa wajen da kayan ta suke, ya bude wardrobe din yana kallon jerin kayan dake gyare a cikin wardrobe din.
"Lefe." Ya fado masa a ransa, hannu ya sa ya ciro Hijab guda daya a cikin jerin kayan, pant dinta ne ya fado, ya sunkuya ya dauka ya kalli wajen da take a tsaye, da sauri ta kautar da kanta kunya matsananciya na kamata, ciki ya mayar ya rufe ya dawo ya mika mata, sannan ya dauki wayar ta dake ajiye a saman gadon, yace tasa Hijab din.
"Ina zamu?" Tace rike da Hijab din bata saka ba
"Gidan Mijinki zaki." Ya amsa mata kai tsaye, yayi hanyar barin dakin sai da ya kai karshe sannan yace
"Karki bata min lokaci."
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (33)
Be iya motsawa daga wajen ba, maganganun Mama da nata na cigaba da yi masa yawo akai, toh ko dai son nata yake? Ya tambayi kansa. No ba haka bane. Wata zuciyar ta rad'a masa, tausayin ta kawai kake ji, ya sake jin wata zuciyar ta tunasar dashi.
"Eh haka ne, tausayi ne kawai nothing more."
Yayi assuring kansa yana samun hujjar da zai rike, kad'a kansa yayi ya fito daga dakin, duk da maganar ta, ta bata masa rai amma kuma ba zai yi abinda suke so ita da Maman ba, sai yayi istikara sannan ya samu gamsashishiyar hujjar da zai rikewa Baba ya yarda dashi. Wani kallo Yaya tayi masa da ya fito, yayi kamar be ganta ba yayi ficewar sa, ta yi dariya tana girgiza kanta, tasan akwai sauran drama amma kuma a chan k'asan zuciyar tana tausayin Tariq din, dan tasan irin su so be iya yi musu da dadi ba.
Tunda ta shiga dakin take juyi a gado, kamar ta tattara kayan ta, ta tafi wajn Baffa haka take ji, baki daya babu abinda yake mata dadi, tana nan kwance har aka soma dawowa, su aunty ne yan farkon tahowa suka taho tare da Safeera da zata kwana a gidan. Tana jin su ta fito da sauri, suka rungume ita da Safeera idon Aunty akanta, sai da suka zauna sannan Auntyn tace
"Jidda me ya faru ne wai?"
Turo baki tayi cikin yanayin rashin jin dadi tace
"Hanani yayi."
"Tariq hoo, amma me yasa?"
"Nima ban sani masa ba, kawai mugunta ce wallahi."
Tace kwala na sake taruwa a idon ta dan ko tunawa tayi sai taji hawaye
"Karki kara cewa mugunta duk tsiya mijinki ne, kuma duk abinda yace shi zakiyi."
"Aunty amma kinsan be kyauta ba ko?"
"Toh me zan ce jidda, tunda shine yake da ikon barki ko hanaki."
"Aikuwa, kuma dole ayi biyayya."
Safeera tace tana dariya, duka Jidda takai mata, tace ta taso su shiga ciki, suka bar Aunty ita kadai sai itama kawai ta wuce dakin ta dan watsa ruwa ta dan warware gajiya.
Bayan tayi wankan tana zaune a falon akayi knocking, kasancewar duk masu aikin gidan idan dare yayi basa shigowa suna bq yasa ba kowa sai ita kadai a falon, tashi tayi ta bud'e kofar sai taga Tariq a tsaye, matsa masa tayi ya shigo sannan ya rufe kofar
"Aunty yunwa."
Yace yana zama idon sa akan hanyar dakin Jidda
"Bari naga ko zaka samu wani abun a kitchen."
"Aunty Indomie nake so, tunda nazo banci ba, a kira sai ta dafa min karki wahalar da kanki."
"Aikuwa Jidda gwana ce, dan tafi ni ma, suna ciki da kawarta Safeera bari na kira ta."
"Nagode Aunty."
"Ah ba komai ai, bari na turo ta."
Tayi gaba tana murmushi, a kalla yanzu ta tabbatar da Tariq yana son Jiddan ta, abinda dama yake daga mata hankali kenan, sai gashi duk kowa ya gama gano shi duk da shi be gama gano kansa ba, he's so obsessed with her. Knocking tayi musu daga kofar ta dan bud'e tace
"Zo ki dafawa Tariq Indomie yunwa yake ji."
Zaro ido tayi,
"A daren nan Aunty?"
"Eh yana falo yana jiran ki, ni kwanciya ma zan dan na gaji sosai, sai da safe Safeera."
"Sai da safe aunty."
"Jiran ki yake." Ta maimaita mata ganin tana zaune ko motsi batayi ba, tashi tayi ta dauko Hijab ta zunbula har k'asa sannan ta zura slippers ta fito tana zumburo baki Safeera na mata dariya,
"Idan naji kin dade zan rufe kofa ta "
tace mata tana dariya
"Allah ya kiyaye na dade, sama-sama zan dafa masa na dawo daki, a daren nan ace ka wani dafa abinci kawai dan a kuntata maka."
Tayi maganar bayan ta rufo dakin yadda Safeeran ba zata jiyo ta ba, yana tsaye jikin bangon corridor din duk yaji me tace, kallon sa tayi gaban ta, ya fadi, ya kad'a kansa yana nuna mata hanya
"Wuce na fasa Indomie din ma, sakwara nake so."
"Wallahi ban iya ba." Tace da saurin ta, dariya taso bashi ya kanne yana nuna mata hanya
"Ita mijinki yake so dole kuma ki yi masa abinda yake so ko na fadawa Aunty."
Tafiya ta cigaba da yi zuwa kitchen din ya take mata baya, ya samu jikin freezer ya tsaya yana folding din hannun sa, tsayawa tayi tana kalle-kalle kamar me neman wani abu,
"Dafa indomie din amma kikayi min sama-sama sai kin daka min sakwara da tiny hands din nan naki."
Indomie din ta dauko ta, ta dora yana kallon ta,
"Bana son jagwalgwalo kuma."
"Ni bana iya abu idan aka sakani a gaba."
"In fita kenan?"
"Eh."
Tsalle yayi ya haye saman deep freezer din
"Karewarta ma kenan, kiyi sauri kuma karki sa yunwa ta kama ni."
Iyaye dole ne ka bisu kayi musu biyayya kuma mahalifiya tafi karfin wasa shiyasa yake matukar yi mata biyayya domin samun rabauta. Amma kuma a wannan gabar be san me yasa ba, baya jin yana tare da Maman.
Zaman sa yayi a waje tare da masu gadin gidan lokaci zuwa lokaci yana dan saka musu baki a hirar dan yadda gidan yake cike da mutane bazai sake shiga ciki ba, tunda dai hankalin Maman ya kwanta for now zai tafi da ita a haka kafin yasan abun yi.
Sai da akayi la'asar sannan ya tashi daga wajen, ya shiga cikin dakin su ya hau tattare muhimman takardun sa waje daya, ya zuba su a yar karamar jaka ya saka a bayan mota, sannan ya tafi kiran Yayan da ta turo tana neman sa. Chan cikin dakin ta, ta kule dan ba kowa take so yasan maganar da zasuyi ba. Mamakin ganin ta a nutse a zaune yasa shi shan jinin jikin sa
"Lafiya Yay?"
"Lafiya ta kalou wallahi."
"Menene ya faru?"
"Takardr jidda zaka ban?"
"Takarda kuma Yaya?"
"Eh, tunda baka son ta ba, ka sakar musu 'ya taje ta auri wanda yake son ta."
"Wanene?" Ya bata fuska
"Ina ruwan ka? Wani ne yazo tun kafin ma ayi maganar ka, wai mu masu shishigi da son gwaninta muka ce gida be koshi ba,ashe zaka zo ka watsa mana ido?"
"Aina yake shi din?"
"Oho ba zaka ji ba, ka bata takardar ta ba sai ta sake kwana da igiyoyin auren ka akanta ba."
"Kuma ita ma tana son shi?"
"Kaji mun yaro, ina ruwanka da wannan kuma? Kai tunda ba da gaske kake ba, ai sai kawai ka yanke hukunci Amma ba zai yiwu ka hanata kula kowa ba kai kuma baka so."
Mikewa yayi ransa a baci ya fice be sake cewa komai ba, dariya suka kwashe da ita, Fauwaz dake makale ya fito suka tafa da Yaya
"Kinsan ta kan tsiya Yaya."
"Ni din ta wasa ce? Sai shegen kishi amma girman kai ya hana shi gane halin da yake ciki."
"Ya sani fa Yaya, kawai yana hana kansa yarda da hakan ne, bari muga abinda zai yi kuma, bari naje naji yadda ake ciki."
"Karka manta kazo ka fesa min."
"Akwai amaana ai ni dake tawan."
"Amanar kad'an ce, tunda ka kusa kashe ni na dawo daga rakiyar ka, bakin mugu."
"Ai ya wuce sai zamu Kano sallah, da kafarki zaki taka ki shiga jirgin ma Hajiya Yaya."
"Bana so, babu kuma shegen da zai saka ni shiga."
"Zamu gani dai, bari naje nagano."
"Munafuki." Tace tana kallon sa, be ji me tace ba, ya fice dan da yaji sai ya dawo sun yi ta da ita.
Kai tsaye part din Aunty Tariq ya nufa ransa a bace fuskar nan tasa a hade tamau, babu kowa a part din Aunty na side din Baba, ita kadai ce sai Usman da yake wasa a falo yana kallon Disney World, tasowa yayi da sauri yayi hugging din Tariq din, ya d'aga shi sama yana kokarin daidaita fuskar sa
"Wasa kake?" Yace yana sauke shi k'asa
"Eh tare muke yi da Yaya Jidda tace zatayi sallah."
"Ina Aunty?"
"Ta fita."
"Ok zauna kayi wasanka ko? Ina zuwa."
Yace ya nufi dakin Jiddan, ta idar da sallah kenan taji rigar dake jikin ta, ta takura mata, sai kawai tayi deciding ta cire ta, data raka Safeera ne ta sakata amma dama bata iya zaman gida da ita, riga da wandon ta ciro na bacci masu dan kauri rigar iya guiwa sai dogon wando, ta saka tana gyara gashin kanta da ya barbazu akan nata ya murd'a kofar ya shiga da sallama muryar sa a chunkushe kamar wanda ya saka wani abu a makoshin sa ya tokare wajen. Kasa dagowa tayi tayi tsam a wajen da take ya shiga takowa yana karewa dogon gashin nata kallo. A daf da ita ya tsaya ta kalli kafarsa dake sanye da takalmi sau ciki. Muryar tasa a ciki-ciki yayi magana
"Ina Hijab dinki?"
Bata amsa ba, dan bata ga amfanin tambayar ba, wurwurga idanun sa yayi tayi a cikin dakin ya taka zuwa wajen da kayan ta suke, ya bude wardrobe din yana kallon jerin kayan dake gyare a cikin wardrobe din.
"Lefe." Ya fado masa a ransa, hannu ya sa ya ciro Hijab guda daya a cikin jerin kayan, pant dinta ne ya fado, ya sunkuya ya dauka ya kalli wajen da take a tsaye, da sauri ta kautar da kanta kunya matsananciya na kamata, ciki ya mayar ya rufe ya dawo ya mika mata, sannan ya dauki wayar ta dake ajiye a saman gadon, yace tasa Hijab din.
"Ina zamu?" Tace rike da Hijab din bata saka ba
"Gidan Mijinki zaki." Ya amsa mata kai tsaye, yayi hanyar barin dakin sai da ya kai karshe sannan yace
"Karki bata min lokaci."
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (33)
Be iya motsawa daga wajen ba, maganganun Mama da nata na cigaba da yi masa yawo akai, toh ko dai son nata yake? Ya tambayi kansa. No ba haka bane. Wata zuciyar ta rad'a masa, tausayin ta kawai kake ji, ya sake jin wata zuciyar ta tunasar dashi.
"Eh haka ne, tausayi ne kawai nothing more."
Yayi assuring kansa yana samun hujjar da zai rike, kad'a kansa yayi ya fito daga dakin, duk da maganar ta, ta bata masa rai amma kuma ba zai yi abinda suke so ita da Maman ba, sai yayi istikara sannan ya samu gamsashishiyar hujjar da zai rikewa Baba ya yarda dashi. Wani kallo Yaya tayi masa da ya fito, yayi kamar be ganta ba yayi ficewar sa, ta yi dariya tana girgiza kanta, tasan akwai sauran drama amma kuma a chan k'asan zuciyar tana tausayin Tariq din, dan tasan irin su so be iya yi musu da dadi ba.
Tunda ta shiga dakin take juyi a gado, kamar ta tattara kayan ta, ta tafi wajn Baffa haka take ji, baki daya babu abinda yake mata dadi, tana nan kwance har aka soma dawowa, su aunty ne yan farkon tahowa suka taho tare da Safeera da zata kwana a gidan. Tana jin su ta fito da sauri, suka rungume ita da Safeera idon Aunty akanta, sai da suka zauna sannan Auntyn tace
"Jidda me ya faru ne wai?"
Turo baki tayi cikin yanayin rashin jin dadi tace
"Hanani yayi."
"Tariq hoo, amma me yasa?"
"Nima ban sani masa ba, kawai mugunta ce wallahi."
Tace kwala na sake taruwa a idon ta dan ko tunawa tayi sai taji hawaye
"Karki kara cewa mugunta duk tsiya mijinki ne, kuma duk abinda yace shi zakiyi."
"Aunty amma kinsan be kyauta ba ko?"
"Toh me zan ce jidda, tunda shine yake da ikon barki ko hanaki."
"Aikuwa, kuma dole ayi biyayya."
Safeera tace tana dariya, duka Jidda takai mata, tace ta taso su shiga ciki, suka bar Aunty ita kadai sai itama kawai ta wuce dakin ta dan watsa ruwa ta dan warware gajiya.
Bayan tayi wankan tana zaune a falon akayi knocking, kasancewar duk masu aikin gidan idan dare yayi basa shigowa suna bq yasa ba kowa sai ita kadai a falon, tashi tayi ta bud'e kofar sai taga Tariq a tsaye, matsa masa tayi ya shigo sannan ya rufe kofar
"Aunty yunwa."
Yace yana zama idon sa akan hanyar dakin Jidda
"Bari naga ko zaka samu wani abun a kitchen."
"Aunty Indomie nake so, tunda nazo banci ba, a kira sai ta dafa min karki wahalar da kanki."
"Aikuwa Jidda gwana ce, dan tafi ni ma, suna ciki da kawarta Safeera bari na kira ta."
"Nagode Aunty."
"Ah ba komai ai, bari na turo ta."
Tayi gaba tana murmushi, a kalla yanzu ta tabbatar da Tariq yana son Jiddan ta, abinda dama yake daga mata hankali kenan, sai gashi duk kowa ya gama gano shi duk da shi be gama gano kansa ba, he's so obsessed with her. Knocking tayi musu daga kofar ta dan bud'e tace
"Zo ki dafawa Tariq Indomie yunwa yake ji."
Zaro ido tayi,
"A daren nan Aunty?"
"Eh yana falo yana jiran ki, ni kwanciya ma zan dan na gaji sosai, sai da safe Safeera."
"Sai da safe aunty."
"Jiran ki yake." Ta maimaita mata ganin tana zaune ko motsi batayi ba, tashi tayi ta dauko Hijab ta zunbula har k'asa sannan ta zura slippers ta fito tana zumburo baki Safeera na mata dariya,
"Idan naji kin dade zan rufe kofa ta "
tace mata tana dariya
"Allah ya kiyaye na dade, sama-sama zan dafa masa na dawo daki, a daren nan ace ka wani dafa abinci kawai dan a kuntata maka."
Tayi maganar bayan ta rufo dakin yadda Safeeran ba zata jiyo ta ba, yana tsaye jikin bangon corridor din duk yaji me tace, kallon sa tayi gaban ta, ya fadi, ya kad'a kansa yana nuna mata hanya
"Wuce na fasa Indomie din ma, sakwara nake so."
"Wallahi ban iya ba." Tace da saurin ta, dariya taso bashi ya kanne yana nuna mata hanya
"Ita mijinki yake so dole kuma ki yi masa abinda yake so ko na fadawa Aunty."
Tafiya ta cigaba da yi zuwa kitchen din ya take mata baya, ya samu jikin freezer ya tsaya yana folding din hannun sa, tsayawa tayi tana kalle-kalle kamar me neman wani abu,
"Dafa indomie din amma kikayi min sama-sama sai kin daka min sakwara da tiny hands din nan naki."
Indomie din ta dauko ta, ta dora yana kallon ta,
"Bana son jagwalgwalo kuma."
"Ni bana iya abu idan aka sakani a gaba."
"In fita kenan?"
"Eh."
Tsalle yayi ya haye saman deep freezer din
"Karewarta ma kenan, kiyi sauri kuma karki sa yunwa ta kama ni."