Sashe 41
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace ganin yana matso ta, amma duk da haka sai da yayi hugging din nata,abinda yake taso tun dazu, yana so ya shaki kamshin jikin nata sosai amma kuma yana hana kansa, daga karshe yaga ba zai iya ba, tunda dai ba wani abu yayi ba, kuma ai ba haramci ya aikata ba. Yaya ce tayi saurin fita dan da ta labe a falon, dariya ma ya bata dan tasan dama wuyar ta yazo hannu, irin su masu sum-sum din nan sun fi kowa iya shege
"Almuri." Tace tana zama a in da ta tashi,
"Me ya faru Yaya?"
"Wai ya hanata zuwa wajen bikin dan shegen kishi."
"Abinda kake so ai shi kake kishi Yaya."
"Bar dan bantan uba, yana so yana yare, zai gane shayi ruwa ne, dama ai dan hakkin daka raina..."
"Haka ne, kina ga a yadda ya shigo fa, kamar ma da fari be lura damu ba."
"Ina zai lura so ya rufe masa ido."
"Kai Yaya."
"Allah kuwa, yaga yar karamar yarinya duk ya rude babban kwabo, da yana cika bakin shi baya so yan-yan-yan."
***A yadda yake ji kamar kafarsa ba zata dauke shi ba, gashi duk yadda taso ya kyale ta, ya kasa, sai da wayar sa dage cikin aljihun gefen rigar sa tayi kara sannan ya saketa yana matsawa baya, da sauri ta koma cikin dakin ta kule chan karshen gefen gadon shi kuma ya d'aga wayar ganin Mama ce
"Wai Tariq me kake nufi dani ne?"
"Na'am Mama?"
"Eh, Jidda bata zo wajn nan ba, sai naji labari na yawo a wajen wai kaje ka dauke ta a gidan makeup kace ba zata ba, me yasa zaka je ka dauke ta? Kuma me yasa zaka hanata zuwa? Bangane maka ba kwata-kwata."
_"Ba zan iya bari tazo wajen nan ba."_
yayi maganar kasa kasa amma duk da haka sai da taji shi,
"Ba zaka iya bari ba? Saboda kana kishin ta ko?"
" Ni? Noo ba haka bane, kawai dai tunda ba wai an riga an rabu bane, dole na kare martabar auren, shine kawai amma ba wani abu bayan nan."
"Kasan da yake kai ka haife ni TARIQ, son yarinyar nan kake."
"Mama!"
"Ka dauka ana wa namiji auren dole ne kuma baya son matar yayi hakuri ya cigaba da bin ta kamar jela, ina lura da kai wallahi, duk take-taken ka na gani."
"Amma Mama ba haka bane, ni ba haka bane, ba spec dina bace ba, no ba haka bane gaskiya."
"Sai kayi kuma, na bar baki."
Ta katse kiran, rike wayar yayi saroro a hannun sa yana jujjuya maganar da Mamsn tayi masa a ransa. Duk maganar da sukayi tana ji kuma ta san akan ta ne, kekashewa taji zuciyar ta, tayi lokaci daya, babu amfanin cigaba da zubar da hawayen ta akan mutumin da ya cika da son kanshi, tasowa tayi tazo har gaban sa, ta tsaya sannan tace.
"Kayi sauri ka kawo karshen wannan drama din, kaga sai ka samo daidai da kai din."
Daga haka ta wuce shi kawai ta fice daga dakin, ta wuce part din Aunty ta shiga dakinta,tayi kwanciyar ta,tana hana kanta sake kuka akan sa.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (34)
***Wajen Yaya ta nufa dan tasan itace kai tsaye zata saka Baba ko ta hanashi. Ta kuma san ta yadda zata bullo mata ta daina ragawa Mama dan ta lura shirun ta yasa take ganin har yanzu tana da ikon taka ta. Bedroom din Yayan ta shiga ta sameta a kwance tana hutawa bayan ta idar da sallar walaha, tashi tayi zaune suka gaisa sannan tace magana tazo su yi
"Ina jinki Halima, mecece matsalar? Dan nasan dole akwai magana."
"Yaya dama akan maganar Jidda ce, ni a gani na tunda har Tariq ya dawo Jidda ya kamata ta tare a gidanta, dama taron bikin ake so ayi kuma ya nuna baya ra'ayi ni a ganina kawai ta tare shine mafi a'ala."
"Ni kaina nayi wannan tunanin kuma jiran Alhaji nake ya shigo, dan na ga alama dan ku bashi da ta ido sam, gwara su je chan su karata."
Dariya ta saka Yayan ta cigaba da bayani
"Al'muri da yake munafuki ne ai kinga yadda yake ko? Irin masu halin nan ke dai kawai ki kalle su, sun fi kowa iya shakiyanci."
"Yanzu ki barmun komai, a yau ba sai gobe ba zata tare, dan babu amfanin zaman."
"Allah ya kaimu Yaya, dama dai maganar kenan abun ya soma damuna."
"Ai dole, yarinya ma tayi hakuri ki bari zanyi maganin shi a yau din nan, sai kisa ta shirya duk abinda zatayi zuwa anjima."
"Toh bari naje Yaya, Allah ya kara girma."
"Amin kinji? Allah yayi albarka."
***Komawa tayi ta saka jiddah a gaba, da Safeera da ita suka taimaka mata ta hade koman ta waje daya, hannu bata saka ba ita a lallai ba in da zata tunda be san worth din ta ba, babu wadda tabi ta kanta musamman Safeera da tasan munafurci ne kawai ba har zuciyar, take maganar ba. Falo ta dawo tayi zaman ta, tana kissisima yadda zata kaya a zaman nasu, duk da kaso hamsin tana tsoron Mama amma kuma sauran kason na kwadaituwa da son zama dashi din.
Fitowa Safeera tayi ta sameta a falon suka cigaba da zama sai ga Isma'il ya kirata, dagawa tayi jidda tayi kamar bata gane da wanda suke waya ba, suka dan jima suna magana daga karshe ta kashe tana murmushi
"Ya Isma'il ne, kinsan ya kusa zuwa gida."
"Allah sarki, Allah ya taimaka."
"Amin, ni tunda tafiya zakiyi ma ai ba amfanin zama na, zan koma gidan Aunty Sajida kawai."
"Wai waye yace miki tafiya zan? Ki jira mana ki gani, nasan ba in da zanje."
"Toh zamu gani, yarinya gwara ma ki saka ranki tafiya dole."
"Idan nace ba zani ba ai babu me daukata. "
"Wallahi tsaf zai dauke ki din, tab!"
"Ke kika sani."
"Ke ma kin sani ai."
***Ran Mama ya kai karshe a baci, dawowar ta kenan daga wajen Yaaya da ta turo aka kirata ta fada mata yau matar Tariq zata tare, da k'yar ta amsa da toh ta taso tazo ta fadawa su Aunty Nafi, suka kuwa hau fanfata akan karta yarda.
Kiran TARIQ tayi be daga ba, sai ta kira Fauwaz shima sai da ta katse sannan ya biyo kiran tace masa ina Tariq yazo maza-maza, baya nan dan tun safe da ya fita training be dawo gidan ba, gidan sa ya wuce a chan yayi wanka ya shirya sannan ya koma bacci dan yasan idan be more baccin sa ba ya koma sai ya samu matsala, shiyasa har Maman ta kira be ji ba.
Sai da rana tayi sannan ya tashi ya dan sake gyara jikin sa sannan ya hau mota ya dawo gidan. Tun a hanya dama Fauwaz ya fada masa Mama tana neman sa, shiyasa yana zuwa part dinta ya wuce tana ganin sa tace ya shigo suka shige chan dakin ta in da babu kowa.
"So nake ka saki Jidda a yanzu ba sai anjima ba."
Kawai tace masa ko zama bata iya yi ba. Kallon ta yake hankalin sa a tashe, ta hade rai taki bari ko kad'an yaga saukin ta, kasa furta komai yayi, ya dinga kokarin tattaro kalaman bakin sa amma ya gaza furta su, idan har yace zai iya sakin Jidda yayi karya, duk da ba wai yana mata son da ba zai iya rabuwa da ita ba, amma ba zai zo ya samu matsala da iyayen sa akan ta ba, haka kuma ba zai taba so hakan ta shafi iyayen sa ba
"Mama dan Allah mu bari mubi komai a sannu, dan Allah "
"Babu wani bin komai a sannu, yau kwana nawa kaana min alkawari amma ka gaza cikawa sai bin yar karamar yarinya a baya kamar wanda aka gama dashi."
"Wai Maama waye yace bin ta nake?"
"Kasan ni yarinya ce ai, bansan me nake ba."
"Ba haka bane Mama."
"Toh naji, duk ba wannan ba, bana son zaman ku karkashin inuwa daya, dan haka sai ka sawaake mata tunda ka kasa samun mafita."
"Baba fa? Zai yi fushi dani sosai."
"Ka barni dashi kawai, kai dai kayi abinda nace, ba zan iya jure ganin ta a matsayin sirikata ba."
"Amma Mama, mesa kika tsaneta haka?"
"Tambaya ta kake?"
" A'ah, kawai dai naga kamar yayi yawa ne mama, kiyi hakuri dan Allah mubi komai a sannu, Dan Allah muyi wa Baba biyayya kar muzo muyi abinda zai bata masa suna shi yanzu da yake a idon duniya abu karami zaki ji ana yi dashi."
"Ba zan ba, akan yarinyar nan zan iya batawa da kowa, idan har jinin Halima ce zata auri jini na, na gwammace komai ya faru."
"Mah?"
"Idan har na isa da kai, ka rabu da ita."
"Menene laifin ta a gareki Mama?"
"Babu komai, ba abinda tayi min kawai bana son ta ne."
"Shikenan mama, zanyi abinda kike so, amma ina zuwa Dan Allah."
Fuskarta ce ta fadada da farin ciki, t
"Dan Allah da gaske kake?"
Daga mata kai yayi
"Toh madallah, ka gama min komai Allah yayi maka albarka."
"Amin Ya Allah."
Ya juya ya fita ita kuma ta koma wajen su Aunty Nafi zuciyar ta cike da farin cikin zata kuntata wa Auntyn dan dama tayi alwashin sai ta mata abinda zata dade tana jin ciwon sa.
"Almuri." Tace tana zama a in da ta tashi,
"Me ya faru Yaya?"
"Wai ya hanata zuwa wajen bikin dan shegen kishi."
"Abinda kake so ai shi kake kishi Yaya."
"Bar dan bantan uba, yana so yana yare, zai gane shayi ruwa ne, dama ai dan hakkin daka raina..."
"Haka ne, kina ga a yadda ya shigo fa, kamar ma da fari be lura damu ba."
"Ina zai lura so ya rufe masa ido."
"Kai Yaya."
"Allah kuwa, yaga yar karamar yarinya duk ya rude babban kwabo, da yana cika bakin shi baya so yan-yan-yan."
***A yadda yake ji kamar kafarsa ba zata dauke shi ba, gashi duk yadda taso ya kyale ta, ya kasa, sai da wayar sa dage cikin aljihun gefen rigar sa tayi kara sannan ya saketa yana matsawa baya, da sauri ta koma cikin dakin ta kule chan karshen gefen gadon shi kuma ya d'aga wayar ganin Mama ce
"Wai Tariq me kake nufi dani ne?"
"Na'am Mama?"
"Eh, Jidda bata zo wajn nan ba, sai naji labari na yawo a wajen wai kaje ka dauke ta a gidan makeup kace ba zata ba, me yasa zaka je ka dauke ta? Kuma me yasa zaka hanata zuwa? Bangane maka ba kwata-kwata."
_"Ba zan iya bari tazo wajen nan ba."_
yayi maganar kasa kasa amma duk da haka sai da taji shi,
"Ba zaka iya bari ba? Saboda kana kishin ta ko?"
" Ni? Noo ba haka bane, kawai dai tunda ba wai an riga an rabu bane, dole na kare martabar auren, shine kawai amma ba wani abu bayan nan."
"Kasan da yake kai ka haife ni TARIQ, son yarinyar nan kake."
"Mama!"
"Ka dauka ana wa namiji auren dole ne kuma baya son matar yayi hakuri ya cigaba da bin ta kamar jela, ina lura da kai wallahi, duk take-taken ka na gani."
"Amma Mama ba haka bane, ni ba haka bane, ba spec dina bace ba, no ba haka bane gaskiya."
"Sai kayi kuma, na bar baki."
Ta katse kiran, rike wayar yayi saroro a hannun sa yana jujjuya maganar da Mamsn tayi masa a ransa. Duk maganar da sukayi tana ji kuma ta san akan ta ne, kekashewa taji zuciyar ta, tayi lokaci daya, babu amfanin cigaba da zubar da hawayen ta akan mutumin da ya cika da son kanshi, tasowa tayi tazo har gaban sa, ta tsaya sannan tace.
"Kayi sauri ka kawo karshen wannan drama din, kaga sai ka samo daidai da kai din."
Daga haka ta wuce shi kawai ta fice daga dakin, ta wuce part din Aunty ta shiga dakinta,tayi kwanciyar ta,tana hana kanta sake kuka akan sa.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (34)
***Wajen Yaya ta nufa dan tasan itace kai tsaye zata saka Baba ko ta hanashi. Ta kuma san ta yadda zata bullo mata ta daina ragawa Mama dan ta lura shirun ta yasa take ganin har yanzu tana da ikon taka ta. Bedroom din Yayan ta shiga ta sameta a kwance tana hutawa bayan ta idar da sallar walaha, tashi tayi zaune suka gaisa sannan tace magana tazo su yi
"Ina jinki Halima, mecece matsalar? Dan nasan dole akwai magana."
"Yaya dama akan maganar Jidda ce, ni a gani na tunda har Tariq ya dawo Jidda ya kamata ta tare a gidanta, dama taron bikin ake so ayi kuma ya nuna baya ra'ayi ni a ganina kawai ta tare shine mafi a'ala."
"Ni kaina nayi wannan tunanin kuma jiran Alhaji nake ya shigo, dan na ga alama dan ku bashi da ta ido sam, gwara su je chan su karata."
Dariya ta saka Yayan ta cigaba da bayani
"Al'muri da yake munafuki ne ai kinga yadda yake ko? Irin masu halin nan ke dai kawai ki kalle su, sun fi kowa iya shakiyanci."
"Yanzu ki barmun komai, a yau ba sai gobe ba zata tare, dan babu amfanin zaman."
"Allah ya kaimu Yaya, dama dai maganar kenan abun ya soma damuna."
"Ai dole, yarinya ma tayi hakuri ki bari zanyi maganin shi a yau din nan, sai kisa ta shirya duk abinda zatayi zuwa anjima."
"Toh bari naje Yaya, Allah ya kara girma."
"Amin kinji? Allah yayi albarka."
***Komawa tayi ta saka jiddah a gaba, da Safeera da ita suka taimaka mata ta hade koman ta waje daya, hannu bata saka ba ita a lallai ba in da zata tunda be san worth din ta ba, babu wadda tabi ta kanta musamman Safeera da tasan munafurci ne kawai ba har zuciyar, take maganar ba. Falo ta dawo tayi zaman ta, tana kissisima yadda zata kaya a zaman nasu, duk da kaso hamsin tana tsoron Mama amma kuma sauran kason na kwadaituwa da son zama dashi din.
Fitowa Safeera tayi ta sameta a falon suka cigaba da zama sai ga Isma'il ya kirata, dagawa tayi jidda tayi kamar bata gane da wanda suke waya ba, suka dan jima suna magana daga karshe ta kashe tana murmushi
"Ya Isma'il ne, kinsan ya kusa zuwa gida."
"Allah sarki, Allah ya taimaka."
"Amin, ni tunda tafiya zakiyi ma ai ba amfanin zama na, zan koma gidan Aunty Sajida kawai."
"Wai waye yace miki tafiya zan? Ki jira mana ki gani, nasan ba in da zanje."
"Toh zamu gani, yarinya gwara ma ki saka ranki tafiya dole."
"Idan nace ba zani ba ai babu me daukata. "
"Wallahi tsaf zai dauke ki din, tab!"
"Ke kika sani."
"Ke ma kin sani ai."
***Ran Mama ya kai karshe a baci, dawowar ta kenan daga wajen Yaaya da ta turo aka kirata ta fada mata yau matar Tariq zata tare, da k'yar ta amsa da toh ta taso tazo ta fadawa su Aunty Nafi, suka kuwa hau fanfata akan karta yarda.
Kiran TARIQ tayi be daga ba, sai ta kira Fauwaz shima sai da ta katse sannan ya biyo kiran tace masa ina Tariq yazo maza-maza, baya nan dan tun safe da ya fita training be dawo gidan ba, gidan sa ya wuce a chan yayi wanka ya shirya sannan ya koma bacci dan yasan idan be more baccin sa ba ya koma sai ya samu matsala, shiyasa har Maman ta kira be ji ba.
Sai da rana tayi sannan ya tashi ya dan sake gyara jikin sa sannan ya hau mota ya dawo gidan. Tun a hanya dama Fauwaz ya fada masa Mama tana neman sa, shiyasa yana zuwa part dinta ya wuce tana ganin sa tace ya shigo suka shige chan dakin ta in da babu kowa.
"So nake ka saki Jidda a yanzu ba sai anjima ba."
Kawai tace masa ko zama bata iya yi ba. Kallon ta yake hankalin sa a tashe, ta hade rai taki bari ko kad'an yaga saukin ta, kasa furta komai yayi, ya dinga kokarin tattaro kalaman bakin sa amma ya gaza furta su, idan har yace zai iya sakin Jidda yayi karya, duk da ba wai yana mata son da ba zai iya rabuwa da ita ba, amma ba zai zo ya samu matsala da iyayen sa akan ta ba, haka kuma ba zai taba so hakan ta shafi iyayen sa ba
"Mama dan Allah mu bari mubi komai a sannu, dan Allah "
"Babu wani bin komai a sannu, yau kwana nawa kaana min alkawari amma ka gaza cikawa sai bin yar karamar yarinya a baya kamar wanda aka gama dashi."
"Wai Maama waye yace bin ta nake?"
"Kasan ni yarinya ce ai, bansan me nake ba."
"Ba haka bane Mama."
"Toh naji, duk ba wannan ba, bana son zaman ku karkashin inuwa daya, dan haka sai ka sawaake mata tunda ka kasa samun mafita."
"Baba fa? Zai yi fushi dani sosai."
"Ka barni dashi kawai, kai dai kayi abinda nace, ba zan iya jure ganin ta a matsayin sirikata ba."
"Amma Mama, mesa kika tsaneta haka?"
"Tambaya ta kake?"
" A'ah, kawai dai naga kamar yayi yawa ne mama, kiyi hakuri dan Allah mubi komai a sannu, Dan Allah muyi wa Baba biyayya kar muzo muyi abinda zai bata masa suna shi yanzu da yake a idon duniya abu karami zaki ji ana yi dashi."
"Ba zan ba, akan yarinyar nan zan iya batawa da kowa, idan har jinin Halima ce zata auri jini na, na gwammace komai ya faru."
"Mah?"
"Idan har na isa da kai, ka rabu da ita."
"Menene laifin ta a gareki Mama?"
"Babu komai, ba abinda tayi min kawai bana son ta ne."
"Shikenan mama, zanyi abinda kike so, amma ina zuwa Dan Allah."
Fuskarta ce ta fadada da farin ciki, t
"Dan Allah da gaske kake?"
Daga mata kai yayi
"Toh madallah, ka gama min komai Allah yayi maka albarka."
"Amin Ya Allah."
Ya juya ya fita ita kuma ta koma wajen su Aunty Nafi zuciyar ta cike da farin cikin zata kuntata wa Auntyn dan dama tayi alwashin sai ta mata abinda zata dade tana jin ciwon sa.