← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 76

Sashe 4

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya sa kai ya cigaba da tafiya zuwa main part din, mota suka shiga Fauwaz ya bi bayan sa, ya sameshi har ya zauna a gefen Baban suna magana, Zama yayi shima ya gaishe da Baban dan shi kadai ya rage a falon duk sun shige ciki. Breakfast din sukayi a tare, sannan Baba yace Tariq yaje ya sauya zuwa manyan kaya, ba a san ransa ba ya chanja zuwa shadda dinkin rigar da kadan ta wuce guiwar sa, ya rike hular a hannu ya fito yana jin shi a takure.
   Cikin gidan ya shiga, ya bi corridor din da zai kaishi part din Antyn, ya shiga bakin sa dauke da sallama kasa-kasa. Su uku ne a zaune a falon, Saudah, Amira da Umaima. Fitar Mama ya basu damar biyo Saudan suka zauna suna janta da hira, Amira ta saka musu waka suna ji ya shigo, a rikice ta danne power botton din wayar ta kashe ta gaba daya, kallon ta yayi ,yayi kamar be ji komai ba, ya wuce ya zauna a cikin daya daga kujerun falon yana ciro wayar sa. A tare suka hada baki da Umaima suka gaishe shi, yayi kamar be ji ba, yana cigaba da danna wayar sa. Sum sum sum suka fice ya zama sai Jiddah kawai a falon

"Ke je ki kira min Anty."

Yace be ko dago ba, ta mike ta nufi dakin Antyn ta kwankwasa, daga ciki tace mata ehem alamun tana toilet, dawowa tayi ta tsaya daga bayan kujerar tace

"Tana bayan gida."

Dagowa yayi jin abinda ta fada, sai a lokacin ya ganta, fuskarta fiki fiki, yar firit kamar ka hureta ta fadi saboda rama, mamaki ya kamashi ganin ta

"Wacece ke?"

Yace yana kafe ta da ido, sosai ta duburburce ganin yadda ya kafe ta da ido, idanun sa manya sosai masu ban tsoro

"Na'am?"

Tace cikin hada kalmonin

"Who are you? Daga ina kika zo?"

Ya sake tambayar ta har lokacin kallon ta yake,be taba ganin ramammiya karmashashiyar yarinya irin ta ba, shi ya zata ma aljana ce, saboda tsabar rama har wani rami ne a fuskarta ya shiga ciki. Bata san amsar da zata bashi ba, sai kawai tayi shiru tana wasa da hannun ta. Anty ce ta fito a daidai lokacin

"A ah, Yaya boss yaushe ka shigo?"

"Ban dade ba, ina kwana?"

Yace yana dauke kansa dga kallon yarinyar

"Lafiya lou, baku tafi ba ashe."

"Eh Baba be gama shiryawa ba, shine nace bari na shigo mu gaisa,wacece wannan Anty?"

"Auw wai Jidda? Jiya na taho da ita yata ce, yar wana ce amma ta dawo hannu na da zama."

"Ok."  Kawai yace yana tabe bakin sa, sai ya mike

"Nima gobe zan koma in sha Allah, zan dade wannan karon har sai na kammala sannan zan dawo."

"Wai, Masha Allah, zamuyi kewa. Allah ya bada saa da nasarar abinda aka je nema."

"In sha Allah Amin."

Yace yana ficewa, d'aga murya tayi tace masa a dawo lafiya ya amsa daga chan ya karasa ficewa.

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

[11/25, 3:54 PM] Rano2: *Sanadin*

               *Labarina*

                     Free Page (4)

©®_Hafsat Rano_

** Tariq ne yake tuka motar Fauwaz na gefen sa,Baba a baya yana duba labarai a wayar sa jefi jefi suna hira da Fauwaz wanda shima rabin hankalin sa yana kan wayar sa yana duba wani pdf. Be fi sau biyu Tariq ya saka musu baki a hirar da suke ba har suka isa garin su Baban in da zasu dauko Hajiya Yaya
A kasan wata bishiya yayi faking kannen Baban dake zazzaune suna shan inuwa suka mike dukka suka yo wajen motar. Fauwaz ne ya bude ma Baba kofa ya matsa baya ya fito, ya shiga mika musu hannu suna gaisawa, kananan kuma suka russuna suna gaishe shi.

Cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, zuwa tsohon shashen Yayan kafin ta koma birni tun daga zuwa wani asibiti da tayi Baban yace tazo kenan, bata son birni sam amma babu yadda ta iya haka dai ta hakura bayan ya samu wasu daga cikin yan uwanta sun saka baki, duk da haka bata son zaman ta a cikin gidan sa dan ba wani shiri suke da Mama ba, ita Yaya dama bakin ta baya shiru bata gani bata tanka ba shiyasa tasu sam bata zo daya da Maman ba, tace Maman ta fiya isa da izza dan iyayenta wasu ne, shiyasa da Baba yazo mata da maganar auren Halima ta bada goyon baya dari bisa dari dan a ganin ta a lokacin ne zai auri daidai dashi.
Hayaniyar Yayan suka fara ji tana ta fada da sababi, muryar ta a sama sosai ta dage tana fada bilhakki da gaskiya, murmushi Baba yayi, ya girgiza kansa yayi sallama a tsakar gidan, muryar sa ta sakata yin shiru ta amsa sallamar tana jefar da sandar da yake hannun ta. Fuskar Tariq a hade dan shi ba kasafai ya fiya son hayaniya da shiga cikin mutane ba duk da Baba yana tirsasa masa shiga cikin yan uwan sa dan suna da matukar yawa, yanayin sa ne a hakan kamar Safiyya, su suko yo Mama dan itama bata cika son mutane ba sai wanda tayi mugun sabo dashi.
Shima kamar Maman ba shiri suke da Yayah ba, dan kullum yi masa korafi take bashi da sakin fuska, surutun ta shi yafi komai damun sa, dan idan ta fara magana baya jin ko hadiyar yawu tana yi. Fauwaz ne dan dakin ta da Amira, sune suka yo ta a surutu da kwashe kwashen mutane kowa nasu ne.
Tabarma ta dauko zata shinfida musu fauwaz ya karba ya tayata, ta zauna a gefen gadon ta suka gaisa da Baban sannan su Fauwaz din suka gaishe ta ta amsa tana ficewa taje ta kawo musu ruwa ta ajiye sannan tace

"Ashe zaku zo, na dauka fa sai wani satin wallahi, ban gama abubuwan da nake anan din ba."

"Menene baki gama ba Yaya?"

"Em.. em akwai wani biki na yar Hajara nan kasa damu, babu dadi ace ban tsaya an yi bikin dani ba."

"Ayya, sai a basu hakuri Yaya, kinga fa lokacin komawar ki wajen likita yayi har yana neman wucewa."

"A ah gaskia ba zaa basu hakuri ba, sai dai a bani gudunmawa me tsoka na bata, sai kuma ka aiko matar ka itama tazo ranar bikin da gudunmawar ta."

Tace tana yin kicin-kicin da fuska, murmushi Baba yayi yace

"An gama Yaya, sai kuma me?"

"Shikenan, sai mu tafi tun da kayi niyya, ni wallahi dan ba yadda zan ne, a kai mutum a ajiye shi waje daya haba!"

"Kiyi hakuri Yaya."

"Idan ban hakuri ba ya zanyi toh? Fatan dayafi karfin ka ai sai ka mayar dashi wasa."

Har Kawu Rabi'u ya kawo madara da kwan zabin da ya tafi karbo wa Baba bata daina sababi ba, magaanar ta kadai kake ji a dakin sai dai Baba yayi murmushi lokaci zuwa lokaci ya amsa mata, shi kam Tariq ji yake kamar ya fice amma yasan idan yayi haka zai gamu da fishin Baba, shiyasa ya hakura ya zauna kawai yana sauraron surutun ta wanda baki daya babu magaanar da za'a kama.
   Fita Baba yayi yace zai je waje ya zauna da yan uwan sa kafin Yayan ta gama shiryawa, yana fita Tariq da ya tabbatar ya kule yaja tsaki yana dafe kansa.

"Uwarka kake wa tsaki bani ba."

Tace tana hararar sa, kallon ta yayi idanun sa na yin kasa sosai yace

"Ni ba dake nake ba."

"Ko ma da wa kake, mutum sai kuncin tsiya ba yar fara'a haba.".

"Yaya Ya Tariq fa shine angon ki, ki dinga lallabashi."

Fauwaz yace yana kokarin sake rura wutar fadan, buga cinyar ta, tayi tana daga murya

"Allah ya kiyashe ni da aikin dana sani, na auri mutum irin wannan ai na kade har ganye na, matar sa ta shiga uku wallahi."

"Idan kun gama ni ina waje."

Yace yana mikewa, ta rakashi da Allah raka taki gona ya fice kawai ya bar Fauwaz yana kyalkyala dariya, da gaske dariya suke bashi musamman Tariq da ya kasa gane wasan Yayan irin wanda ake yi na tsakanin jika da kaka, da gaske yake daukar komai duk da ba kasafai ya fiya nuna fushin sa ba amma zaka ga sam baya sakewa da ire-iren wasannin.
   Shi ya taimaka mata ta karasa hada kayan ta sannan ya daukar mata jakar, suka fito ta dinga shiga waje-waje tana musu sallama tun yana bin ta har ya gaji yace yana mota. A kwance ya samu Tariq din ya kwantr da kujerar side din me zaman banza fuskarsa rufe da hular da ya saka, booth ya bude ya saka kayan Yayan sannan ya dawo ta side dinsa yayi masa magana, mikewa yayi ya fita ya bashi wajen ya koma mazaunin driver.

"Har yanzu ka kasa gane wace Yaya."

"Haka aka ce maka?"

"Ai naga kamar abun yana damunka, banda yawan maganar ta she's very nice and fun to be with, zatayi ta saka dariya ne."

"Ni kuma sai aka ce maka dariya nake so nayi ko? Bani da aikin yi sai dariya ko?"

"Ba haka nake nufi ba, yawwa gata nan ma ta fito, case closed."

Yace ya ja bakin sa yayi shiru.

"Ni zan bude kofar da kai ne kenan?"

"Afwan Hajiya Yaya, wane mutum ya bar sarauniya da bude kofa?"

Ya bude mata da sauri ya taimaka mata ta shiga, sannan ya rufe mata kofar.

"Ranki ya dade." Yace yana dariya

"Kafi oo sau dubu, Allah dai ya baka mata ta gari me hankali da sanin ya kamata kamar kai."

"Amin."

Yace yana cigaba da dariya, Baba ne yazo ya shiga motar kusa da Yaya, sannan suka sake sallama dasu Kawu Rabi'u, Tariq yaja motar suka fita daga kauyen.
Chapter 4 · 0% Book details