Sashe 10
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kinsan cewa rayuwa da mutuwa duk na Allah ne ko? Haka kinsan cewa bawa baya taba wuce kaddarar sa, kiyi hakuri, kiyi hakuri duk me rai mamaci ne."
"Dan Allah me ya faru?" Tace hannun ta na rawa
"Muhammad ne..."
Sai ta mike da sauri,
"Me ya same shi?"
"Zauna dan Allah." Yace yana riko hannun ta, kasa zama tayi ta hau girgiza masa kai
"Me ya same shi? Me ya sami d'ana."
"Ya fada a rijiya, Allah yayi masa rasuwa."
Kara ta kwalla da karfi,
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, shikenan an kashe min d'a."
Sai ta fashe da kuka me karfi, kukan da ya kai attention din Tariq kan wayar dake hannun sa yana kokarin zuba tea a cup,a kunne ya saka wayar da sauri yana sauraren abinda Maman take cewa
"Sai da na nuna bana so yaran nan su je, ka dage dole sai sun je, shikenan ta kashe min shi,an raba ni da d'ana, Wayyo Aallah na."
Riko ta Baba yayi, ta kwace tana matsawa baya, kamar zata zauce haka take ji, da sauri Tariq ya katse kiran sannan ya sake kira at the same time, Baba ne ya dauki wayar, ya daga
"Muhammad ne Allah yayi mishi rasuwa yanzu."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, rashin lafiya yayi?"
" A'ah, tsautsayi ne ya gamu dashi,ka kwantar da hankalin ka zan kira ka."
Sai ya kashe wayar, yayi saurin fita ya bi bayan Mama da ta fice da gudu tana kwala ma yaran kira. Da sauri Safiyya, Maryam da Umaima suka fito a kusan tare, Yaya dake part dinta itama ta fito a gigice, Safiyya ce ta rungume Maman da take kuka tana kiran ta kashe mata shi, kamar wadda zata zauce haka ta koma, duk suma suka saka kuka ganin Maman na kuka sosai, daka musu tsawa Baba yayi ganin sam sun maki sauraren sa, yana kokarin yayi magana amma suna kuka Maryam hadda kururuwa, shiru sukayi duk suka koma kuka kasa-kasa, yace su wuce zuwa falo, sannan ya juya, suka bi bayan sa banda Mama da ta tsaya a wajen, sai da Safiyya ta rike ta sannan suka koma ciki, duk suka zauna suna fuskar su a cikin kafafunsu suna kuka kasa kasa , Yaya ce kawai a zaune a kujera, Mama na daga kofa taki zama, Baban ma a tsaye yake ba zaka iya tantance yanayin halin da yake ciki ba, Muhammad yaro ne me matukar shiga rai, shiyasa ya shiga ransu sosai duk da karancin shekarun sa,
"Dukkan mu zamu mutu babu Wanda zai zauna a duniyar nan sai dai in har lokacin mu be yi ba, amma idan yayi dole ne mu tafi, babu kuma wanda ya isa ya hana, kowanne bawa da yadda Allah ya kaddaro masa SANADIN mutuwar sa, Muhammad lokacin sa ne yayi,ko yana gaban mu ne bamu isa mu hana ba wallahi, kukan ku ba zai dawo dashi ba kuma ba zai chanja komai ba sai ma sabawa Allah da kuke kokarin yi ta hanyar kin yarda da kaddara."
"Allah ya gafarta masa yasa me ceto ne."
Yaya tace a sanyaye ita kanta mutuwar ta kad'a ta, dan hawaye take yi duk da bata bude murya ba,
"Kiyi hakuri Aisha, kiyi masa addu'a kawai, idan Allah ya kaimu da asubah zamu tafi in sha Allah."
Daga haka ya juya da sauri ya bar falon,zaman dirshen Mama tayi a wajen ta cigaba da kuka me cin rai, zuciyar ta taki amince mata ba an shirya cutar mata da yara bane dama tun farko shiyasa bata amince da tafiyar ba, waya Safiyya ta dauka ta kira gidan su Maaman, cikin kankanin lokaci sai gasu sisters da brothers din Mama har da Hajiya Babba, babu wadda ta yarda a cikin su cewa lokacin Muhammad ne yayi, dukkan su sun tafi akan shiri ne, wasu ma gani suke Aunty ce ta jefa shi a rijiyar dan sun yarda babu abinda kishiya ba zata iya aikatawa akan yayan kishiyar ta ba. A gidan duk suka kwana Hajiya Babba kawai aka mayar gida zaa dawo da ita gobe, kusan duk basu rintsa ba.
Bangaren Aunty kuwa sosai jikinta ya rikice da mugun zazzabi, tun bayan da aka kaishi aka dawo ta tabbatar da gaske ya rasu ba mafarki take ba, bata san wanne kalar tunani mutane zasuyi akan ta ba amma ta tabbatar ba zata taba fita ba, me zata cewa Mama ta yarda da ita ne wai? Me kuma zata ce wa Baba da saurin yaran su yarda babu sakacin ta?
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Ta furta da karfi sai kuma ta fashe da kuka, rike ta Innar su Saude tayi tana bata Baki
"Kiyi hakuri, haka Allah ya kaddara babu makawa sai ya faru."
"Me zan ce wa duniya? Me zan fadawa mutane su yarda bani da hannu a ciki? Su yarda ba sakaci na bane? Me yasa wai ma ba Usman bane ya mutun?"
Da sauri ta rufe mata baki tana bata fuskar ta sosai
"Karki yi sabo wallahi."
"Astagfirullah."
Ta hau fada da sauri da sauri, jidda da Amira dake kusa dasu suka kara tsananta kukan su, har wani jaja-jaj fuskar jidda tayi saboda kuka, fuskar su ta daga sosai, su ya bi, Usman yace su dawo shi sai ya tsaya yace zai jira su,ya akayi har ya je wajen rijiyar ya fada babu wanda ya lura shine abinda yafi damun Baffa.
Gidan baki daya babu wanda ya rintsa saboda zulumi da tashin hankali, da asuba, Baba, Safwan da abokin Safwan Jamil, neighbors suke sai abokan Baba su biyu Alhaji Adamu da Malam Nura sai driver Baban suka dauki hanya, suka isa wajen 7 lokacin su Baffa sun fita har an shinfida tabarmi suna zazzaune cike da zulumin tashin hankalin da ya same su, tunda Baffa ya hango motar su Baban gabansa ya fadi, haka ya daure ya taro su, suka hadu suka zazzauna, gefen Baban Baffa ya zauna jikin sa a sanyaye, lura da yanayin Baban ya sakashi yin shiru dan da so yake yayi masa bayani amma sam Baban ya nuna babu bukatar hakan. Sun dan jima a zaune har rana ta fito sosai, sannan suke ce zasu tafi. Baffa ne ya nemi Baban ya shigo ciki su yi magana da aunty dan sosai take cikin wani hali, tashi yayi yabi bayan Baffan zuwa cikin gidan, suna zazzaune a tsakar gida da sauri Amira ta tashi tayi wajen Baban tana fashewa da kuka, rike hannun ta yayi be ce komai ba, ya isa gefen tabarmar da aka shinfida masa ya zauna sannan ya amsa gaisuwar matan dake wajen tare da Aunty duk suka tashi suka shiga ciki ya rage daga shi sai Aunty, kukan ta ne ya tsananta har ta gaza furta kalma daya ,yana jin ta be ce komai ba, har sai da ta dauki lokaci dan kanta ta rage ta shiga jan hanci.
"Kin gama?" Yace yana kallon ta, girgiza masa kai tayi da sauri
"Toh ya ishe ni haka, kin isa ki hana abinda ya faru ya faru ne? Ko kuma zaki iya chanja abinda Allah ya riga ya kaddara?"
Girgiza kanta tayi da sauri, ya gid'a kansa sannan yace
"Bana son shiririta, abinda ya riga ya faru ya faru, Allah ya jikan sa yasa ya huta, kar ku bata mana lokaci tare nake da mutane, ku fito mu wuce."
Yana fadan haka ya mike, ya fice daga gidan, jikinta a sanyaye ta tashi itama, taje suka dauko kayan su, suka fito Jiddah dauke da Usman ,Amira ta rike musu kayan, Iya Lami da tayi dawowar safe na tsaye daga gefen bayan gida ta zuba musu ido,tana hasashen yadda zaa kwashe da uwar d'an idan an koma, zata so ace da ita zaa yi tafiyar dan kawai taga yadda Halima zata wulakanta dan ta tabbatar ba za'a kwashe kalou ba dan ma mijin nasu babban mutum ne me dattako.
Sallama sukayi mata,ita da Innar su Saude da sauran matan, ta amsa kamar ta damu da abinda ya faru, ta rakasu har zaure tana bawa Auntyn baki, babu wanda ya kulata suka fice dan kowa ya riga ya san karya take kawai dai dan kar ace bata yi bane. Motar da Fauwaz da Jamil da Driver suka shigo ita su Auntyn suka shiga sai Jamil ya koma wajen su Baba ya zauna a gaba. Baffa na tsaye da sauran mutanen unguwar, sai matan dake mammakale a katanga, daga musu hannu su Baffa sukayi sanda aka tada motar, idanun sa akan Jiddah da itama shi take kallo, har suka bar unguwar tasu. Ajiyar zuciya Baffa ya sauke yana fatan komai yazo wa Haliman da sauki dan ya hangi tashin hankali shinfide acikin kwayar idanun ta, ya kuma san abinda take gudu da tsoro wanda har ya haifar mata da zazzafan zazzabi wanda baya raba daya biyu daga jiya zuwa yau Jinin ta yayi mugun hawa.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (9)
"Dan Allah me ya faru?" Tace hannun ta na rawa
"Muhammad ne..."
Sai ta mike da sauri,
"Me ya same shi?"
"Zauna dan Allah." Yace yana riko hannun ta, kasa zama tayi ta hau girgiza masa kai
"Me ya same shi? Me ya sami d'ana."
"Ya fada a rijiya, Allah yayi masa rasuwa."
Kara ta kwalla da karfi,
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, shikenan an kashe min d'a."
Sai ta fashe da kuka me karfi, kukan da ya kai attention din Tariq kan wayar dake hannun sa yana kokarin zuba tea a cup,a kunne ya saka wayar da sauri yana sauraren abinda Maman take cewa
"Sai da na nuna bana so yaran nan su je, ka dage dole sai sun je, shikenan ta kashe min shi,an raba ni da d'ana, Wayyo Aallah na."
Riko ta Baba yayi, ta kwace tana matsawa baya, kamar zata zauce haka take ji, da sauri Tariq ya katse kiran sannan ya sake kira at the same time, Baba ne ya dauki wayar, ya daga
"Muhammad ne Allah yayi mishi rasuwa yanzu."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, rashin lafiya yayi?"
" A'ah, tsautsayi ne ya gamu dashi,ka kwantar da hankalin ka zan kira ka."
Sai ya kashe wayar, yayi saurin fita ya bi bayan Mama da ta fice da gudu tana kwala ma yaran kira. Da sauri Safiyya, Maryam da Umaima suka fito a kusan tare, Yaya dake part dinta itama ta fito a gigice, Safiyya ce ta rungume Maman da take kuka tana kiran ta kashe mata shi, kamar wadda zata zauce haka ta koma, duk suma suka saka kuka ganin Maman na kuka sosai, daka musu tsawa Baba yayi ganin sam sun maki sauraren sa, yana kokarin yayi magana amma suna kuka Maryam hadda kururuwa, shiru sukayi duk suka koma kuka kasa-kasa, yace su wuce zuwa falo, sannan ya juya, suka bi bayan sa banda Mama da ta tsaya a wajen, sai da Safiyya ta rike ta sannan suka koma ciki, duk suka zauna suna fuskar su a cikin kafafunsu suna kuka kasa kasa , Yaya ce kawai a zaune a kujera, Mama na daga kofa taki zama, Baban ma a tsaye yake ba zaka iya tantance yanayin halin da yake ciki ba, Muhammad yaro ne me matukar shiga rai, shiyasa ya shiga ransu sosai duk da karancin shekarun sa,
"Dukkan mu zamu mutu babu Wanda zai zauna a duniyar nan sai dai in har lokacin mu be yi ba, amma idan yayi dole ne mu tafi, babu kuma wanda ya isa ya hana, kowanne bawa da yadda Allah ya kaddaro masa SANADIN mutuwar sa, Muhammad lokacin sa ne yayi,ko yana gaban mu ne bamu isa mu hana ba wallahi, kukan ku ba zai dawo dashi ba kuma ba zai chanja komai ba sai ma sabawa Allah da kuke kokarin yi ta hanyar kin yarda da kaddara."
"Allah ya gafarta masa yasa me ceto ne."
Yaya tace a sanyaye ita kanta mutuwar ta kad'a ta, dan hawaye take yi duk da bata bude murya ba,
"Kiyi hakuri Aisha, kiyi masa addu'a kawai, idan Allah ya kaimu da asubah zamu tafi in sha Allah."
Daga haka ya juya da sauri ya bar falon,zaman dirshen Mama tayi a wajen ta cigaba da kuka me cin rai, zuciyar ta taki amince mata ba an shirya cutar mata da yara bane dama tun farko shiyasa bata amince da tafiyar ba, waya Safiyya ta dauka ta kira gidan su Maaman, cikin kankanin lokaci sai gasu sisters da brothers din Mama har da Hajiya Babba, babu wadda ta yarda a cikin su cewa lokacin Muhammad ne yayi, dukkan su sun tafi akan shiri ne, wasu ma gani suke Aunty ce ta jefa shi a rijiyar dan sun yarda babu abinda kishiya ba zata iya aikatawa akan yayan kishiyar ta ba. A gidan duk suka kwana Hajiya Babba kawai aka mayar gida zaa dawo da ita gobe, kusan duk basu rintsa ba.
Bangaren Aunty kuwa sosai jikinta ya rikice da mugun zazzabi, tun bayan da aka kaishi aka dawo ta tabbatar da gaske ya rasu ba mafarki take ba, bata san wanne kalar tunani mutane zasuyi akan ta ba amma ta tabbatar ba zata taba fita ba, me zata cewa Mama ta yarda da ita ne wai? Me kuma zata ce wa Baba da saurin yaran su yarda babu sakacin ta?
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Ta furta da karfi sai kuma ta fashe da kuka, rike ta Innar su Saude tayi tana bata Baki
"Kiyi hakuri, haka Allah ya kaddara babu makawa sai ya faru."
"Me zan ce wa duniya? Me zan fadawa mutane su yarda bani da hannu a ciki? Su yarda ba sakaci na bane? Me yasa wai ma ba Usman bane ya mutun?"
Da sauri ta rufe mata baki tana bata fuskar ta sosai
"Karki yi sabo wallahi."
"Astagfirullah."
Ta hau fada da sauri da sauri, jidda da Amira dake kusa dasu suka kara tsananta kukan su, har wani jaja-jaj fuskar jidda tayi saboda kuka, fuskar su ta daga sosai, su ya bi, Usman yace su dawo shi sai ya tsaya yace zai jira su,ya akayi har ya je wajen rijiyar ya fada babu wanda ya lura shine abinda yafi damun Baffa.
Gidan baki daya babu wanda ya rintsa saboda zulumi da tashin hankali, da asuba, Baba, Safwan da abokin Safwan Jamil, neighbors suke sai abokan Baba su biyu Alhaji Adamu da Malam Nura sai driver Baban suka dauki hanya, suka isa wajen 7 lokacin su Baffa sun fita har an shinfida tabarmi suna zazzaune cike da zulumin tashin hankalin da ya same su, tunda Baffa ya hango motar su Baban gabansa ya fadi, haka ya daure ya taro su, suka hadu suka zazzauna, gefen Baban Baffa ya zauna jikin sa a sanyaye, lura da yanayin Baban ya sakashi yin shiru dan da so yake yayi masa bayani amma sam Baban ya nuna babu bukatar hakan. Sun dan jima a zaune har rana ta fito sosai, sannan suke ce zasu tafi. Baffa ne ya nemi Baban ya shigo ciki su yi magana da aunty dan sosai take cikin wani hali, tashi yayi yabi bayan Baffan zuwa cikin gidan, suna zazzaune a tsakar gida da sauri Amira ta tashi tayi wajen Baban tana fashewa da kuka, rike hannun ta yayi be ce komai ba, ya isa gefen tabarmar da aka shinfida masa ya zauna sannan ya amsa gaisuwar matan dake wajen tare da Aunty duk suka tashi suka shiga ciki ya rage daga shi sai Aunty, kukan ta ne ya tsananta har ta gaza furta kalma daya ,yana jin ta be ce komai ba, har sai da ta dauki lokaci dan kanta ta rage ta shiga jan hanci.
"Kin gama?" Yace yana kallon ta, girgiza masa kai tayi da sauri
"Toh ya ishe ni haka, kin isa ki hana abinda ya faru ya faru ne? Ko kuma zaki iya chanja abinda Allah ya riga ya kaddara?"
Girgiza kanta tayi da sauri, ya gid'a kansa sannan yace
"Bana son shiririta, abinda ya riga ya faru ya faru, Allah ya jikan sa yasa ya huta, kar ku bata mana lokaci tare nake da mutane, ku fito mu wuce."
Yana fadan haka ya mike, ya fice daga gidan, jikinta a sanyaye ta tashi itama, taje suka dauko kayan su, suka fito Jiddah dauke da Usman ,Amira ta rike musu kayan, Iya Lami da tayi dawowar safe na tsaye daga gefen bayan gida ta zuba musu ido,tana hasashen yadda zaa kwashe da uwar d'an idan an koma, zata so ace da ita zaa yi tafiyar dan kawai taga yadda Halima zata wulakanta dan ta tabbatar ba za'a kwashe kalou ba dan ma mijin nasu babban mutum ne me dattako.
Sallama sukayi mata,ita da Innar su Saude da sauran matan, ta amsa kamar ta damu da abinda ya faru, ta rakasu har zaure tana bawa Auntyn baki, babu wanda ya kulata suka fice dan kowa ya riga ya san karya take kawai dai dan kar ace bata yi bane. Motar da Fauwaz da Jamil da Driver suka shigo ita su Auntyn suka shiga sai Jamil ya koma wajen su Baba ya zauna a gaba. Baffa na tsaye da sauran mutanen unguwar, sai matan dake mammakale a katanga, daga musu hannu su Baffa sukayi sanda aka tada motar, idanun sa akan Jiddah da itama shi take kallo, har suka bar unguwar tasu. Ajiyar zuciya Baffa ya sauke yana fatan komai yazo wa Haliman da sauki dan ya hangi tashin hankali shinfide acikin kwayar idanun ta, ya kuma san abinda take gudu da tsoro wanda har ya haifar mata da zazzafan zazzabi wanda baya raba daya biyu daga jiya zuwa yau Jinin ta yayi mugun hawa.
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*
*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*
*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*
😄😄😄😄😄😄😄
*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*
*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*
INAYA(riba biyu)___mamughee
SANADIN LABARINA___Rano
BABU SO___Billynabdul
FARHATUL K'ALB___Miss xoxo
GURBIN IDO____Huguma
*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*
*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*
Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300
*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank
*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902
*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107
*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (9)