Sashe 38
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Folding hannun sa yayi yana kallon ikon Allah, ta sauka daga motar tayi gaba. Da sauri ya fito daidai lokacin da wata mota ta haske ta, ya hango gashin kanta ta dan mayafin dake kanta da ba wani na kirki ba da wanda ya bayyanar da kusan gashin kanta, wasu maza sake kusa da ita suka kalle ta, da saurin sa cikin baci rai ya riko hannun ta, ya shiga janta zuwa motar, ya turata ya danna lock sannan ya koma ya shiga cikin motar, yaja suka bar wajen.
Kukan ta cigaba da yi masa, ransa ya sake baci sosai, ya dinga gudu sosai a titin ya dauke hanyar gidan, kanta na k'asa har suka karasa in da zasu, yayi parking sannan ya zura kansa baya ya bud'e ledar kayan da ya siyo dazu, ya dauko jacket din sa, ya zauna sosai sannan ya dora mata ita a saman bayan ta, dagowa tayi idanun ta da sukayi ja sosai ya kalla sai ya kauda kansa, ya shaki iska ya fezar da bakin sa, sannan ya juyo yana tamke fuskar sa sosai, ya dauki rigar ya bude ta, ya sa hannu ya janye mayafin dake jikin nata, ta kalle shi da sauri ya dalla mata harara ya shiga saka mata rigar akan doguwar rigar dake jikinta, ya balle botir biyu na jiki ya bar sauran, sannan ya dauki mayafin ya nannad'a mata akanta, ya sake zagayo dashi ya rufe kan nata, ya d'an ja baya ya kalle ta kad'an sannan ya zagaya ya fita ya bude mata.
"Fito." Yace yana kauda kansa gefe
Kallon wajen tayi, ta ki fitowa,
"Fito nace kafin ranki ya baci."
Yayi maganar still yana kallon gefe, share hawaye tayi, ta zuro kafafunta ta fito, ta tsaya a gaban sa, yar karama sosai akan sa, bata fi ya hadiye ta ba
"Strong head."
Ya furta sanda ta tsaya a gabansa kanta na k'asa. Hannun ta, ya kama cikin nasa, ya shiga takawa zuwa cikin building din, wanda yake dauke da tsirarun mutane saboda yadda lokacin ya dan fara ja, reception yaje ya karbi key ba tare da yace komai ba,suka haura sama ya ciro key ya saka a jikin kofar ya bud'e,suka shiga ciki ya maida kofar ya rufe. Guest house din Baba ne, anan yake saukar duk wasu bakin sa, daki ne babban gaske, me dauke da madaidacin gado, tv, fridge da yar madaidaciyar wardrobe. A jikin kofar taja ta tsaya,yayi gaba abin sa ya zauna a gefen gadon yana zaro wayar sa, tun dazu yake jin kiran amma yaki dagawa saboda baya son yin magana a yadda yake jin sa. Ta gefen idon sa ya kalleta tana tsaye a jikin kofar ya dauke kansa, yau sai ya kure ta duk miskilancin ta kuwa, kuma sai ya nuna mata shi din gaba yake da ita ba daidai suke ba, shiyasa ya fasa komawa dasu gidan, yaga yadda zatayi yasan dole a karshe ta magantu,daga nan sai ya maida ta din.
Tsawon lokaci tana tsaye a kofar har kafarta ta fara sagewa, kamar be san da ita a wajen ba yadda ya dinga sabgogin sa, zamewa tayi ta zauna kawai a wajen ta hada kanta da guiwar ta. Tashi yayi ya duba time yaga sha daya har ta kusa, sai ya shiga toilet ya dauro alwala yazo yayi akan dan madaidacin carpet din dake wajen, ya idar ya haye kan gadon ya kwanta bayan ya kashe hasken dakin ya zama sai kad'an
Dagowa tayi tana kallon wajen da yake a kwance, da gaske yake kenan ba zai maida ita gida ba, me zata ce wa aunty? Gashi bata fito da waya ba balle ta kira, tana nan a durkushe a wajen cikin zulumi gashi ta gaji da kukan da bata san ma'anar sa ba. Shiru tayi cikin tunanin me ya kamata tayi, sai kawai ta yanke daukar wayarsa ko text ne ta turawa aunty, duk da tasan kila Amira ta fada mata amma tasan dole zata damu da bata dawo ba, ita duk nauyi da kunyar Auntyn ma take ji amma dole sai ta kira ta ko text message. Tashi tayi sad'af-sad'af ta nufi wajen da yake kwance, dama a gefen sa ya ajiye wayar, ta kai hannun ta zata dauka ya damke hannun yana bud'e idon sa, suka had'a ido da sauri tace
"Aunty zan kira."
Kallon bakin ta yayi, yaki sakin hannun ta, ya jawota jikin sa gaba daya yana matse ta, ya shiga wajen kiran ya kira Aunty duk da bashi da tabbas din batayi bacci ba a lokacin, kira daya ta dauka kuwa, yayi sallama ta amsa
"Aunty afwan na tashe ki kina bacci."
"A ah ban ma kwanta ba Tariq."
"Ok dama wannan ce take so zatayi miki magana."
"Jidda wai, ba komai mayi magana da safe kawai."
Bata jira yayi magana ba ta kashe wayar,
"Kinga ni ko? Aunty ko yanka ki nayi na cinye ba zata ce min komai ba."
Ya rad'a mata a kunne, muskutawa tayi ya sake jawota yana hade ta da jikin sa.
"Ki yi bacci kawai dan ba tafiya zamuyi ba, ki barni zan samo solution yadda za'a yi, sai ki daina kuka dan an aura miki ni."
Daga haka be sake ce mata komai ba, ya rufe idonsa yana jin wani irin nutsuwa na saukar masa. Rufe idon ta, tayi kamshin turaren sa na cikata, tayi luf ko kwakkwaran motsi ta kasa yi, tana jin shi ya soma jan numfashi, alamun ya fara nisa a cikin baccin sa, kallon fuskar sa dinga yi, a hankali a hankali abinda take ji na rashin nutsuwa ya dinga gushewa, wata nutsuwa na maye gurbin sa.
***Idan tace ta san lokacin da bacci ya dauke ta, tayi karya, bacci tayi sosai irin wanda ta dade bata yi irin sa ba. Bangaren Tariq din ma haka ne, bacci yayi peacefully har yaso ya makara tashi. Shi ya fara farkawa ya dan janye jikin sa yana kallon fuskar ta, very cute da dan karamin lips dinta da ya dace da yar fuskarta. Duk da ta chanja masa sosai amma shi har yanzu kallon baby yake mata, dan a yanzun ma yar karama ya ganta a gabansa. Samun kansa yayi da yin murmushi ya tashi yaje yayi alwala yazo daidai saitin kanta ya shafa mata ruwan hannun sa a fuskar ta, da sauri ta bud'e idon ta, ta tashi zaune tana zazzare ido, tamke fuskar sa yayi, ya wuce gaba zuwa wajen da zai yi sallah, tashi tayi ta shiga toilet din tayi alwalar itama ta fito ta tsaya tana tunanin da abinda zatayi sallah dan mayafin kanta babu yadda za'a yi yayi sallah.
Yana zaune yana addu'a tunda ta fito, bata ce masa komai ba shima be ce mata ba, tana ta tsaye har ya gama ya taso yazo ya kwanta yana kulle idon sa
"Za.. n..yi.. sallah." Ta fada a rarrabe kamar me jin tsoro
"Yi mana." Yace still idanun sa na rufe
"Mayafi na ba zai ba."
"Kinsan ba zai sallah ba amma kika yafa kattin banza da wofi suna kallanki?"
Ya fada a hasale tunowa da abinda ya faru jiya
"A cikin gida ne ai."
"Cikin gidan babu Maza? Ko muharraman ki ne? Eh?"
Yace yana tashi zaune, shiru tayi ganin daga magana har ya harzuko, kwafa yai ya tashi ya fita ya sauka kasa, ya samo mata madaidacin mayafi a wajen ma'aikata wajen, ya kawo mata ta yafa a kasa tayi rolling da nata, sannan tayi sallar. Ta zauna a wajen har gari yayi haske sosai, yana ta baccin sa hankali kwance. Baki daya hankalin sa yayi gida, tana ta sake-sakn ko ta gudu ne sai gashi an kirashi, ya sa hannu ya kashe kiran aka sake kira a karo na biyu, sai da ya dan ja tsaki sannan ya daga yana kara wayar a kunne
"Hello..."
"Tariq kana ina ne wai?" Muryar Mama ta fito ta cikin wayar har tana juyowa daga in da take zaune, dan bude idon sa yayi ya murza kansa cikin yanayin baccin dake kansa yace
"Bana gidan Mah, anjima zan shigo."
"Da gaske ne kenan" tace gabanta na faduwa dan taji Amira da Fauwaz suna maganar kasa -kasa
"Me?"
"Ba komai, kazo gida kawai inason ganin ka."
"Shikenan, I'm on my way."
Ya katse kiran yana leko ta daga wajen da take zaune, ya d'an ya mutse fuska ya mike tayi saurin dauke kanta zuwa dayan side din, kamar be gani ba, ya shiga ya gyara jikin sa ya fito yace ta taso, da sauri ta mike har tana kusan bashi dariya.
***Mama na compound din zata fita Tariq din ya shigo, idon ta akan motar tana son gasgata abinda take gani, Jidda ce a zaune kusa dashi, jiri-jiri taji yana neman kayarda ita, kafin ma su gama parking tayi saurin shigewa ciki dan bata jin ko fitar zata iya a lokacin kuma.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (31)
ASSALAM ALAIKUM DEARIES
BARKAN KU DA KOKARI…. KAMAR
KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA
MUNA BARAR ROKON KU WAJEN
TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS
DAKE MANHAJAR YOUTUBE
YARO NE DAYA TASHI DA SON
KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE
KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN
SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A
TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE.
A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A
TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM
ALLAH KHAIRAN AS YOU DO... "
Assalamualaikum dear sisters and
brothers.
Welcome to ummu sudais YouTube
channels?
A channel where the Holv Quran is been
recited from different Angles.
Click on this link and listen to the
Beautiful recitation that will melt your
heart
https://youtu.be/Lafgc749sK8
Your subscription to our channel is of
Great important. Please help us grow
our channel by subscribing and liking
****
Da sauri ta bud'e motar ta fice ya tsaya yana kallon ta, hadda d'an gudun ta, ta bude kofa sai ta waigo ta kalli wajen da yake, ta jujjuya bakin ta sannan ta shige da sauri, murmushi yayi ya rufe motar ya nufi bangaren Maman yana jin sa sakayau kamar wanda ya sauke wani baban nauyi dake kansa. A tsaye ya samu Maman tana kaiwa da komowa a tsakanin hadadden falon nata, tun kafin ya gama shigowa ta soma fada
"Ni zaka wulakanta Tariq? Ni?"
"Mama... Me ya faru?"
Kukan ta cigaba da yi masa, ransa ya sake baci sosai, ya dinga gudu sosai a titin ya dauke hanyar gidan, kanta na k'asa har suka karasa in da zasu, yayi parking sannan ya zura kansa baya ya bud'e ledar kayan da ya siyo dazu, ya dauko jacket din sa, ya zauna sosai sannan ya dora mata ita a saman bayan ta, dagowa tayi idanun ta da sukayi ja sosai ya kalla sai ya kauda kansa, ya shaki iska ya fezar da bakin sa, sannan ya juyo yana tamke fuskar sa sosai, ya dauki rigar ya bude ta, ya sa hannu ya janye mayafin dake jikin nata, ta kalle shi da sauri ya dalla mata harara ya shiga saka mata rigar akan doguwar rigar dake jikinta, ya balle botir biyu na jiki ya bar sauran, sannan ya dauki mayafin ya nannad'a mata akanta, ya sake zagayo dashi ya rufe kan nata, ya d'an ja baya ya kalle ta kad'an sannan ya zagaya ya fita ya bude mata.
"Fito." Yace yana kauda kansa gefe
Kallon wajen tayi, ta ki fitowa,
"Fito nace kafin ranki ya baci."
Yayi maganar still yana kallon gefe, share hawaye tayi, ta zuro kafafunta ta fito, ta tsaya a gaban sa, yar karama sosai akan sa, bata fi ya hadiye ta ba
"Strong head."
Ya furta sanda ta tsaya a gabansa kanta na k'asa. Hannun ta, ya kama cikin nasa, ya shiga takawa zuwa cikin building din, wanda yake dauke da tsirarun mutane saboda yadda lokacin ya dan fara ja, reception yaje ya karbi key ba tare da yace komai ba,suka haura sama ya ciro key ya saka a jikin kofar ya bud'e,suka shiga ciki ya maida kofar ya rufe. Guest house din Baba ne, anan yake saukar duk wasu bakin sa, daki ne babban gaske, me dauke da madaidacin gado, tv, fridge da yar madaidaciyar wardrobe. A jikin kofar taja ta tsaya,yayi gaba abin sa ya zauna a gefen gadon yana zaro wayar sa, tun dazu yake jin kiran amma yaki dagawa saboda baya son yin magana a yadda yake jin sa. Ta gefen idon sa ya kalleta tana tsaye a jikin kofar ya dauke kansa, yau sai ya kure ta duk miskilancin ta kuwa, kuma sai ya nuna mata shi din gaba yake da ita ba daidai suke ba, shiyasa ya fasa komawa dasu gidan, yaga yadda zatayi yasan dole a karshe ta magantu,daga nan sai ya maida ta din.
Tsawon lokaci tana tsaye a kofar har kafarta ta fara sagewa, kamar be san da ita a wajen ba yadda ya dinga sabgogin sa, zamewa tayi ta zauna kawai a wajen ta hada kanta da guiwar ta. Tashi yayi ya duba time yaga sha daya har ta kusa, sai ya shiga toilet ya dauro alwala yazo yayi akan dan madaidacin carpet din dake wajen, ya idar ya haye kan gadon ya kwanta bayan ya kashe hasken dakin ya zama sai kad'an
Dagowa tayi tana kallon wajen da yake a kwance, da gaske yake kenan ba zai maida ita gida ba, me zata ce wa aunty? Gashi bata fito da waya ba balle ta kira, tana nan a durkushe a wajen cikin zulumi gashi ta gaji da kukan da bata san ma'anar sa ba. Shiru tayi cikin tunanin me ya kamata tayi, sai kawai ta yanke daukar wayarsa ko text ne ta turawa aunty, duk da tasan kila Amira ta fada mata amma tasan dole zata damu da bata dawo ba, ita duk nauyi da kunyar Auntyn ma take ji amma dole sai ta kira ta ko text message. Tashi tayi sad'af-sad'af ta nufi wajen da yake kwance, dama a gefen sa ya ajiye wayar, ta kai hannun ta zata dauka ya damke hannun yana bud'e idon sa, suka had'a ido da sauri tace
"Aunty zan kira."
Kallon bakin ta yayi, yaki sakin hannun ta, ya jawota jikin sa gaba daya yana matse ta, ya shiga wajen kiran ya kira Aunty duk da bashi da tabbas din batayi bacci ba a lokacin, kira daya ta dauka kuwa, yayi sallama ta amsa
"Aunty afwan na tashe ki kina bacci."
"A ah ban ma kwanta ba Tariq."
"Ok dama wannan ce take so zatayi miki magana."
"Jidda wai, ba komai mayi magana da safe kawai."
Bata jira yayi magana ba ta kashe wayar,
"Kinga ni ko? Aunty ko yanka ki nayi na cinye ba zata ce min komai ba."
Ya rad'a mata a kunne, muskutawa tayi ya sake jawota yana hade ta da jikin sa.
"Ki yi bacci kawai dan ba tafiya zamuyi ba, ki barni zan samo solution yadda za'a yi, sai ki daina kuka dan an aura miki ni."
Daga haka be sake ce mata komai ba, ya rufe idonsa yana jin wani irin nutsuwa na saukar masa. Rufe idon ta, tayi kamshin turaren sa na cikata, tayi luf ko kwakkwaran motsi ta kasa yi, tana jin shi ya soma jan numfashi, alamun ya fara nisa a cikin baccin sa, kallon fuskar sa dinga yi, a hankali a hankali abinda take ji na rashin nutsuwa ya dinga gushewa, wata nutsuwa na maye gurbin sa.
***Idan tace ta san lokacin da bacci ya dauke ta, tayi karya, bacci tayi sosai irin wanda ta dade bata yi irin sa ba. Bangaren Tariq din ma haka ne, bacci yayi peacefully har yaso ya makara tashi. Shi ya fara farkawa ya dan janye jikin sa yana kallon fuskar ta, very cute da dan karamin lips dinta da ya dace da yar fuskarta. Duk da ta chanja masa sosai amma shi har yanzu kallon baby yake mata, dan a yanzun ma yar karama ya ganta a gabansa. Samun kansa yayi da yin murmushi ya tashi yaje yayi alwala yazo daidai saitin kanta ya shafa mata ruwan hannun sa a fuskar ta, da sauri ta bud'e idon ta, ta tashi zaune tana zazzare ido, tamke fuskar sa yayi, ya wuce gaba zuwa wajen da zai yi sallah, tashi tayi ta shiga toilet din tayi alwalar itama ta fito ta tsaya tana tunanin da abinda zatayi sallah dan mayafin kanta babu yadda za'a yi yayi sallah.
Yana zaune yana addu'a tunda ta fito, bata ce masa komai ba shima be ce mata ba, tana ta tsaye har ya gama ya taso yazo ya kwanta yana kulle idon sa
"Za.. n..yi.. sallah." Ta fada a rarrabe kamar me jin tsoro
"Yi mana." Yace still idanun sa na rufe
"Mayafi na ba zai ba."
"Kinsan ba zai sallah ba amma kika yafa kattin banza da wofi suna kallanki?"
Ya fada a hasale tunowa da abinda ya faru jiya
"A cikin gida ne ai."
"Cikin gidan babu Maza? Ko muharraman ki ne? Eh?"
Yace yana tashi zaune, shiru tayi ganin daga magana har ya harzuko, kwafa yai ya tashi ya fita ya sauka kasa, ya samo mata madaidacin mayafi a wajen ma'aikata wajen, ya kawo mata ta yafa a kasa tayi rolling da nata, sannan tayi sallar. Ta zauna a wajen har gari yayi haske sosai, yana ta baccin sa hankali kwance. Baki daya hankalin sa yayi gida, tana ta sake-sakn ko ta gudu ne sai gashi an kirashi, ya sa hannu ya kashe kiran aka sake kira a karo na biyu, sai da ya dan ja tsaki sannan ya daga yana kara wayar a kunne
"Hello..."
"Tariq kana ina ne wai?" Muryar Mama ta fito ta cikin wayar har tana juyowa daga in da take zaune, dan bude idon sa yayi ya murza kansa cikin yanayin baccin dake kansa yace
"Bana gidan Mah, anjima zan shigo."
"Da gaske ne kenan" tace gabanta na faduwa dan taji Amira da Fauwaz suna maganar kasa -kasa
"Me?"
"Ba komai, kazo gida kawai inason ganin ka."
"Shikenan, I'm on my way."
Ya katse kiran yana leko ta daga wajen da take zaune, ya d'an ya mutse fuska ya mike tayi saurin dauke kanta zuwa dayan side din, kamar be gani ba, ya shiga ya gyara jikin sa ya fito yace ta taso, da sauri ta mike har tana kusan bashi dariya.
***Mama na compound din zata fita Tariq din ya shigo, idon ta akan motar tana son gasgata abinda take gani, Jidda ce a zaune kusa dashi, jiri-jiri taji yana neman kayarda ita, kafin ma su gama parking tayi saurin shigewa ciki dan bata jin ko fitar zata iya a lokacin kuma.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (31)
ASSALAM ALAIKUM DEARIES
BARKAN KU DA KOKARI…. KAMAR
KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA
MUNA BARAR ROKON KU WAJEN
TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS
DAKE MANHAJAR YOUTUBE
YARO NE DAYA TASHI DA SON
KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE
KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN
SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A
TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE.
A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A
TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM
ALLAH KHAIRAN AS YOU DO... "
Assalamualaikum dear sisters and
brothers.
Welcome to ummu sudais YouTube
channels?
A channel where the Holv Quran is been
recited from different Angles.
Click on this link and listen to the
Beautiful recitation that will melt your
heart
https://youtu.be/Lafgc749sK8
Your subscription to our channel is of
Great important. Please help us grow
our channel by subscribing and liking
****
Da sauri ta bud'e motar ta fice ya tsaya yana kallon ta, hadda d'an gudun ta, ta bude kofa sai ta waigo ta kalli wajen da yake, ta jujjuya bakin ta sannan ta shige da sauri, murmushi yayi ya rufe motar ya nufi bangaren Maman yana jin sa sakayau kamar wanda ya sauke wani baban nauyi dake kansa. A tsaye ya samu Maman tana kaiwa da komowa a tsakanin hadadden falon nata, tun kafin ya gama shigowa ta soma fada
"Ni zaka wulakanta Tariq? Ni?"
"Mama... Me ya faru?"