Sashe 25
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***Baba na zaune a hadadden falon sa na ciki wanda ke cike da ababen more rayuwa, news yake kalla hankalin sa baki daya yana kai har wayar sa ta gama ringing sam be ji ba. Mama ce tazo ta zauna a kubin sa, cikn shigar alfarma kamar ko da yaushe, kamshin turaren ta ya cika ilahirin falon. Dan juyowa yayi ya dube ta, yayi murmushi kawai itama ta maida masa ya cigaba da kallon news din har zuwa sanda aka gama, juyowa yayi ya dauki wayar sa zai yi kira sai yaga missed calls din Tariq, kwana wajen biyu kenan basuyi magana ba, yana taso ya kirashi dama yaji progress din training din nasa dan baki daya yayi dedicating lokacin sa akan son yayi achieving hours din nan, yawanci ma yanzu ya fiyi saboda yanayin busy din da yake shiyasa ya tsirga sosai duk da giant ne a tsaye yake amma hatta idanun sa sun fada saboda rashin isashen lokacin da baya samu. Ko waya ma da Baba kawai sukeyi shima kuma duk maganar akan training din nasa ne sai jefi-jefi yake kiran Mama ko ta kirashi yaga missed call ya kirata idan yana free. Yanzu ma fitowar sa kenan daga cikin wajen yana cike da farin cikin akwai yiwuwar in less than a year da ta rage masa sai iya hada hours din, shiyasa ya cika da murna ya kira Baba dan ya fada masa amma kuma be dauka ba. Cigaba da tafiya yayi zuwa in dai zai hau train dan yau akwai in da zashi ba kai tsaye gida zai koma ba, yana so yaje yayi siyayya kafin a shiga cikin sati ya zama so busy ya kasa siyan abubuwan da bashi dasu. Kiran Baban ne ya shigo, ya daga yana rataya rigar sanyin dake rike da a hannun sa a saman kafadar sa, suka gaisa ya tambaye shi yadda ake ciki, ya sanar masa da duk progress din da aka samu, yayi masa murna sannan yace yana so ya nemi alfarma a wajen sa
"Inaso nayi maka wani katsalandan a rayuwar ka, duk da bazan fada maka ko menene ba, amma ina neman amincewar ka, idan har ka amince shikenan, ina me tabbatar maka da ba zakayi nadama ba."
"Baba... Akwai abinda dama zakayi min da har sai an nemi amincewa ta?"
"Eh."
"Toh na amince Baba, iyaye ba zasu taba yin abu dan su cutar da dansu ba, sai dan su faranta masa, I can't wait na dawo nazo naga ko menene."
"Masha Allah, thanks for trusting me, ba zaka taba dana sani ba, ka kula da kanka kaji? Sai munyi magana Allah yayi maka albarka."
"Amin ya Allah."
Yace yana jin dadi a duk lokacin da Baba ya saka masa albarka shiyasa yake yawan koyi da Baban dan halayen sa ababen koyi ne.
Farin cikin sa ne ya karu bayan gama wayar, yana fatan ko menene Baban zai masa ya zame masa alkhairi a rayuwar sa.
Duk abubuwan da yake bukata ya siyo ya dawo ya samu Ishaq yana kokarin knocking a kofar sa, sai gashi yazo, ya matsa ya bud'e masa ya shiga bayan ya rage mishi kayan dake hannun sa
"Tuzuru ai na dauka ka dawo tun dazu ganin yau Friday da wuri kake dawowa."
"Naje African market ne, na samo yan kayayyaki, dawowa ta kenan."
"Ok naga alama ai, kaga da ka yarda kayi wuf da Yasmin duk wannan wahalar ba zaka sha ba, kuma ka samu cook."
"Don't mention her name please."
"Wai dai na tuna maka, kasan fa tana nan tana zaman jiran ka, wallahi da zaka yarda ko? Da har azumin nan sai ka daina shi, dama duk munsan dalilin azumin katon gauro kamar ka."
Da sauri ya kalle shi, ya ajiye pack din pepper din da ya fito dashi yana maida hankalin sa wajen sa
"Menene reason din fasting dina?"
"Waye be sani ba, oga rashin aure ne zaka wani fake da busy busy baka samu kaci abinci."
"Dan iska." Yace ya jefe shi da wani babban carrot, chafe wa yayi yaje wajen sink ya wanke yazo ya hau ci yana kyalkyalawa Tariq din dariya, murmushi kawai shima yake dan yasan maganar Ishaq din da kamshin gaskiya amma baya so yayi convincing kansa akan haka ne, dan be gama shiryawa aure yanzu ba, be ma fara neman matar da zai aura ba.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (20)
***Yana ajiye wayar Mama da take kallon sa tace
"Me ake shiryawa ba'a sanar dani ba?"
Murmushi ya sakar mata dan yana kyautata zaton idan ya fada mata zata iya bori ta tada hankalin kowa shi kansa Tariq din ta tayar masa da nasa
"Wannan tsakanin uba da dansa ne."
"Inyee, haka ne dama honourable?"
"Toh idan kuna sirrin ku ke da yan matan ki ina sani ne?"
"Ai shikenan, zamuji ai idan tayi tsami."
"Ba ma zatayi ba in sha Allah."
"Shikenan."
Tace tana hasaso kila gida ne Babba Baban ya samawa Tariq din ko dai wani abun babba.
Waya ya shiga yi ba kakkautawa, hakan ya saka Maman zamewa ta barshi shi kadai,ta koma dakin ta, ta dauki wayarta ta kira Aunty Mimi sukayi magana sannan ta fito ta nufi part din girls din nata, ta samesu kowacce tana zaune da waya ana fama, Maryam na karanta novel a arewabooks, ita kuma Umaima tana kan tiktok tana more kallo, Safiyya na waya da saurayin ta Dr sufyan (urologists ne). Sai jidda tana buga game din candy crush a sabuwar wayarta, shigowar Maman ya sakasu duk maida hankalin su kanta,kowa ya ajiye waya ta zauna tare dasu suka kunna TV suna kalla. Kusan 30min ta dauka a part din nasu, sannan ta tashi ta tafi, haka take musu kullum musamman idan Baba be shigo gida da wuri ba toh tana tare dasu har sai dare ya raba kafin ta tafi bangaren Baban.
***Duk yadda Isma'il yaso ya share amma ya kasa, ba sosai Jidda take hawa WhatsApp din ba ko yayi mata magana bata dubawa ma kwata-kwata, gashi ko kiran ta yayi sama-sama take amsa masa, shiryawa yayi kawai ya tafi gidan dan a kalla idan face-to-face ne zata saurare shi ko babu yawa, duk da yasan akwai yarinta a al'amarin ta, amma kuma ya san ta san komai, ya kamata ace ta bashi dama ko yaya ne.
Haka kawai taji sam beyi mata ba ko kad'an, dan kiran da yake mata ma ba karamin takura mata yake ba, ji take kamar ta kashe wayar ta hakura gaba daya, dan da tasan Safeera zata bashi number da bata ma fara kiran ta da number din ba. Jujjuya wayar take a hannu suna zaune su biyu ita da Aunty kowa da abinda ya dame shi, ta lura tun zuwan Baba Auntyn bata da walwala har ya koma,sai dai kuma bayan da ta fita ranar ta dawo sai ta sake ganin sauyi sosai a tattare da ita dan hatta kuzarin ta sai da ya ragu, gashi bata ce mata komai ba balle tasan abinda yake damun ta.
Knocking akayi a kofar, suka kalli juna ita da Aunty kafin ta tashi ta bud'e kofar,
"Hajiya tayi bako."
Sai ya juya Isma'il dake tsaye a bayan sa tun farko ya bayyana a gaban ta, da sauri ta janye kanta daga kofar cikin tafiyar sauri-sauri ta wuce falon zuwa bedroom dinta dan dan siririn mayafi ya saka ta yane kanta, jikinta sanye da riga me gajeren hannu da skirt. Tashi Aunty tayi ganin mutum a tsaye sai duk kunya ta kamata tace ya shigo ciki,ya shigo jikin sa a sanyaye, ya zauna sannan ya gaida Auntyn cike da girmamawa, ta amsa ranta duk babu dadi dan har ga Allah bata so Jidda ta rasa miji kamar Isma'il.
"Bari a kawo maka ruwa." Tace tana neman hanyar barin falon, dakatar da ita yayi ta hanyar cewa
"Aunty dan Allah a bar ruwan nan a koshe nake wallahi."
"Toh shikenan, ina zuwa."
Sai tabi bayan Jiddan, zuwa dakin Jiddan ta sameta a zaune a saman drawer ta zurma Hijab har k'asa fuskar ta babu fara'a ko kad'an, kallon ta Aunty tayi da ta gama gano bata son Isma'il din tun ranar farko tace
"Kije kuyi magana, dan Allah ki saki ranki, Usman zaizo ya zauna."
Dan sakin fuskar tayi, tayi gaba har ta fita Aunty ta kirata
"Kina ji? Baka wulakanta mutum ko baka sansa Jiddah,kokari za'a yi a rabu lafiya, duk tsiya mutumin da yace yana son ka ai ya gama maka komai a duniya , kuma be kamata ya zama makiyi a wajen ka ba."
Kara sakin fuskar tayi ta gid'a wa Aunty kai sannan tafita, maimakon ta tsaya a falon sai ta wuce shi ta fice ko kallon sa batayi ba, sai da taje ta riko hannun Usman sannan ta dawo falon, ta zaunar dashi a gefen ta, kanta a kasa ta gaishe shi,
"Lafiya lou." Yace duk ya gama tsorata da yanayin ta. Shiru tayi tana taba botir din jikin rigar Usman, har lokacin bata yarda ya dago ba bare har su hada ido, kamar wanda aka tsoma a cikin ruwan zafi haka yake jin sa, ga wata iriyar fargaba da faduwar gaba, shi be taba samun kansa a irin wannan yanayin ba, baya iya komai sai tunanin ta, haka duk abinda yake ita yake gani, amma kuma zuciyar sa ta soma karaya ganin irin tarbar da ya samu daga wajen Jiddan a yau bayan ba haka ya santa ba
"Jidda, maganar ranar nan ce tasa na sake dawowa, kinga ba zan hanaki karatun ki kawai dai inason a san dani ne, you can take all the time you want, ba zan taba magana ba, zan jira ki shiga university, idan ma har sai kin gama ne fine, zan iya jira."
Banza tayi masa dan bata tsinci komai a maganganun sa ba, ita ba dan karatun ta, take kin sa ba, shi so halitta ne, haka kawai taji bata son shi so na soyayya, tana dai respecting dinsa a matsayin shi na Yayan Safeera.
"Inaso nayi maka wani katsalandan a rayuwar ka, duk da bazan fada maka ko menene ba, amma ina neman amincewar ka, idan har ka amince shikenan, ina me tabbatar maka da ba zakayi nadama ba."
"Baba... Akwai abinda dama zakayi min da har sai an nemi amincewa ta?"
"Eh."
"Toh na amince Baba, iyaye ba zasu taba yin abu dan su cutar da dansu ba, sai dan su faranta masa, I can't wait na dawo nazo naga ko menene."
"Masha Allah, thanks for trusting me, ba zaka taba dana sani ba, ka kula da kanka kaji? Sai munyi magana Allah yayi maka albarka."
"Amin ya Allah."
Yace yana jin dadi a duk lokacin da Baba ya saka masa albarka shiyasa yake yawan koyi da Baban dan halayen sa ababen koyi ne.
Farin cikin sa ne ya karu bayan gama wayar, yana fatan ko menene Baban zai masa ya zame masa alkhairi a rayuwar sa.
Duk abubuwan da yake bukata ya siyo ya dawo ya samu Ishaq yana kokarin knocking a kofar sa, sai gashi yazo, ya matsa ya bud'e masa ya shiga bayan ya rage mishi kayan dake hannun sa
"Tuzuru ai na dauka ka dawo tun dazu ganin yau Friday da wuri kake dawowa."
"Naje African market ne, na samo yan kayayyaki, dawowa ta kenan."
"Ok naga alama ai, kaga da ka yarda kayi wuf da Yasmin duk wannan wahalar ba zaka sha ba, kuma ka samu cook."
"Don't mention her name please."
"Wai dai na tuna maka, kasan fa tana nan tana zaman jiran ka, wallahi da zaka yarda ko? Da har azumin nan sai ka daina shi, dama duk munsan dalilin azumin katon gauro kamar ka."
Da sauri ya kalle shi, ya ajiye pack din pepper din da ya fito dashi yana maida hankalin sa wajen sa
"Menene reason din fasting dina?"
"Waye be sani ba, oga rashin aure ne zaka wani fake da busy busy baka samu kaci abinci."
"Dan iska." Yace ya jefe shi da wani babban carrot, chafe wa yayi yaje wajen sink ya wanke yazo ya hau ci yana kyalkyalawa Tariq din dariya, murmushi kawai shima yake dan yasan maganar Ishaq din da kamshin gaskiya amma baya so yayi convincing kansa akan haka ne, dan be gama shiryawa aure yanzu ba, be ma fara neman matar da zai aura ba.
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (20)
***Yana ajiye wayar Mama da take kallon sa tace
"Me ake shiryawa ba'a sanar dani ba?"
Murmushi ya sakar mata dan yana kyautata zaton idan ya fada mata zata iya bori ta tada hankalin kowa shi kansa Tariq din ta tayar masa da nasa
"Wannan tsakanin uba da dansa ne."
"Inyee, haka ne dama honourable?"
"Toh idan kuna sirrin ku ke da yan matan ki ina sani ne?"
"Ai shikenan, zamuji ai idan tayi tsami."
"Ba ma zatayi ba in sha Allah."
"Shikenan."
Tace tana hasaso kila gida ne Babba Baban ya samawa Tariq din ko dai wani abun babba.
Waya ya shiga yi ba kakkautawa, hakan ya saka Maman zamewa ta barshi shi kadai,ta koma dakin ta, ta dauki wayarta ta kira Aunty Mimi sukayi magana sannan ta fito ta nufi part din girls din nata, ta samesu kowacce tana zaune da waya ana fama, Maryam na karanta novel a arewabooks, ita kuma Umaima tana kan tiktok tana more kallo, Safiyya na waya da saurayin ta Dr sufyan (urologists ne). Sai jidda tana buga game din candy crush a sabuwar wayarta, shigowar Maman ya sakasu duk maida hankalin su kanta,kowa ya ajiye waya ta zauna tare dasu suka kunna TV suna kalla. Kusan 30min ta dauka a part din nasu, sannan ta tashi ta tafi, haka take musu kullum musamman idan Baba be shigo gida da wuri ba toh tana tare dasu har sai dare ya raba kafin ta tafi bangaren Baban.
***Duk yadda Isma'il yaso ya share amma ya kasa, ba sosai Jidda take hawa WhatsApp din ba ko yayi mata magana bata dubawa ma kwata-kwata, gashi ko kiran ta yayi sama-sama take amsa masa, shiryawa yayi kawai ya tafi gidan dan a kalla idan face-to-face ne zata saurare shi ko babu yawa, duk da yasan akwai yarinta a al'amarin ta, amma kuma ya san ta san komai, ya kamata ace ta bashi dama ko yaya ne.
Haka kawai taji sam beyi mata ba ko kad'an, dan kiran da yake mata ma ba karamin takura mata yake ba, ji take kamar ta kashe wayar ta hakura gaba daya, dan da tasan Safeera zata bashi number da bata ma fara kiran ta da number din ba. Jujjuya wayar take a hannu suna zaune su biyu ita da Aunty kowa da abinda ya dame shi, ta lura tun zuwan Baba Auntyn bata da walwala har ya koma,sai dai kuma bayan da ta fita ranar ta dawo sai ta sake ganin sauyi sosai a tattare da ita dan hatta kuzarin ta sai da ya ragu, gashi bata ce mata komai ba balle tasan abinda yake damun ta.
Knocking akayi a kofar, suka kalli juna ita da Aunty kafin ta tashi ta bud'e kofar,
"Hajiya tayi bako."
Sai ya juya Isma'il dake tsaye a bayan sa tun farko ya bayyana a gaban ta, da sauri ta janye kanta daga kofar cikin tafiyar sauri-sauri ta wuce falon zuwa bedroom dinta dan dan siririn mayafi ya saka ta yane kanta, jikinta sanye da riga me gajeren hannu da skirt. Tashi Aunty tayi ganin mutum a tsaye sai duk kunya ta kamata tace ya shigo ciki,ya shigo jikin sa a sanyaye, ya zauna sannan ya gaida Auntyn cike da girmamawa, ta amsa ranta duk babu dadi dan har ga Allah bata so Jidda ta rasa miji kamar Isma'il.
"Bari a kawo maka ruwa." Tace tana neman hanyar barin falon, dakatar da ita yayi ta hanyar cewa
"Aunty dan Allah a bar ruwan nan a koshe nake wallahi."
"Toh shikenan, ina zuwa."
Sai tabi bayan Jiddan, zuwa dakin Jiddan ta sameta a zaune a saman drawer ta zurma Hijab har k'asa fuskar ta babu fara'a ko kad'an, kallon ta Aunty tayi da ta gama gano bata son Isma'il din tun ranar farko tace
"Kije kuyi magana, dan Allah ki saki ranki, Usman zaizo ya zauna."
Dan sakin fuskar tayi, tayi gaba har ta fita Aunty ta kirata
"Kina ji? Baka wulakanta mutum ko baka sansa Jiddah,kokari za'a yi a rabu lafiya, duk tsiya mutumin da yace yana son ka ai ya gama maka komai a duniya , kuma be kamata ya zama makiyi a wajen ka ba."
Kara sakin fuskar tayi ta gid'a wa Aunty kai sannan tafita, maimakon ta tsaya a falon sai ta wuce shi ta fice ko kallon sa batayi ba, sai da taje ta riko hannun Usman sannan ta dawo falon, ta zaunar dashi a gefen ta, kanta a kasa ta gaishe shi,
"Lafiya lou." Yace duk ya gama tsorata da yanayin ta. Shiru tayi tana taba botir din jikin rigar Usman, har lokacin bata yarda ya dago ba bare har su hada ido, kamar wanda aka tsoma a cikin ruwan zafi haka yake jin sa, ga wata iriyar fargaba da faduwar gaba, shi be taba samun kansa a irin wannan yanayin ba, baya iya komai sai tunanin ta, haka duk abinda yake ita yake gani, amma kuma zuciyar sa ta soma karaya ganin irin tarbar da ya samu daga wajen Jiddan a yau bayan ba haka ya santa ba
"Jidda, maganar ranar nan ce tasa na sake dawowa, kinga ba zan hanaki karatun ki kawai dai inason a san dani ne, you can take all the time you want, ba zan taba magana ba, zan jira ki shiga university, idan ma har sai kin gama ne fine, zan iya jira."
Banza tayi masa dan bata tsinci komai a maganganun sa ba, ita ba dan karatun ta, take kin sa ba, shi so halitta ne, haka kawai taji bata son shi so na soyayya, tana dai respecting dinsa a matsayin shi na Yayan Safeera.