← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 76

Sashe 76

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

***Kwana biyu da maganar tafiyar ya siya mata ticket ita kadai dan bazai samu damar zuwa ba kuma, duk bashi da walwala ganin haka yasa ta nuna murnar ta duk da itama a gefe daya bata san yadda zatayi coping idan babu shi ba, ya riga ya saba mata da caring dinsa haka dole zata sha famar rashin shi.
   Ana gobe zata tafi ya kanainaye ta dan tun magriba ya dawo gidan ya hanata sakat duk in da ta motsa yana manne da ita, ji yake kamar yace ya fasa aikin nasa kawai su tafi tare su koma gida suyi normal rayuwar su amma ya zai? Da k'yar ya barta ta karasa hada kayan da zata tafi dasu suka yi dinner yace bacci yake ji ta san sarai kuma ba wani bacci rigima ce irin tasa gashi ita yanzu sam bata san abinda yake so din amma shi kamar wanda aka kara ingizowa baya taba barin ta abu kad'an tayi sai yace tayi turning nashi on, haka dai take daurewa yanzun ma haka ta daure dai dan ta lura da duk take-taken sa zai iya canceling tafiyar yace sai wani lokacin shiyasa take ta lallabawa tana bin sa yadda yake so din.
   Ita ta fara tashi da safe bayan sun yi sallar asubah maimakon ya barta ta karasa abinda zata karasa kafin su tafi amma ya ki barin ta, ya rike ta kam yana tura kansa cikin rigarta wajen da tafi komai daukar hankalin sa yanzu a jikinta saboda yadda suka kara girma sosai. Bata hanashi ba duk da ta kai karshe amma haka ta taimaka masa ya samu abinda yake so sannan sukayi wanka tare suka shirya. Zai wajen azahar sannan suka fita zuwa airport din suna zuwa yayi mata duk abinda zai yi, ya rakata har cikin jirgin yana rik'e da ita, sai da ta zauna sosai tana kallon sa yayi hugging dinta so tight a hankali ya rad'a mata

"Ki kula min da kanki da babyna "

"In sha Allah."

"I love you so much Jidda nah."

"I love you too."

"Allah ya kiyaye, call me da kun isa dan Allah "

"I will, in sha Allah."

Tashi yayi ya juya ya fice ganin saura kadan jirgin ya tashi, yana tsaye daga gefen wajen jirgin ya soma tafiya a hankali a hankali har ya daga sama, ya sauke ajiyar zuciya yana komawa ciki dan shine zai dauki next passengers din da zasu tashi zuwa Manchester.

   ***Kasancewar ba wannan ne tafiyar farko ba sai taga dan saukin tafiyar duk da shima ta galabaita, san gefen ta akwai wasu couples da yaran su,su biyu kuma yan Nigeria ne sune ma suka zama kamar yan uwanta. Matar me suna Amrah da Mijinta Sultan (Abinda Ke Cikin Zuciya) sai yaran su biyu, sun burgeta sosai saboda yadda suka shaku da junan su kuma yadda sukeyi ita da mijin nata ya kara sa mata kaunar Ya Tariq dinta tana hasaso suma sun zama haka watarana. Exchanging contacts sukayi da matar daidai lokacin da suka iso filin jirgin na Abuja. Mama ce da kanta tazo daukar ta, tunda ta samu labarin cikin Jiddan take cike da matukar farin ciki, sun dade da shiryawa da Baba kuma tsakanin ta da Anty babu laifi kadaran kadahan Yaya ce dai take shan gata daidai gwargwado a wajen ta.
   Mamakin Jiddan ne ya dadu sanda suka fito taga Maman a tsaye tare da Amira da Usman suna jiran ta, da sauri Amira ta taho zata rungume ta Mama ta daka mata tsawa

"Baki da hankali ne? Baki ga halin da take ciki bane ba?"

Kunya ce ta kama Amiran ita kuma Jidda ta dinga dariya ta karaso ta russuna zata gaida Maman tace Maza Maza ta mike ba'a son me ciki da durkuso,tashi tayi a kunyace ta gaida Maman ta amsa tana kallon cikin nata.

***Rayuwa ce ta cigaba da garawa cikin ikon Allah har cikin Jidda ya shiga wata tara, an yi bikin su Amira Wanda Jidda ta zama itace akan komai dan hatta Mama ita ta barwa ragamar komai duk abinda zatayi sai ta nemi shawarar Jiddan wanda take cike da kaifin tunani hakan ya sa ta kara shiga zuciyar Maman sosai.
   Yaya ce tazo ta zauna da ita da k'yar sanda ta shiga wata takwas dan sai da Baba yasa baki sannan ta yarda tazo suka zauna. Waya suka gama kenan da Ya Tariq yace ta tashi ta fita ta dan zazzagaya gidan saboda tace masa bata jin dadin jikinsa. Yunkurawa tayi da nufin tashi taji wani abu ya soke ta da sauri ta durkusa ta kwala kiran Yaya.  Tare suka shigo da sabuwar me aikin ta da mama ta kawo mata bayan Godiya, da sauri ta fita tace a kunna mota dan har Jiddan ta kai kasa saboda wani irin murdawa da cikin ta yayi ga wani irin ciwon mara da ya taso mata gadangadan. Yaya ce ta riketa tana mata sannu, Godiya taje da sauri ta sau waya ta kira Aunty ta fada mata, sai ta aika Usman tace ya fadowa Mama aikowa mayafi kawai ta yafa ta fito, kafin taje sun wuce asibiti sai ta bisu chan din.
  Cikin ikon Allah ana zuwa ba'a fi minti talatin ba Jidda ta haihu haihuwa me sauki kuma lafiya lou dan ko karuwa batayi ba. Murna a wajen Mama tayi saurin kiran Anty t fada mata sannan ta kira Baba shi kuma ya kira Tariq yana tsaka da shirin tahowa dan ranar zai baro kasar sai ga kyakkyawan labari. Sujuduj shukur yayi yana kara godiya Allah da ya sauke ta lafiya.

Mace aka samu me kama daya sak da Jiddan har farin kamar dai yadda Tariq din kullum yake jaddada mata me kama da ita yake so. Nan da nan asibitin ya cika da su Anty, Amira, Ya Safiyya da babyn ta haka ma Umaima, Ya Fauwaz da matarsa. Maryam ce kawai bata nan tana Kano amma an kirata an fada mata. Baba ne yazo yaga sabuwar amaryar tasa wadda Yaya ta rike ta kam ta hana kowa sai dai Ka kalle ta a hannun ta, Baba kawai ta bari ya dauka shi da abokin sa amma daga su bata sake barin kowa ba. Kasancewar kalou aka haihu yasa basu kara awa daya ba aka sallame su. Gida aka wuce da ita part din Mama in da dama tun kafin haihuwar tasa aka gyara mata dakin dan so take ta kara wanke kanta a wajen Tariq din da Baba har ma da Jiddan.

***Tana zaune bayan anyi ma jarirriyar wanka yamma Mama tazo tace ta taso ruwa ya yi, tashi tayi ta dora towel a saman kanta ta shiga toilet din, Maman ce da kanta tayi mata wankan towel din ta gasa masa jikin ta sosai sannan ta nuna mata yadda zatayi tsarki sosai, ta fita ta barta taje ta kunna bunner a dakin sai ga Anty ta shigo ta dauki babyn ta fito da ita falon wajen bakin da akayi.
Farfesu me zafi aka kawo mata Maman da kanta tasa ta taci sosai sannan ta bata magungunan ta tace ta kwanta ta huta sosai ta fita ta jawo mata kofar dakin.
Ta dade sosai tana baccin cikin baccin taji kamar ana shafa mata fuskar ta, bud'e idon ta tayi dake cike da bacci ta ganshi yayi kneel down a gaban ta yana kallon ta cike da tsantsar tausayin ta. Da sauri ta tashi tana bude baki, sai ta rungume shi cike da farin cikin ganin sa

"Jidda nah!" Ya furta yana kara rungume ta sosai

"Thank you so much, nagode nagode nagode, kin gama min komai a duniyar nan da kika haifa min Princess dita."

Gefen ta, ta kalla jarirriyar na ajiye a kusa da ita tana bacci, ya dade da shigowa yana kallon su cike da so da kauna, ji yake kamar ya hadiye su saboda kauna.

"Kin ganta ko? Kamar ku daya har idon naki ne Baby."

"Haka nima nake?"

"Sosai."

"Amma kalli fingers dinta irin naka ne."

"Na gani Jidda, Allah kenan, Allah ya raya mana ita yayi mata albarka, I love you so much."

"I love you so so so much."

Ta maida masa tana sake hugging dinsa

"Kayi mata huduba?"

"Yes! Na saka mata Halimatussadiya."

"Da gaske?" Ta waro idon ta

"Da gaske, Anty ta chanchanci fiye da haka."

"Nagode nagode nagode mijina."

"Shssh, babu godiya a tsakanin mu, ina sonki sosai fiye da yadda nake son kai na, zan iya yin komai saboda farin cikin ki."

"Inason ka sosai, beyond words! Allah ya barmu tare har karshen rayuwar mu."

"Amin Ya Allah!"

"What next?" Yace yana bude hannun sa

"A very beautiful beginning in sha Allah."

"Zaa bude sabon chapter rayuwar Jidda da Tariq."

"In sha Allah."

Tace tana sake kwanciya a jikin sa.

ALHAMDULILLAH!!! TAMMAT!!!

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ 400
*(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ 400
*(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ 400
*(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ 400
*(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ 400
*(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 2k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_
*HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_
*_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_*
Chapter 76 · 0% Book details