Sashe 64
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ok bari na zo muje." Ya mike tayi saurin cewa
"Dan Allah kar muje tare."
"Why? Ke da babyn ki?"
"Ni dai dan Allah."
"Me yasa toh?"
"Kunya zaka sa ni ji."
Dariya yayi k'adan ya koma ya zauna
"Shikenan sai kin dawo."
Juyawa tayi ta fita shi kuma ya cigaba da zaman jiran Mama wadda ya baro su suna fafatawa da Baba akan abinda ya faru.
**Kaamar munafuka haka ta shiga wajen Yayan tana labewa, Sarai Yaya ta ganta amma ta maze ta tsuke fuskar ta tana yin kamar bata ga Jidda ba
"Assalamu alaikum." Tayi sallamar tana shiga gaba daya
"Amin." Yaya tace a gajarce
Kusa da ita Jiddan ta zauna ta kauda kanta gefe ta koma dayan gefen ta sake dauke kanta,
"Dan Allah Yaya kiyi hakuri."
"Da akayi me?"
"Komai ma, dan Allah wallahi ba laifi na bane Allah Yaya, dan Allah."
"Ba dai kin zabi miji ba? Ke dadi miji ko? Har kike rawar kai ki shige dakin miji da tsakar rana kiki fitowa ko?"
"Na shiga uku."
"Kiyi hakuri dan Allah."
"A ah ai ba komai, ba komai kinji? Masu hali irin Malam ma kaza aji ya ka cika bare kana bin su, ni da zan siyar miki kima da darajar wajen sa shine kika watsan k'asa a ido kika shige daki kukayi mukus ko? Dadi aure "
"Na shiga dari ma ba uku ba." Ya furta a hankali, sai kuma a fili tace
"Ba haka bane Yaya, kiyi hakuri ni dai dan Allah."
Noke kafardar ta, tayi
"Dan Allah Yayarmu, Hajiya Yaya ikon Allah, ki taimaka kiyi hakuri ko na zauna na fasa komawa."
"Ki zauna a ina?
"Anan."
"Kaji mukafukar yarinya, ni zaki ma kinibibi?"
"Da gaske Yaya."
"Wasa kike ko?"
"Da gaske mana."
"Toh ma hakura,."
"Ni idan bakya so sai nayi zamana anan din kawai."
"Nace miki na hakura, ba in da zaki zauna da ya wuce dakin mijinki, na bar maganar ma kwata-kwata, shikenan?"
"Toh shikenan Yaya, amma da..."
"A bar maganar, samo min yoghurt a firij na dan sha."
"Hajiya Yaya da cin dadi."
"Arzikin d'a, ke ma ki zage jiki ki zazzago su baka san wanda zai jikan ka ba."
"Nawa ma kikayi Yaya?"
"Sha hudu nayi."
"Wai!"
"Biyar ne suke raye a yanzu."
"Masha Allah."
"Haka mukayi haihuwar nan da wahala ma ba irin ta yanzu da gata yayi muku yawa ba, wai tsabar lalacewa wai da miji ake jego, mu zamanin mu ka isa? Ai kai da miji sai kayi arba'in har ba irin Malam masu bakin hali ba."
"Zamanin ne ya chanja Yaya."
"Ai na gani, sai a shige daka da miji a bar me zaman dabaro tana hamma da zare ido, yaran yanzu sam basu da ta ido wallahi."
"Zamanin ne fa Yaya."
"Ai sai ku karata ga ku nan gasu, shiyasa ni ba gidan wadda zanje zaman dabaro kin ganni nan, kowa ya karata chan."
"Uhum." Jidda tace tana hasaso yadda zata kaya idan akace wai itace da ciki ko zata haihu.
***Fada sosai Baban yake ya dauki waya ya kira Tariq yace ya dawo, dama cewa yayi ya basu waje zai kirashi, sai gashi nan ya shigo ya kalli Mama da take cikin tsananin tashin hankali, ta so ita ta fara sanar da Baba maganar tayi masa bayani yadda zai gane amma sai akaci rashin sa'a ya sani wanda bata san ta wajen wa ba, amma kuma yace text akayi masa shiyasa tayi tunanin Nafi ce ta tura masa text din, bata san haka zata mata ba, gashi ta kara sata a matsala dan Baba yace babu ruwan sa tunda har ta iya tura Yara gidan Tariq din duk da tasan rashin dacewar hakan shima kuma ba zai iya komai ba illa ya tursasawa Tariq din auren Salmar kamar yadda yace Maman na so tunda da bata so ba zata fara tura su ba, babu irin bayanin da batayi masa ba akan Nafi karya take amma fafur yaki yace dama ai ya gaya mata tun ba yau ba, ta fita daga harkar gidan Tariq amma taki, shikenan tunda har ta zabi hakan dama kuma bata son jidda sai ya auri Salman dan ya gaji da halin ta.
Gefen Baban Tariq ya zauna Baba ya kalle shi ya nuna sa da hannu sannan ya nuna Maman
"Ga uwar ka nan, tasan duk abinda yake faruwa saboda son zuciyar ta, ta jawo maka matsala da kanta, bani da abinda kuma zan yi akan wannan maganar dan ko zuwa sukayi suka fadawa duniya sun bata min suna, babu kuma wanda zai yarda da mu, duk da su kansu illa zasuyi wa kansu babba amma mutane basa gane hakan idan har suka rasa abun da suka kwalla fa rai akai basu samu ba, toh sai su yi kokarin shafa maka bakin penti, yanzu zamani ne na social media kuma duk abinda aka ce siyasa ta shigo zakayi kokarin kare mutuncin ka da martabar iyalin ka dan abu kad'an sunan ka zai karade ko ina, bani da niyyar tursasa maka aure a wannan lokacin, amma tunda har ban isa na saka ko na hana mahaifiyar ka ba, shikenan gata nan,kaje ka fara shirye-shiryen auren Salmar, idan yaso sai ka ajiye Hauwa'u a gida kaamar yadda take so, ka dauki matar da ta zaba maka ku tafi"
Da sauri Tariq ya dago kansa da yake duke, ya kalli Baban
"Sai ka fara shirye-shirye dan babu lokaci, abinda mahaifiyar ka take so ne, tunda ita Hauwa'u ba 'ya bace a wajen ta,amma ta sani, tana da 'yaya mata duk abinda kayi wa dan wani kaima sai anyi wa naka."
Kan Tariq a k'asa ya kasa motsawa dan be yi tunanin abinda Baban zai ce kenan ba, bayan yayi masa duk bayanin da zai masa kuma ya gamsu ya amince, amma kuma sai yaga Baban ya chanja baki daya kamar bashi ba, tashi Mama tayi dan tasan ko me zatayi ba zai saurare ta a lokacin ba, shiyasa kawai taga gwara ta fita zuwa sanda zai huce, sannan taje ta samu Nafi suyi duk wacce zasuyi dan wallahi da Tariq ya auri Salma gwara ta hakura da Jidda duk da bata son ta.
Yunkurawa Tariq yayi zai bi bayan Maman bayan yayi godiya a ciki ciki Baban ya dakatar dashi yace ya zauna, zama yayi ya tankwashe kafarsa
"Na kira wani a embassy, yace ku shiga gobe da safe, idan yaso daga chan sai ku wuce kanon."
"Na'am?"
"Eh, sannan akan maganar da mukayi yanzu..."
"Baba dan Allah kayi hakuri wallahi ba zan iya auren yarinyar nan ba."
"Na sani, kuma nima ba zan bari ka aure ta ba ,inaso mahaifiyar ku tayi hankali ne, ta ajiye duk makaman yakin ta,ta rungumi Jiddah dan idan aka tafi a haka ko 'yaya kukayi zata iya kin su, tunda tana kin uwarsu."
Ajiyar zuciya ya sauke me karfi wadda har sai da ya bawa Baban dariy
"Jairi, kannen ka mata ne suka sanar dani duk abinda yake faruwa tun ranar da uwata suka zo gidan, nayi shiru ne ina bibiyar komai,."
_"Ashe yaran nan suna da rana."_ yace a cikin zuciyar sa, godiya ya sake yiwa Baban yayi masa sallama ya fito ya wuce kai tsaye wajen aunty dan yasan anan zai tarar da ita
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (52)
***Abinci ta zuba ta zauna tana ci a k'asan carpet suna hira da Aunty sai gashi ya turo kofar ya shigo bakin sa dauke da sallama. A ciki ta amsa Anty kuma ta amsa a fili tana masa maraba. Yanayin da ya ganta a zaune sai ya tuna masa ita ranar da ya fara ganin ta da muryar ta kamar usur wuyanta kamar mirikin lema.
"Barka da rana Aunty."
"Barka dai Tariq, ya gida?"
"Alhamdulillah Aunty."
"Madallah, ya shirye-shiryen tafiyar?"
"Ana kan yi, Visa din Jiddah ce dama zata dan mana delay kad'an."
Ya karashe yana kallon fuskar ta, tunda ya shigo ta daina cin abincin da take ci yana lura da ita
"Masha Allah, toh Allah ya bada sa'a ya taimaka."
A yadda Antyn tayi maganar zaka gane cewa ba karamin farin ciki tayi ba da tafiyar Jiddan, abinda dama take ta hangowa kenan dan indai ya tsallake ya tafi shikenan kuma kashin ta ya bushe a wajen Mama da Nafi dan ta lura Nafin ce take sake zuga Mama akan Jidda,yanzu kuwa idan suka tafi ba shikenan ba?
"Bbyna..." Yayi maganar yadda aunty ba zata ji ba, dago kyawawan idanun ta tayi ta sauke su kansa, ya motsa bakin sa a hankali yace
Kin gama?"
Girgiza masa kai tayi ta cigaba da juya spoon din
"Ok, ki karasa sai mu tafi."
Gid'a masa kai tayi, yayi murmushi kad'an ya zare glasses din idon sa yace
"Aunty, gobe zamu je embassy daga nan zamu wuce Kano in sha Allah."
"Kai dama na biku kawai mu tafi wallahi."
"Aunty mu tafi kawai toh mana."
"A ah, babanku ma ba zai yarda ba, nima kuma tsokanar ku nake duk da inason zuwa din amma zan bari cikin next week in sha Allah."
"Toh Allah ya kaimu."
"Amin ya Allah.'
Mikewa Jidda tayi da plate din dan babu kuma in da abincin zai cigaba da shiga dan gaba daya ya hanata sakat da kallon shi duk da idon sa yana cikin bakin glass amma tsaf ta gano kallon ta yake kuma ta san shi sarai zai iya bata kunya a wajen auntyn dan shi kam babu ruwansa ko a jikin sa.
"Jidda dai wannan cin abincin na wasa me wallahi."
"Shiyasa bata kiba ai aunty."
"Aikuwa, a haka ma ai jiddah tayi kumari, sosai."
"Yanzun ma da sauran ta." Yace k'asa-k'asa amma sai da taji, ta juyo ta dan kalle shi ya motsa bakin sa yana mata murmushi ta shige kitchen din ta wanke bakin ta sannan ta fito ta wuce tsohon dakin ta, bin bayan ta aunty tayi suka barshi a zaune tana shiga ta zauna tace Jiddan ma ta zauna, rike da hisnul muslim dinta da counter sai yar jakar da sarka da abun kafar nan suke ciki da ta dauka a cikin kayan ta tazo ta zauna kusa da Auntyn
"Akwai abinda yake damun ki ne?"
"Dan Allah kar muje tare."
"Why? Ke da babyn ki?"
"Ni dai dan Allah."
"Me yasa toh?"
"Kunya zaka sa ni ji."
Dariya yayi k'adan ya koma ya zauna
"Shikenan sai kin dawo."
Juyawa tayi ta fita shi kuma ya cigaba da zaman jiran Mama wadda ya baro su suna fafatawa da Baba akan abinda ya faru.
**Kaamar munafuka haka ta shiga wajen Yayan tana labewa, Sarai Yaya ta ganta amma ta maze ta tsuke fuskar ta tana yin kamar bata ga Jidda ba
"Assalamu alaikum." Tayi sallamar tana shiga gaba daya
"Amin." Yaya tace a gajarce
Kusa da ita Jiddan ta zauna ta kauda kanta gefe ta koma dayan gefen ta sake dauke kanta,
"Dan Allah Yaya kiyi hakuri."
"Da akayi me?"
"Komai ma, dan Allah wallahi ba laifi na bane Allah Yaya, dan Allah."
"Ba dai kin zabi miji ba? Ke dadi miji ko? Har kike rawar kai ki shige dakin miji da tsakar rana kiki fitowa ko?"
"Na shiga uku."
"Kiyi hakuri dan Allah."
"A ah ai ba komai, ba komai kinji? Masu hali irin Malam ma kaza aji ya ka cika bare kana bin su, ni da zan siyar miki kima da darajar wajen sa shine kika watsan k'asa a ido kika shige daki kukayi mukus ko? Dadi aure "
"Na shiga dari ma ba uku ba." Ya furta a hankali, sai kuma a fili tace
"Ba haka bane Yaya, kiyi hakuri ni dai dan Allah."
Noke kafardar ta, tayi
"Dan Allah Yayarmu, Hajiya Yaya ikon Allah, ki taimaka kiyi hakuri ko na zauna na fasa komawa."
"Ki zauna a ina?
"Anan."
"Kaji mukafukar yarinya, ni zaki ma kinibibi?"
"Da gaske Yaya."
"Wasa kike ko?"
"Da gaske mana."
"Toh ma hakura,."
"Ni idan bakya so sai nayi zamana anan din kawai."
"Nace miki na hakura, ba in da zaki zauna da ya wuce dakin mijinki, na bar maganar ma kwata-kwata, shikenan?"
"Toh shikenan Yaya, amma da..."
"A bar maganar, samo min yoghurt a firij na dan sha."
"Hajiya Yaya da cin dadi."
"Arzikin d'a, ke ma ki zage jiki ki zazzago su baka san wanda zai jikan ka ba."
"Nawa ma kikayi Yaya?"
"Sha hudu nayi."
"Wai!"
"Biyar ne suke raye a yanzu."
"Masha Allah."
"Haka mukayi haihuwar nan da wahala ma ba irin ta yanzu da gata yayi muku yawa ba, wai tsabar lalacewa wai da miji ake jego, mu zamanin mu ka isa? Ai kai da miji sai kayi arba'in har ba irin Malam masu bakin hali ba."
"Zamanin ne ya chanja Yaya."
"Ai na gani, sai a shige daka da miji a bar me zaman dabaro tana hamma da zare ido, yaran yanzu sam basu da ta ido wallahi."
"Zamanin ne fa Yaya."
"Ai sai ku karata ga ku nan gasu, shiyasa ni ba gidan wadda zanje zaman dabaro kin ganni nan, kowa ya karata chan."
"Uhum." Jidda tace tana hasaso yadda zata kaya idan akace wai itace da ciki ko zata haihu.
***Fada sosai Baban yake ya dauki waya ya kira Tariq yace ya dawo, dama cewa yayi ya basu waje zai kirashi, sai gashi nan ya shigo ya kalli Mama da take cikin tsananin tashin hankali, ta so ita ta fara sanar da Baba maganar tayi masa bayani yadda zai gane amma sai akaci rashin sa'a ya sani wanda bata san ta wajen wa ba, amma kuma yace text akayi masa shiyasa tayi tunanin Nafi ce ta tura masa text din, bata san haka zata mata ba, gashi ta kara sata a matsala dan Baba yace babu ruwan sa tunda har ta iya tura Yara gidan Tariq din duk da tasan rashin dacewar hakan shima kuma ba zai iya komai ba illa ya tursasawa Tariq din auren Salmar kamar yadda yace Maman na so tunda da bata so ba zata fara tura su ba, babu irin bayanin da batayi masa ba akan Nafi karya take amma fafur yaki yace dama ai ya gaya mata tun ba yau ba, ta fita daga harkar gidan Tariq amma taki, shikenan tunda har ta zabi hakan dama kuma bata son jidda sai ya auri Salman dan ya gaji da halin ta.
Gefen Baban Tariq ya zauna Baba ya kalle shi ya nuna sa da hannu sannan ya nuna Maman
"Ga uwar ka nan, tasan duk abinda yake faruwa saboda son zuciyar ta, ta jawo maka matsala da kanta, bani da abinda kuma zan yi akan wannan maganar dan ko zuwa sukayi suka fadawa duniya sun bata min suna, babu kuma wanda zai yarda da mu, duk da su kansu illa zasuyi wa kansu babba amma mutane basa gane hakan idan har suka rasa abun da suka kwalla fa rai akai basu samu ba, toh sai su yi kokarin shafa maka bakin penti, yanzu zamani ne na social media kuma duk abinda aka ce siyasa ta shigo zakayi kokarin kare mutuncin ka da martabar iyalin ka dan abu kad'an sunan ka zai karade ko ina, bani da niyyar tursasa maka aure a wannan lokacin, amma tunda har ban isa na saka ko na hana mahaifiyar ka ba, shikenan gata nan,kaje ka fara shirye-shiryen auren Salmar, idan yaso sai ka ajiye Hauwa'u a gida kaamar yadda take so, ka dauki matar da ta zaba maka ku tafi"
Da sauri Tariq ya dago kansa da yake duke, ya kalli Baban
"Sai ka fara shirye-shirye dan babu lokaci, abinda mahaifiyar ka take so ne, tunda ita Hauwa'u ba 'ya bace a wajen ta,amma ta sani, tana da 'yaya mata duk abinda kayi wa dan wani kaima sai anyi wa naka."
Kan Tariq a k'asa ya kasa motsawa dan be yi tunanin abinda Baban zai ce kenan ba, bayan yayi masa duk bayanin da zai masa kuma ya gamsu ya amince, amma kuma sai yaga Baban ya chanja baki daya kamar bashi ba, tashi Mama tayi dan tasan ko me zatayi ba zai saurare ta a lokacin ba, shiyasa kawai taga gwara ta fita zuwa sanda zai huce, sannan taje ta samu Nafi suyi duk wacce zasuyi dan wallahi da Tariq ya auri Salma gwara ta hakura da Jidda duk da bata son ta.
Yunkurawa Tariq yayi zai bi bayan Maman bayan yayi godiya a ciki ciki Baban ya dakatar dashi yace ya zauna, zama yayi ya tankwashe kafarsa
"Na kira wani a embassy, yace ku shiga gobe da safe, idan yaso daga chan sai ku wuce kanon."
"Na'am?"
"Eh, sannan akan maganar da mukayi yanzu..."
"Baba dan Allah kayi hakuri wallahi ba zan iya auren yarinyar nan ba."
"Na sani, kuma nima ba zan bari ka aure ta ba ,inaso mahaifiyar ku tayi hankali ne, ta ajiye duk makaman yakin ta,ta rungumi Jiddah dan idan aka tafi a haka ko 'yaya kukayi zata iya kin su, tunda tana kin uwarsu."
Ajiyar zuciya ya sauke me karfi wadda har sai da ya bawa Baban dariy
"Jairi, kannen ka mata ne suka sanar dani duk abinda yake faruwa tun ranar da uwata suka zo gidan, nayi shiru ne ina bibiyar komai,."
_"Ashe yaran nan suna da rana."_ yace a cikin zuciyar sa, godiya ya sake yiwa Baban yayi masa sallama ya fito ya wuce kai tsaye wajen aunty dan yasan anan zai tarar da ita
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (52)
***Abinci ta zuba ta zauna tana ci a k'asan carpet suna hira da Aunty sai gashi ya turo kofar ya shigo bakin sa dauke da sallama. A ciki ta amsa Anty kuma ta amsa a fili tana masa maraba. Yanayin da ya ganta a zaune sai ya tuna masa ita ranar da ya fara ganin ta da muryar ta kamar usur wuyanta kamar mirikin lema.
"Barka da rana Aunty."
"Barka dai Tariq, ya gida?"
"Alhamdulillah Aunty."
"Madallah, ya shirye-shiryen tafiyar?"
"Ana kan yi, Visa din Jiddah ce dama zata dan mana delay kad'an."
Ya karashe yana kallon fuskar ta, tunda ya shigo ta daina cin abincin da take ci yana lura da ita
"Masha Allah, toh Allah ya bada sa'a ya taimaka."
A yadda Antyn tayi maganar zaka gane cewa ba karamin farin ciki tayi ba da tafiyar Jiddan, abinda dama take ta hangowa kenan dan indai ya tsallake ya tafi shikenan kuma kashin ta ya bushe a wajen Mama da Nafi dan ta lura Nafin ce take sake zuga Mama akan Jidda,yanzu kuwa idan suka tafi ba shikenan ba?
"Bbyna..." Yayi maganar yadda aunty ba zata ji ba, dago kyawawan idanun ta tayi ta sauke su kansa, ya motsa bakin sa a hankali yace
Kin gama?"
Girgiza masa kai tayi ta cigaba da juya spoon din
"Ok, ki karasa sai mu tafi."
Gid'a masa kai tayi, yayi murmushi kad'an ya zare glasses din idon sa yace
"Aunty, gobe zamu je embassy daga nan zamu wuce Kano in sha Allah."
"Kai dama na biku kawai mu tafi wallahi."
"Aunty mu tafi kawai toh mana."
"A ah, babanku ma ba zai yarda ba, nima kuma tsokanar ku nake duk da inason zuwa din amma zan bari cikin next week in sha Allah."
"Toh Allah ya kaimu."
"Amin ya Allah.'
Mikewa Jidda tayi da plate din dan babu kuma in da abincin zai cigaba da shiga dan gaba daya ya hanata sakat da kallon shi duk da idon sa yana cikin bakin glass amma tsaf ta gano kallon ta yake kuma ta san shi sarai zai iya bata kunya a wajen auntyn dan shi kam babu ruwansa ko a jikin sa.
"Jidda dai wannan cin abincin na wasa me wallahi."
"Shiyasa bata kiba ai aunty."
"Aikuwa, a haka ma ai jiddah tayi kumari, sosai."
"Yanzun ma da sauran ta." Yace k'asa-k'asa amma sai da taji, ta juyo ta dan kalle shi ya motsa bakin sa yana mata murmushi ta shige kitchen din ta wanke bakin ta sannan ta fito ta wuce tsohon dakin ta, bin bayan ta aunty tayi suka barshi a zaune tana shiga ta zauna tace Jiddan ma ta zauna, rike da hisnul muslim dinta da counter sai yar jakar da sarka da abun kafar nan suke ciki da ta dauka a cikin kayan ta tazo ta zauna kusa da Auntyn
"Akwai abinda yake damun ki ne?"