Sashe 75
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tayi dariya, yak'e Jidda tayi ta wuce kawai ciki ta barta a falon bakin ciki na tirnike ta, daga zuwan ta? Sai ta fara cin karo da irin wannan masu budadden idon? Tana daki tana jin motsin ta a falon ko me take yi oho, wanka ta tashi ta shiga ta dauko wani kaya da take tunanin da BA zata iya sawa ba saboda da kunya amma da taga irin shigar da Yasmin din tayi cikin wani matsattsen jeans da riga ta saka turban kawai akanta ko mayafi babu yasa ta ji itama zata iya.
Wankan tayi ta fito ta shirya cikin rigar da ta kasance red colour ta shafa kalolin turarurruka masu kamshin gaske harda wani hadin khumra da Anty ta siya mata a wajen wata mata. Rigar da kadan ta wuce guiwar ta sai ta saka socks me dan tsawo ta gyara gashin kanta ta saka hair band ta fito da gashin ta tsakiyar kan. Light makeup tayi ta shafa red jan baki sosai wanda ya sake fito da sihirtaccen kyawun ta. Rigar daga saman wuyan an dan tsaga ta sai ta dora farar karamar rigar sanyi irin me gashin nan.
Yunwa take ji sosai, ragowar abincin da sukayi order jiya ta tuno ta fito falon, Yasmin na zaune tana kallo a TV tana danna waya ta saki baki ganin Jiddan, kin kallon ta Jiddan tayi ta wuce kitchen din da yake cikin falon Yasmin din na kallon ta tunda ba wai a rufe yake ba, fridge ta bud'e ta dauko abincin tayi warming dinsa a microwave ta zubo a plate tazo ta zauna a kujerar dake facing dinta ta shiga cin abincin a hankali.
"Ya sunan ki?"
Dagowa Jidda tayi ta kalle ta,
"Na'am?"
"What is your name? Sannan menene alakar ku da Tariq?"
"Jidda, alakar mu kuma wannan shi zaki tambaya ai."
"Me yasa?"
"Zai fi iya fada miki ai."
"But baya tsayawa ya saurare ni ai, ni kadai nake son shi amma shi ko kallo ban ishe shi ba, please i need your help."
Wani kallo Jidda tayi mata irin kallon baki da hankali din nan, sannan tayi dariya kawai tana cigaba da cin abincin ta dan ta lura sam Yasmin din bata da hankali.
"Please kanwar mu, wallahi inason shi sosai."
"Naga alama ai, ki sameshi kawai kiyi masa magana nima tsoron sa nake ji."
"Ba zaki iya ba?"
"No ba zan iya ba."
Tace tana mikewa, taje ta wanke plate din ta gyara wajen ta dawo falon ta zauna tayi connecting wayarta da wifi ta kira Amira facetime, lokacin su kusan biyar din yamma. Bata daga ba sai kawai ta mike ta dan kalli Yasmin din tace
"Ki gaida gida ni na shiga ciki."
"Tafiya zan nima, idan ya dawo kice nazo, ga breakfast dinsa nan hade da lunch zan kawo dinner."
"Chef ce ke?"
"Yes." Tace tana murmushi
"Ok yayi."
Tace tana yin gaba, ita kuma Yasmin din ta mike sai gashi ya turo kofar ya shigo, tsayawa chak Jidda tayi jin an budo kofar wanda ta tabbatar da shine, kayan jikin ta, ta kalla kunya na kamata amma sai ta daure ta cije ta juyo tana fuskantar sa., Takalmi yake kokarin cirewa ya lura da Yasmin din dake tsaye a falon nasu, sai Jiddah ta ya kalleta ya sake kalla kafin ya tabbatar da itan ce ko wata ce daban saboda tsabar kyawun da yaga tayi masa. Da wani irin salo da bata san ta iya shi ba, ta nufe shi ta karasa da dan sassarfa ganin yadda yake bin ta da wani irin kallo, rungume shi tayi da sauri ya saki jakar hannun sa yana kankame ta sosai a jikin sa.
"Welcome home baby." Tace tana ciro kanta daga kirjinsa, kin cikata yayi yana shakar kamshin turaren da take yi cikin wani irin yanayi
"I missed you so much."
"Ba kai ne ka tafi ka barni ba?"
"I'm so sorry kinji? Bana so na tashe ki ne naga kin gaji sosai, shiyasa amma dama ba dadewa zan ba."
"Tom shikenan na hakura." Tace tana masa murmushi
"You look very beautiful."
Yace yana kallon kayan jikin nata, murmushi tayi ta duka ta dauki briefcase din tasa ta rike hannun sa
"We have a visitor."
Tace tana nuna masa Yasmin dake tsaye kamar gunki.
"She's not welcome here." Yayi mata whispering a kunne.
"Yasmin welcome, meet my beautiful wife Jidda."
"Oh,okh yayi, Allah ya bada zaman lafiya. But she's young!"
"Young and sweet." Yace yana kissing hannun Jiddan da ke cikin nasa.
"Bari na wuce, Allah ya taimaka."
"Amin mun gode." Jidda tace tana mata murmushi
"Kin manta basket dinki." Tace mata ganin zata fice, banza tayi ta karasa ficewa da sauri. Kicibis sukayi da Ishaq sai kawai ta fashe masa da kuka
"Subhallahi, me ya faru Yasmin?"
"Ishaq Tariq sam bashi da tausayi, ashe aure yayi? Duk yadda nake son shi me yasa baya so na? I'm I ugly? Or what?"
"Calm down, kinsan akwai differences tsakanin ki da Tariq, beside be taba furta miki kalmar so."
"Na sani, kuma I'm 100% ok with that hoping zai iya so na ko gaba ne, amma saboda tsabar wulakanci kaga abinda sukayi min shi da so called wife din shi?"
"Kiyi hakuri please, bari zamuyi magana dashi."
"There no need Ishaq, na hakura wallahi."
Sai ta juya da sauri ta bar wajen. girgiza kai yayi ya fasa zuwa wajen Tariq din kawai ya bi bayan ta.
***Yana zaune kamar sarki ta cire masa tie din ta kawo masa ruwa yasha sai ya jawota kan kafarsa ya manna kansa a jikinsa
"Kin yi kyau Jidda na,and naji dadin yadda kika fahimce ni, kuma kika yi treating Yasmin yadda ya kamata ba hauka ba zubar da class, she mean nothing to me kuma itama ta sani, Ishaq ne duk yayi complicating abun yana bata false hope bayan yasan ba haka bane ba"
"Allah sarki, sai dai tayi hakuri."
"Tariq naki ne ke kadai ko?"
"Yes!" Ta gida masa kai
"Good." Yace yana dariya
"Mine and only mine."
Ta dora tana tashi daga jikin sa rike da tie din nasa. Jawota yayi ya maida ita ta zauna
"Then give me cin hanci idan kinaso na zama yours baki daya."
"Me kake so?"
"Anything special."
"Ok an gama ranka ya dade."
"Wow! Sai ni dan gata." Yace yana matso da fuskar sa tata, yasa baki akan lips dinta ya shiga tsotsa a hankali in a passionate way.
***Rayuwa me dadi da inganci suke yi a tsakanin su cike da kaunar Jun, Tariq baya shakkar nunawa kowa irin kalar soyayyar da yake mata musamman yanzu da suke kasar masu jajayen kunnuwa da babu wanda zai damu da abinda kake ciki ko kayi. Tare suka je ya bawa Yasmin hakuri dan ko yaya ne mutumin da yace yana son ka yafi wanda yaki ka, ashe ma tun ranar da abun ya faru Ishaq ya shigar da kansa wajen ta, and she accepted saboda dama sun shaku sosai.
Duk da busy schedule din Tariq haka yake kula da Jiddan sosai kuma kullum a gida yake kwana tunda har yanzu be fara zama irin so busy din nan ba. Duk abinda zai yi within kasar yake ya dawo amma dai daf yake da fara fita wasu kasashen anan ne kuma dai dole Jidda tayi hakuri, be taba jin yana da second option a aikin nasa ba sai da ya tabbatar dole watarana ya dinga tafiye tafiye sosai kuma ba tare da Jiddan tasa ba.
Wajen taran dare ya shigo gidan a gajiye tikis yana hanya sukayi magana da Fauwaz akan maganar auren sa da aka tambaya wanda Baba yace dukka zai hada harda su amira tunda itama ta samu mijin maryam dama Ya Isma'il ne, da murnar sanar mata ya shigo gidan amma sai ya sameta a kwance ta lulluba da bargo tana rawar sanyi, da sauri ya yaye mata bargon ya durkusa a gaban ta
"Subhallahi, menene?" Yace yana dagota jikin sa
"Zazzabi nake da amai."
Tace tana rufe idon ta saboda tsabar yadda ta galabaita dan kusan sau ashirin tana amai.
"Shine baki kirani ba? Kinga yadda kika galabaita?"
Yace yana cire blanket din saboda yadda zazzabi ya rufe ta sosai. Ruwa ya debo a tap me dumi yazo ya rurrufe dakin sosai yazo ya jawota jikin sa ya janye rigar ta ya shiga goge mata jikin da yayi zafi sosai. Sai da yaga zazzabin ya dan daidaita sannan ya shiga ta wayar sa yayi booking appointments na ganin Dr ya zabi 1hour sannan ya gyara mata jikin ta suka tafi asibitin.
Suna zuwa akayi mata duk gwaje-gwajen da za'a mata aka tabbatar she's pregnant, tsabar murnar be san sanda ya dagata sama ba, dariya Dr din ta dinga musu sannan ta basu maganguna suka dawo gida. Tun daga lokacin shikenan kuma laulayi ya fara me matukar wahalarwa, duk sanda zai fita kamar zai mata kuka saboda tausayin ta,amma sai ta karfafa masa guiwa ta samu ya fitan baya dadewa sosai yake dawowa sai kuma washegari. Da haka har cikin yayi kwari sosai,daidai lokacin bikin su Ya Fauwaz, be so ba dole yace ta fara shiri ya kaita gidan saboda shima aikin nasa ya fara matsawa sosai dan zai iya tafiya yayi kwana biyu ko uku ma baya nan, kuma ko ya dawo ba zai fi yan awowi ba zai sake tafiya. Murna sosai ta hau yi dan batayi tunanin zasu je gida nan kusa ba, shi kansa be yi tunanin hakan ba amma gwara gidan da ta zauna anan din babu kowa shima ba zama yake ba ga ciki kuma.
Wankan tayi ta fito ta shirya cikin rigar da ta kasance red colour ta shafa kalolin turarurruka masu kamshin gaske harda wani hadin khumra da Anty ta siya mata a wajen wata mata. Rigar da kadan ta wuce guiwar ta sai ta saka socks me dan tsawo ta gyara gashin kanta ta saka hair band ta fito da gashin ta tsakiyar kan. Light makeup tayi ta shafa red jan baki sosai wanda ya sake fito da sihirtaccen kyawun ta. Rigar daga saman wuyan an dan tsaga ta sai ta dora farar karamar rigar sanyi irin me gashin nan.
Yunwa take ji sosai, ragowar abincin da sukayi order jiya ta tuno ta fito falon, Yasmin na zaune tana kallo a TV tana danna waya ta saki baki ganin Jiddan, kin kallon ta Jiddan tayi ta wuce kitchen din da yake cikin falon Yasmin din na kallon ta tunda ba wai a rufe yake ba, fridge ta bud'e ta dauko abincin tayi warming dinsa a microwave ta zubo a plate tazo ta zauna a kujerar dake facing dinta ta shiga cin abincin a hankali.
"Ya sunan ki?"
Dagowa Jidda tayi ta kalle ta,
"Na'am?"
"What is your name? Sannan menene alakar ku da Tariq?"
"Jidda, alakar mu kuma wannan shi zaki tambaya ai."
"Me yasa?"
"Zai fi iya fada miki ai."
"But baya tsayawa ya saurare ni ai, ni kadai nake son shi amma shi ko kallo ban ishe shi ba, please i need your help."
Wani kallo Jidda tayi mata irin kallon baki da hankali din nan, sannan tayi dariya kawai tana cigaba da cin abincin ta dan ta lura sam Yasmin din bata da hankali.
"Please kanwar mu, wallahi inason shi sosai."
"Naga alama ai, ki sameshi kawai kiyi masa magana nima tsoron sa nake ji."
"Ba zaki iya ba?"
"No ba zan iya ba."
Tace tana mikewa, taje ta wanke plate din ta gyara wajen ta dawo falon ta zauna tayi connecting wayarta da wifi ta kira Amira facetime, lokacin su kusan biyar din yamma. Bata daga ba sai kawai ta mike ta dan kalli Yasmin din tace
"Ki gaida gida ni na shiga ciki."
"Tafiya zan nima, idan ya dawo kice nazo, ga breakfast dinsa nan hade da lunch zan kawo dinner."
"Chef ce ke?"
"Yes." Tace tana murmushi
"Ok yayi."
Tace tana yin gaba, ita kuma Yasmin din ta mike sai gashi ya turo kofar ya shigo, tsayawa chak Jidda tayi jin an budo kofar wanda ta tabbatar da shine, kayan jikin ta, ta kalla kunya na kamata amma sai ta daure ta cije ta juyo tana fuskantar sa., Takalmi yake kokarin cirewa ya lura da Yasmin din dake tsaye a falon nasu, sai Jiddah ta ya kalleta ya sake kalla kafin ya tabbatar da itan ce ko wata ce daban saboda tsabar kyawun da yaga tayi masa. Da wani irin salo da bata san ta iya shi ba, ta nufe shi ta karasa da dan sassarfa ganin yadda yake bin ta da wani irin kallo, rungume shi tayi da sauri ya saki jakar hannun sa yana kankame ta sosai a jikin sa.
"Welcome home baby." Tace tana ciro kanta daga kirjinsa, kin cikata yayi yana shakar kamshin turaren da take yi cikin wani irin yanayi
"I missed you so much."
"Ba kai ne ka tafi ka barni ba?"
"I'm so sorry kinji? Bana so na tashe ki ne naga kin gaji sosai, shiyasa amma dama ba dadewa zan ba."
"Tom shikenan na hakura." Tace tana masa murmushi
"You look very beautiful."
Yace yana kallon kayan jikin nata, murmushi tayi ta duka ta dauki briefcase din tasa ta rike hannun sa
"We have a visitor."
Tace tana nuna masa Yasmin dake tsaye kamar gunki.
"She's not welcome here." Yayi mata whispering a kunne.
"Yasmin welcome, meet my beautiful wife Jidda."
"Oh,okh yayi, Allah ya bada zaman lafiya. But she's young!"
"Young and sweet." Yace yana kissing hannun Jiddan da ke cikin nasa.
"Bari na wuce, Allah ya taimaka."
"Amin mun gode." Jidda tace tana mata murmushi
"Kin manta basket dinki." Tace mata ganin zata fice, banza tayi ta karasa ficewa da sauri. Kicibis sukayi da Ishaq sai kawai ta fashe masa da kuka
"Subhallahi, me ya faru Yasmin?"
"Ishaq Tariq sam bashi da tausayi, ashe aure yayi? Duk yadda nake son shi me yasa baya so na? I'm I ugly? Or what?"
"Calm down, kinsan akwai differences tsakanin ki da Tariq, beside be taba furta miki kalmar so."
"Na sani, kuma I'm 100% ok with that hoping zai iya so na ko gaba ne, amma saboda tsabar wulakanci kaga abinda sukayi min shi da so called wife din shi?"
"Kiyi hakuri please, bari zamuyi magana dashi."
"There no need Ishaq, na hakura wallahi."
Sai ta juya da sauri ta bar wajen. girgiza kai yayi ya fasa zuwa wajen Tariq din kawai ya bi bayan ta.
***Yana zaune kamar sarki ta cire masa tie din ta kawo masa ruwa yasha sai ya jawota kan kafarsa ya manna kansa a jikinsa
"Kin yi kyau Jidda na,and naji dadin yadda kika fahimce ni, kuma kika yi treating Yasmin yadda ya kamata ba hauka ba zubar da class, she mean nothing to me kuma itama ta sani, Ishaq ne duk yayi complicating abun yana bata false hope bayan yasan ba haka bane ba"
"Allah sarki, sai dai tayi hakuri."
"Tariq naki ne ke kadai ko?"
"Yes!" Ta gida masa kai
"Good." Yace yana dariya
"Mine and only mine."
Ta dora tana tashi daga jikin sa rike da tie din nasa. Jawota yayi ya maida ita ta zauna
"Then give me cin hanci idan kinaso na zama yours baki daya."
"Me kake so?"
"Anything special."
"Ok an gama ranka ya dade."
"Wow! Sai ni dan gata." Yace yana matso da fuskar sa tata, yasa baki akan lips dinta ya shiga tsotsa a hankali in a passionate way.
***Rayuwa me dadi da inganci suke yi a tsakanin su cike da kaunar Jun, Tariq baya shakkar nunawa kowa irin kalar soyayyar da yake mata musamman yanzu da suke kasar masu jajayen kunnuwa da babu wanda zai damu da abinda kake ciki ko kayi. Tare suka je ya bawa Yasmin hakuri dan ko yaya ne mutumin da yace yana son ka yafi wanda yaki ka, ashe ma tun ranar da abun ya faru Ishaq ya shigar da kansa wajen ta, and she accepted saboda dama sun shaku sosai.
Duk da busy schedule din Tariq haka yake kula da Jiddan sosai kuma kullum a gida yake kwana tunda har yanzu be fara zama irin so busy din nan ba. Duk abinda zai yi within kasar yake ya dawo amma dai daf yake da fara fita wasu kasashen anan ne kuma dai dole Jidda tayi hakuri, be taba jin yana da second option a aikin nasa ba sai da ya tabbatar dole watarana ya dinga tafiye tafiye sosai kuma ba tare da Jiddan tasa ba.
Wajen taran dare ya shigo gidan a gajiye tikis yana hanya sukayi magana da Fauwaz akan maganar auren sa da aka tambaya wanda Baba yace dukka zai hada harda su amira tunda itama ta samu mijin maryam dama Ya Isma'il ne, da murnar sanar mata ya shigo gidan amma sai ya sameta a kwance ta lulluba da bargo tana rawar sanyi, da sauri ya yaye mata bargon ya durkusa a gaban ta
"Subhallahi, menene?" Yace yana dagota jikin sa
"Zazzabi nake da amai."
Tace tana rufe idon ta saboda tsabar yadda ta galabaita dan kusan sau ashirin tana amai.
"Shine baki kirani ba? Kinga yadda kika galabaita?"
Yace yana cire blanket din saboda yadda zazzabi ya rufe ta sosai. Ruwa ya debo a tap me dumi yazo ya rurrufe dakin sosai yazo ya jawota jikin sa ya janye rigar ta ya shiga goge mata jikin da yayi zafi sosai. Sai da yaga zazzabin ya dan daidaita sannan ya shiga ta wayar sa yayi booking appointments na ganin Dr ya zabi 1hour sannan ya gyara mata jikin ta suka tafi asibitin.
Suna zuwa akayi mata duk gwaje-gwajen da za'a mata aka tabbatar she's pregnant, tsabar murnar be san sanda ya dagata sama ba, dariya Dr din ta dinga musu sannan ta basu maganguna suka dawo gida. Tun daga lokacin shikenan kuma laulayi ya fara me matukar wahalarwa, duk sanda zai fita kamar zai mata kuka saboda tausayin ta,amma sai ta karfafa masa guiwa ta samu ya fitan baya dadewa sosai yake dawowa sai kuma washegari. Da haka har cikin yayi kwari sosai,daidai lokacin bikin su Ya Fauwaz, be so ba dole yace ta fara shiri ya kaita gidan saboda shima aikin nasa ya fara matsawa sosai dan zai iya tafiya yayi kwana biyu ko uku ma baya nan, kuma ko ya dawo ba zai fi yan awowi ba zai sake tafiya. Murna sosai ta hau yi dan batayi tunanin zasu je gida nan kusa ba, shi kansa be yi tunanin hakan ba amma gwara gidan da ta zauna anan din babu kowa shima ba zama yake ba ga ciki kuma.