Sashe 37
Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A gabansa ya tsaya bayan ya jawo towel sabo daga cikin closet dinsa, ya rataya a kafadar sa
"Yanzu ace har da kai, za'a yi min irin wannan auren a rasa wanda zai fada min."
"I'm very sorry, amma kaima kasan babu wanda yake going against maganar Baba, kuma kai ba kowa ma kake kulawa ba ko da a family din su Mama ne, da nasan definitely wani sai ya fada ma, mu kuwa ba zamu ketare maganar Baba ba, har Mama da taso nuna bata so sai da suka samu matsala akan haka."
"Akan auren?"
"Yes, akan auren wallahi."
"This is serious."
"Shiyasa nake so ka tsaya muyi magana, duk da naga dazu ranka ya baci sosai, amma nasan ba zai yi lasting ba, just hear me out."
"There is no need ai, Baba ya fada min komai, so ka barshi kawai."
Sai ya juya yayi shigewar sa toilet, dan ji yake kamar ya shekara be wanka ba. Yana wankan yana tunanin fuskar ta, wadda ta tsaya masa a ko ina, mamakin kansa yake yi, har ya gama wankan ya dauro alwala ya fito, ya shirya cikin kayan baccin sa, ya feshe jikin sa da turaren Versace collection, ya fito falon ya dauki wayar sa ya sake komawa ciki ya rufe kofar ya rage hasken dakin zuwa me duhu, yayi relaxing akan couch ya kunna datar wayar sa yana so ya duba Ishaq. Ya dan dau lokaci akan wayar yana kallon messages din Yasmin na popping a saman wayar ya share be duba ba, ya saka wayar a flight mood ya kwanta bayan ya karo karfin A C din dakin saboda yadda yake da jin zafin gaske, gashi ya saba sosai da yanayin sanyin kasar da ya baro. A tunanin sa yadda ya dauko gajiya yana rufe idon sa bacci zai dauke shi, amma sai ya samu kansa da kasa baccin kwata-kwata, ya runtse idon sa ya bude amma still baccin yaaki zuwa kemaimai. Mikewa yayi ya kunna hasken dakin ya fito da system dinsa domin ya samu ya mantar da kwakwalwar sa tunanin da take ta kokarin turo masa, ya dade nan ma amma babu wani progress, tunanin ta ne yake neman damun sa, dan ko dan runtse ido yayi sai ya hango ta, a tsaye a kitchen din nan tana jan ajiyar zuciya, duk da be san dalilin kukan nata ba, amma ya taba shi sosai, wanda har yake jin da ya sani ya tambaye ta dalilin kukan nata, duk da baya jin akwai wani abu da zai iya mata bayan tambayar.
Tunawa da yayi be yi shafa'i da wutri ba, yasa shi kashe system din da saka ran kila dan be yi bane yasa ya kasa bacci amma yanzu tunda ya tuna yana idarwa yasan zai kwashe shi baccin. Da wannan tunanin yayi sallar ya sake kwantawa amma dai still ba wani progress, tsaki yaja ya zura slippers dinsa ya fito, ya wuce Fauwaz a falon yana wani aikin cike cike a system, ya bishi da ido har ya fice.
Harabar gidan tana nan kamar rana saboda hasken da ya mamaye ilahirin gidan, be san dalilin da ya fito dashi ba, be kuma san wajen wa zai je ba, ya samu kansa kawai da hakan ya dinga zagaye compound din kamar me gadi, idanun sa na kan part din zuciyar sa na fizgar sa akan ya je, ya shiga amma ya daure, sai da ya gaji da zagayen sannan ya koma ciki ya sake dukunkunewa a cikin blanket, ya samu da k'yar baccin ya dauke shi bayan ya cika kansa da tunanin ranar da duk wani abu da ya wakana a ranar.
***A makare ya tashi dan saura kiris ya rasa sallah a masallaci, dan sau biyu Fauwaz na tashin sa amma ya kasa tashi sai da yaji da gaske idan be tashi ba zai rasa sallar sannan ya taso yayi alwawar a gurguje yafita zuwa masallaci, ana sallar ya dawo daki saboda wani irin bacci da yake ji. Yana kwanciya ya koma baccin wanda har sai da rana ta daga sosai sannan ya tashi, shi din ma aiken Mama ne ya sashi tashi dole dan ta matsu yazo taji yadda aka kare duk da bata taba tunanin akwai wanda zai masa maganar nan a jiyan ba ganin ya dawo kuma ya gaji, ta san kuma basu hadu da Baba ba dan late Baban ya dawo.
Wanka yayi a gurguje, ya nufi part din Maman, ya tarar da abincin sa achan ya dan yi breakfast din sama-sama sannan suka zauna da Maman ta dan bugo cikin sa dan taji yadda ake ciki
"Akwai wata magana da kukayi da wani bayan dawowar ka ne?"
"Magana?" Yace kamar me nazari,
"Eh kamar maganar aure haka ko wani abu."
"Oh eh, Baba yayi min magana."
"Yace maka me? Yaushe ma kuka hadu dashi?"
"Jiya very late, yayi mun maganar."
"Ina fatan baka amince masa ba, dan nasan babu abinda zakayi da wannan yarinyar me kama da sadakar yalla, kafi karfin ta nesa ba kusa ba, saboda haka bana so, ban amince zaman ku a karkashin inuwa daya ba."
"Mama?"
"Kwarai da gaske bana son auren, karfi na kawai akafi dan an hada ni da mahaifin ku,dan haka tunda kai na isa da kai, inaso ka sakar musu 'ya, dan bana kaunar ta ko miskila zarratin wallahi,idan yaso koma wace sai ka samo kuyi auren ku".
"Tunda ba kya son ta sai ki hanata numfashi Aisha."
Mikewa tayi Tariq din ma ya mike da sauri suka kalli kofar da Baban ya shigo, kofar baya da ya saba shigowa part din. Da safe Mama taji fitar sa dan da wuri ya fice daga gidan bata kuma zata ya dawo ba, kunya ce ta lullube ta, ta rasa in da zata saka kanta dan ba haka taso ayi ba, ya akayi ma bata ji bud'e kofar ba sai shigowar sa kawai
"Nace tunda bakya son ta, sai ki katse mata numfashi."
Hanyar ficewa Tariq ya nema, Baba ya buga masa tsawar da tasa shi kasa kara ko step daya
"Wallahi wallahi wallahi, kaji rantsuwar dan musulmi ko? Wallahi ka kuskura, ka saki Hauwa'u wallahi babu ni babu kai, kaji na fada maka."
"Ayi hakuri Baba."
Ya russunar da kansa k'asa
"Ke kuma, ko ciwon kai Hauwa'u tayi sai na tuhume ki, dan bazan kara yarda dake ba, ni ne ubanta dan haka zan yi duk yadda zan yi na kare ta daga sharrin ki, mutuniyar banza."
K'ala Mama bata ce ba, ya juya ya fice Tariq ya bi bayan sa da sauri
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (30)
***Wani abu yaji tunda tsakiyar kansa har zuwa tafin kafarsa, yaji kamar duniyar na juyawa baki daya a tsakankanin su, su biyu kadai, kokarin zare jikinta take ya matse ta sosai ya hana mata ko da kwakkwaran motsi. Lamo tayi tana jan numfashin kadan-kadan. Bugun zuciyar ta ne ya hadu da nasa, har tana iya jin yadda tasa ke beating very fast kamar wanda yayi gudun tsere.
"Why are you always crying?"
Yace cikin muryar sa da ta shiga chan ciki, bata amsa ba, sai dan motsawa da tayi kad'an ya sake kankame ta
"Tell me? Ba kya son auren?"
Wani irin faduwa gaban ta yayi, ya cigaba da magaanar cikin kunnenta
"Nima bana so... So ki daina kuka zamu samu hanyar da ba zamuyi hurting iyayen mu ba, I promise you."
Baki daya tunanin ta ne ya tsaya na dan dakiku, taji gaba daya duniyar na juya mata, a tunanin sa saboda bata son auren take kuka? a tunanin ta kuma ta dauka he's ready to accept her, a tunanin ta ba zai iya furta mata baya son auren ba duk da bata da yakinin dama yana so din, a karo na biyu ya sake breaking heart dinta, into pieces. Fizge jikin ta tayi da karfin gaske, ta matsa daga jikin motar ta juya masa baya. Kallon bayan ta yake yana jin duk babu dadi. Kukan ta cigaba da yi yana jinra, yana jin wani irin zafi a cikin zuciyar sa, be san meyasa kukan yake taba shi ba, duk da dama shi a rayuwar sa ya tsani yaga mace tana kuka, kallon su yake a matsayin wasu weak mutane da kukan kawai zai iya haddasa musu babban al'amari.
Zuciyar ta ce ta dake, taji a lokaci daya kukan da take ya dauke, taji bata son sake ko da minti daya ne a zaune a cikin motar, babu amfani, kwata-kwata babu amfanin cigaba da kukan ta, duk da tasan da gasken gaske take son shi, amma kuma babu amfani tunda shi baya so, zata sakawa zuciyar ta salama ta karbi duk wani abu da yazo mata, ba zata sake bata hawayen ta ba, balle murfin motar tayi, zata fita yayi saurin fincikota, ya rike ta k'akam yana saka idon sa acikin nata
"Menene matsalar ki?" Ya fada yana zagaye idanun sa a kan fuskar ta
"Ka kyale ni dan Allah."
"Me yasa? Tell me? Ki bud'e bakin ki, kiyi magana."
"Gida nake son zuwa." Tace tana kauda kanta gefe ganin yadda yake motso da fuskar sa daf da tata.
"Zaki je gidan, just tell me menene yake saki kuka? Are you sick? Baki da lafiya ne?"
Girgiza masa kai tayi
"Toh menene? Tell me dan Allah..."
"Ba komai, ni ka kaini gida."
"Ba zan kaiki din ba, anan zamu kwana babu in da zaki."
Kallon sa tayi ya gid'a mata kai, kwace hannun ta, tayi ta motsa kafarta tana kokarin sauka yace
"Idan kika fita wallahi sai na baki mamaki."
Kamar bata ji ba, ita burin ta kawai ta je gida, ta gaji da zama waje daya dashi knowing fully baya son ta, he's just concern akan kukan da take, which yake tunanin ma son auren ne bata yi shiyasa.
"Yanzu ace har da kai, za'a yi min irin wannan auren a rasa wanda zai fada min."
"I'm very sorry, amma kaima kasan babu wanda yake going against maganar Baba, kuma kai ba kowa ma kake kulawa ba ko da a family din su Mama ne, da nasan definitely wani sai ya fada ma, mu kuwa ba zamu ketare maganar Baba ba, har Mama da taso nuna bata so sai da suka samu matsala akan haka."
"Akan auren?"
"Yes, akan auren wallahi."
"This is serious."
"Shiyasa nake so ka tsaya muyi magana, duk da naga dazu ranka ya baci sosai, amma nasan ba zai yi lasting ba, just hear me out."
"There is no need ai, Baba ya fada min komai, so ka barshi kawai."
Sai ya juya yayi shigewar sa toilet, dan ji yake kamar ya shekara be wanka ba. Yana wankan yana tunanin fuskar ta, wadda ta tsaya masa a ko ina, mamakin kansa yake yi, har ya gama wankan ya dauro alwala ya fito, ya shirya cikin kayan baccin sa, ya feshe jikin sa da turaren Versace collection, ya fito falon ya dauki wayar sa ya sake komawa ciki ya rufe kofar ya rage hasken dakin zuwa me duhu, yayi relaxing akan couch ya kunna datar wayar sa yana so ya duba Ishaq. Ya dan dau lokaci akan wayar yana kallon messages din Yasmin na popping a saman wayar ya share be duba ba, ya saka wayar a flight mood ya kwanta bayan ya karo karfin A C din dakin saboda yadda yake da jin zafin gaske, gashi ya saba sosai da yanayin sanyin kasar da ya baro. A tunanin sa yadda ya dauko gajiya yana rufe idon sa bacci zai dauke shi, amma sai ya samu kansa da kasa baccin kwata-kwata, ya runtse idon sa ya bude amma still baccin yaaki zuwa kemaimai. Mikewa yayi ya kunna hasken dakin ya fito da system dinsa domin ya samu ya mantar da kwakwalwar sa tunanin da take ta kokarin turo masa, ya dade nan ma amma babu wani progress, tunanin ta ne yake neman damun sa, dan ko dan runtse ido yayi sai ya hango ta, a tsaye a kitchen din nan tana jan ajiyar zuciya, duk da be san dalilin kukan nata ba, amma ya taba shi sosai, wanda har yake jin da ya sani ya tambaye ta dalilin kukan nata, duk da baya jin akwai wani abu da zai iya mata bayan tambayar.
Tunawa da yayi be yi shafa'i da wutri ba, yasa shi kashe system din da saka ran kila dan be yi bane yasa ya kasa bacci amma yanzu tunda ya tuna yana idarwa yasan zai kwashe shi baccin. Da wannan tunanin yayi sallar ya sake kwantawa amma dai still ba wani progress, tsaki yaja ya zura slippers dinsa ya fito, ya wuce Fauwaz a falon yana wani aikin cike cike a system, ya bishi da ido har ya fice.
Harabar gidan tana nan kamar rana saboda hasken da ya mamaye ilahirin gidan, be san dalilin da ya fito dashi ba, be kuma san wajen wa zai je ba, ya samu kansa kawai da hakan ya dinga zagaye compound din kamar me gadi, idanun sa na kan part din zuciyar sa na fizgar sa akan ya je, ya shiga amma ya daure, sai da ya gaji da zagayen sannan ya koma ciki ya sake dukunkunewa a cikin blanket, ya samu da k'yar baccin ya dauke shi bayan ya cika kansa da tunanin ranar da duk wani abu da ya wakana a ranar.
***A makare ya tashi dan saura kiris ya rasa sallah a masallaci, dan sau biyu Fauwaz na tashin sa amma ya kasa tashi sai da yaji da gaske idan be tashi ba zai rasa sallar sannan ya taso yayi alwawar a gurguje yafita zuwa masallaci, ana sallar ya dawo daki saboda wani irin bacci da yake ji. Yana kwanciya ya koma baccin wanda har sai da rana ta daga sosai sannan ya tashi, shi din ma aiken Mama ne ya sashi tashi dole dan ta matsu yazo taji yadda aka kare duk da bata taba tunanin akwai wanda zai masa maganar nan a jiyan ba ganin ya dawo kuma ya gaji, ta san kuma basu hadu da Baba ba dan late Baban ya dawo.
Wanka yayi a gurguje, ya nufi part din Maman, ya tarar da abincin sa achan ya dan yi breakfast din sama-sama sannan suka zauna da Maman ta dan bugo cikin sa dan taji yadda ake ciki
"Akwai wata magana da kukayi da wani bayan dawowar ka ne?"
"Magana?" Yace kamar me nazari,
"Eh kamar maganar aure haka ko wani abu."
"Oh eh, Baba yayi min magana."
"Yace maka me? Yaushe ma kuka hadu dashi?"
"Jiya very late, yayi mun maganar."
"Ina fatan baka amince masa ba, dan nasan babu abinda zakayi da wannan yarinyar me kama da sadakar yalla, kafi karfin ta nesa ba kusa ba, saboda haka bana so, ban amince zaman ku a karkashin inuwa daya ba."
"Mama?"
"Kwarai da gaske bana son auren, karfi na kawai akafi dan an hada ni da mahaifin ku,dan haka tunda kai na isa da kai, inaso ka sakar musu 'ya, dan bana kaunar ta ko miskila zarratin wallahi,idan yaso koma wace sai ka samo kuyi auren ku".
"Tunda ba kya son ta sai ki hanata numfashi Aisha."
Mikewa tayi Tariq din ma ya mike da sauri suka kalli kofar da Baban ya shigo, kofar baya da ya saba shigowa part din. Da safe Mama taji fitar sa dan da wuri ya fice daga gidan bata kuma zata ya dawo ba, kunya ce ta lullube ta, ta rasa in da zata saka kanta dan ba haka taso ayi ba, ya akayi ma bata ji bud'e kofar ba sai shigowar sa kawai
"Nace tunda bakya son ta, sai ki katse mata numfashi."
Hanyar ficewa Tariq ya nema, Baba ya buga masa tsawar da tasa shi kasa kara ko step daya
"Wallahi wallahi wallahi, kaji rantsuwar dan musulmi ko? Wallahi ka kuskura, ka saki Hauwa'u wallahi babu ni babu kai, kaji na fada maka."
"Ayi hakuri Baba."
Ya russunar da kansa k'asa
"Ke kuma, ko ciwon kai Hauwa'u tayi sai na tuhume ki, dan bazan kara yarda dake ba, ni ne ubanta dan haka zan yi duk yadda zan yi na kare ta daga sharrin ki, mutuniyar banza."
K'ala Mama bata ce ba, ya juya ya fice Tariq ya bi bayan sa da sauri
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**
©®*_*_Hafsat Rano_*_*
Page (30)
***Wani abu yaji tunda tsakiyar kansa har zuwa tafin kafarsa, yaji kamar duniyar na juyawa baki daya a tsakankanin su, su biyu kadai, kokarin zare jikinta take ya matse ta sosai ya hana mata ko da kwakkwaran motsi. Lamo tayi tana jan numfashin kadan-kadan. Bugun zuciyar ta ne ya hadu da nasa, har tana iya jin yadda tasa ke beating very fast kamar wanda yayi gudun tsere.
"Why are you always crying?"
Yace cikin muryar sa da ta shiga chan ciki, bata amsa ba, sai dan motsawa da tayi kad'an ya sake kankame ta
"Tell me? Ba kya son auren?"
Wani irin faduwa gaban ta yayi, ya cigaba da magaanar cikin kunnenta
"Nima bana so... So ki daina kuka zamu samu hanyar da ba zamuyi hurting iyayen mu ba, I promise you."
Baki daya tunanin ta ne ya tsaya na dan dakiku, taji gaba daya duniyar na juya mata, a tunanin sa saboda bata son auren take kuka? a tunanin ta kuma ta dauka he's ready to accept her, a tunanin ta ba zai iya furta mata baya son auren ba duk da bata da yakinin dama yana so din, a karo na biyu ya sake breaking heart dinta, into pieces. Fizge jikin ta tayi da karfin gaske, ta matsa daga jikin motar ta juya masa baya. Kallon bayan ta yake yana jin duk babu dadi. Kukan ta cigaba da yi yana jinra, yana jin wani irin zafi a cikin zuciyar sa, be san meyasa kukan yake taba shi ba, duk da dama shi a rayuwar sa ya tsani yaga mace tana kuka, kallon su yake a matsayin wasu weak mutane da kukan kawai zai iya haddasa musu babban al'amari.
Zuciyar ta ce ta dake, taji a lokaci daya kukan da take ya dauke, taji bata son sake ko da minti daya ne a zaune a cikin motar, babu amfani, kwata-kwata babu amfanin cigaba da kukan ta, duk da tasan da gasken gaske take son shi, amma kuma babu amfani tunda shi baya so, zata sakawa zuciyar ta salama ta karbi duk wani abu da yazo mata, ba zata sake bata hawayen ta ba, balle murfin motar tayi, zata fita yayi saurin fincikota, ya rike ta k'akam yana saka idon sa acikin nata
"Menene matsalar ki?" Ya fada yana zagaye idanun sa a kan fuskar ta
"Ka kyale ni dan Allah."
"Me yasa? Tell me? Ki bud'e bakin ki, kiyi magana."
"Gida nake son zuwa." Tace tana kauda kanta gefe ganin yadda yake motso da fuskar sa daf da tata.
"Zaki je gidan, just tell me menene yake saki kuka? Are you sick? Baki da lafiya ne?"
Girgiza masa kai tayi
"Toh menene? Tell me dan Allah..."
"Ba komai, ni ka kaini gida."
"Ba zan kaiki din ba, anan zamu kwana babu in da zaki."
Kallon sa tayi ya gid'a mata kai, kwace hannun ta, tayi ta motsa kafarta tana kokarin sauka yace
"Idan kika fita wallahi sai na baki mamaki."
Kamar bata ji ba, ita burin ta kawai ta je gida, ta gaji da zama waje daya dashi knowing fully baya son ta, he's just concern akan kukan da take, which yake tunanin ma son auren ne bata yi shiyasa.