← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 76

Sashe 57

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)*

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_
*HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_
*_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_*
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (46)

Assalamualaikum

NAFISAT K ABDULLAHI
Is an actress in the kannywood industry

She's a singer and can sing all types of songs

You can't afford to miss her newly released song named *KADDARATA* part 1-4 on her YouTube channel *OFFICIAL FEENAT*

You can only click on this link and stand a chance to listen and watch her amazing video

https://youtu.be/t__84EwU7Fo

Dont only enjoy the emotional video but also *SUBSCRIBE* to anable you to be notified when ever she upload another video

Like and drop your comment under the video to encourage her do more of that .

The only way you can support and encourage her is by *SUBSCRIBING* to her YouTube channel below

https://youtu.be/t__84EwU7Fo

She is used to noticing those following and commenting on her videos .

*GUESS WHAT*?

https://youtu.be/t__84EwU7Fo

Click and see for yourself
Thank you so much

***Maganar tafiyar Mama tayi masa dan tana so taje kano a weekends din da za'a shiga idan akwai abinda zata taho masa dashi, ko da tayi masa maganar tafiyar sai yace yayi postponding dinta har ya tura musu mail ma duk da basuyi reply ba

"Amma me yasa zaka daga? Ba kace suna jiran ka ba?" Ta tambaya cike da mamakin sa

"Wani abu ne ya taso Mama, dole na fara solving din matsalar kafin na tafi."

"Matsalar mecece?"

"Umm... Ba wani babban abu bane in sha Allah, karki damu."

"Dole dai akwai dalili, haka kawai ba zaka daga tafiya ba."

"Allah yasa haka ne mafi alkhairi "

"Amin." Tace a gajarce

"Yaushe Baba zai dawo? Ban sameshi a waya ba tunda ya tafi "

"Mun yi magana jiya amma be maganar dawowar ba tukunna, kasan baya fada yanzu sai ana i gobe."

"Fasa tafiya sukayi da Auntyn?"

"Oho ban sani ba."

Murmushi yayi kawai ya cigaba da zama shiru, itama tayi masa shiru sai da Maryam ta fito ta gaishe shi sannan ya tuna da maganar su Amira

"Mah tunda ba tafiya zan ba sai su dawo ko?"

"Akan ka suke zaune? Ko ita shafaffiya da mai din ce tace su tafi?"

Shiru yayi mata dan be san me zai ce mata ba, ba kuma yaso tana involving Jidda a ciki dan da yasan yadda zata dauki maganar da be yi ba. Jin yayi shiru yasa itama tayi shiru suka cigaba da zama a haka, sai chan ya tashi yace zai tafi lokacin ana shirye-shiryen kiran sallar magriba, sallama sukayi ya wuce masjid yayi sallah suka gaisa da wasu mutanen Baba da suke yawan zuwa gidan sannan ya wuce gida ba tare da ya koma ciki ba.
Yana daf da shiga gidan shi da Faisal Safiyya ta kirashi, suka gaisa tayi masa maganar Salma da dalilin zuwa gidan nasu, shiru yayi yana jin ta har ta gama bayanin da ya riga ya sani shiru kawai yayi dan baya son batawa Mama, sai dai maganar zubar da man da tayi da niyya ya matukar bashi tsoro dan zata iya aikata komai, dama yayi tunanin itace tunda dazu da yaji suna maganar da Jidda da amira akan man da aka zubar din amma sai Jiddan ta rufe maganar, ransa ne yaji ya baci, yace wa safiyyan karta damu yayi assuring dinta babu abinda zai faru sannan sukayi sallama ya kashe wayar yana tunanin yadda zai bullowa al'amarin Maman dan yarinyar ta kai shi karshe musamman da ya tuna bakar wahalar da Jiddan tasha dazun. Dama ya ga take taken ta sharewa yayi kawai yana jiran right time dan duk wani action da zai dauka akan Jidda abin zai kare, shiyasa ya kyale tun farko amma yanzu yasan abinda zai kawai ya kawo karshen wannan drama din, jiran Baba kawai yake ya dawo suyi magana idan har ya bashi goo ahead shikenan.

Shigar Jidda daki kenan ya shigo gidan, tana toilet bata ji shigowar sa ba, wuf Salma ta fito falon ta tsaya tana jiran shigowar sa, ta chanja kayan jikinta zuwa kanana bodyhug da jeans da ya kamata sosai, kanta babu ko dankwali sai attach din da ta bazo har gadon bayan ta. Turo kofar yayi cike da karsashin ganin ta, dan ji yake kamar yayi shekara be sa ta a idon sa ba, so yake yaga jikin nata duk da sau biyu yana kiran wayarta bata dauka ba sai yayi tunanin ko baccin take har lokacin sai kawai ya kyale ta. Annurin fuskar sa ne ya ringa janyewa yana maye gurbi da bacin rai, tsananin bacin ran ganin shigar iskancin da yarinyar tayi ta kuma toge a hanya tana masa kallo tamkar tsohuwar mayya.

"Ya T Welcome."

"Amira!!!" Ya kwala mata kira, a guje ta fito itama Jidda ta fito da sauri,

"Jeki fito da kayan da kuka zo dasu." Yace zuciyar sa na tafasa, da sauri ta juya jidda da ta tsaya daga hanya ta kasa karasowa ya kuma ki yarda ya kalli sashen da take ta sake jingina da bangon wajen tana kallon ikon Allah. Amira ce ta fito ya nuna mata hanya

"Ja wannan mahaukaciyar yarinyar ku fice min daga gida."

"Ya Tariq nice mahaukaciya?"

"Shut up stupid, Allah Amira kika bari na kara magana sai na baku mamaki, kije ki samu faisal ya sauke ku a gida."

"Ke kuma,wallahi wallahi ko kafar ki na gani a hanyar gidan nan sai na tattaka ki na zubar, stupid girl."

"Muje malama."

Amira tace tana hararar ta, tsayawa tayi taki motsawa jin tarin Jidda a bayan ta, ba'a taba humiliating dinta irin yau ba, kamar an dasa ta a wajn haka ta kasa motsawa, sai da Amira ta fizgi hannun ta sannan ta iya daga kafarta guda daya sannan ta motsa dayar. Wuce su yayi yana kokarin daidaita fushin da yake ciki, ya nufe ta ganin duk ta tsorata da yanayin sa. Ji tayi kawai yayi hugging dinta da sauri yana sauke ajiyar zuciya, kafin ya ja hannun ta su bar falon ba tare da ya sake bi ta kan su Amira ba.

Tun a mota Salman ta dinga rusa kuma Amira bata tanka mata ba, dama tun ranar farko taso ya Tariq din ya kore su amma ya kyale su, ita tana ta danna waya bata ma lura da falo Salman ta fito ba, ta dauka ma tana toilet ashe yar iskar yarinya wai tarar Ya Tariq din tazo,lallai bata san waye shi ba, su kansu da suke ciki daya basa zama tare dashi haka ba mayafi bare har suyi wata banzar shiga sam basu taso da wannan rayuwar ba, akwai limit a komai idan aka cire ma Ya Fauwaz da Ya Safiyya babu Wanda a cikin su Ya Tariq din yake wata doguwar magaana dasu bare har su samu fuskar raina shi, ita Amira da yake ma itace karama kuma akwai tazara sosai a tsakanij su tsoron sa ma take ji shiyasa bata so zuwan su gidan ba, shima kuma yasan ba zata so ba amma ya zatayi da Mama? Tun farko basu iya cewa Maman a ah ba a komai tace tunda dama ba tarbiyya bace, shiyasa har Ya Tariq din baya ketare maganar ta sai dai a irin case din yanzu na jiddah da kuma ko waye tasan hakan zai yi tunda dai tsanar da tayi ma Jiddan ba ta da wani kwakkwaran dalili. motar na gama parking Amira ta fice ta wuce part din Yaya dan ma kar su Mama su cikata da tambaya dan yau tasan akwai rikici a wajen Aunty Nafi akan shalelen ta, dan bata sani ba ma ko kafin fitowar ta daga daki Ya Tariq din ya dan mammari fuskar ta.
Tunda suka shiga dakin ya zauna be ce uffan ba, tana ta satar kallon sa yayi nisa a tunani, he looked disturbed kamar akwai wani abu bayan abinda ya faru yanzu da ya dame shi. Ji tayi duk ta damu da damuwar sa dan tunda tazo gidan bata taba ganin damuwa karara kamar haka a fuskar shi ba. Kasa sukuni tayi, ta taso tazo gabansa ta zauna ya kalli babban dan yatsan kafar tata sannan ya kalli fuskar ta, sai ya zamo ya zauna a kasan kan carpet din da ke gaban gadon ya kama hannun nata

"Sun daina ciwon?"

Yace bayan ya hadiye yawun da ya taru a makoshin sa, gid'a masa kai tayi, ya lura tana son yin amfani da kanta wajen amsa tambayar da amsar ta dari bisa dari.

"Kafar fa?"

"Da sauki."

"Basu daina ba ko? Raguwa ciwon kawa yayi."

"Eh."

"Owk sannu."

"Uhumm."

"Shine baki fada min Salma ce ta zubar da man da kika zame ba ko? Yanzu idan da tsautsayi kika karye fa? Ko wani abu worst than this ya faru? Shikenan sai kiyi shiru?"

"Bana son ranka ya baci ne, shiyasa kawai na kyale, tunda Allah ya kiyaye ma."

"Karki kara irin wannan, babu amfanin zaman mu da ita in dai cutarwa zata shigo ciki."

"In sha Allah ba zan kara ba."

"Good."

"Shikenan?" Tace ganin be saki ran nasa ba har lokacin, girgiza mata kai yayi yadda take yi yace

"Ba shikenan ba."

"Ok." Tace a sanyaye.

"Ciwon ya daina?" Ya sake tambayar ta bayan be dade ta tambayar ta ba

"Kad'an yake yi."

"Ok ."
Chapter 57 · 0% Book details