← Book details Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 76

Sashe 22

Sanadin Labarina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ita, dan Malamin da ya bashi rubutu ya fada min, idan aka basshi haka sakaka toh ko auren ma ba zai ba, haka zai kare rayuwar sa, ni kuma sai na duba kaf dangi babu me halin Jidda, ita kadai zata iya taimaka mana ta rufa mana asiri."

"Amma Yaya Jiddah fa, da Ya Tariq?"

"Menene a ciki?"

"Ba komai, amma a fara jin ta bakin ta kar ayi mata dole."

"In sha Allahu ma babu wata matsala, ina ji a raina zasuyi rayuwar aure ingantacciya."

"Toh yanzu ta yaya hakan zata kasance?"

"Ni dai kai zaka taimaka min, ka sami Jiddah da maganar naga kuna shiri sosai, ni kuma zan fadawa Baban KU."

"Toh Ya Tariq din fa?"

"Karka fada masa, irin matsalar sa ai baa fada musu sai dai kawai ayi dan aka daka ta tasu wallahi ba za'a yi ba."

"Auren dole kenan za'a masa."

"Dallah ana kaika."

"Toh ai Yaya abin ne, nasan halin ya Tariq da taurin kai, kar ya bata ma yarinya lokaci azo ba'a barta ta zabi miji da kanta ba shi kuma yazo yace ya fasa."

"Ai wallahi ina me tabbatar maka be isa ba, kai dai kawai kayi abinda nace, sauran ka bar komai a hannu na, Dijengala nake me abun mamaki "

"Toh Allah ya taimaka dije."

"Ka fadi sunan uwarka."

"Hahaha, Allah sai na fasa taimaka miki."

"Yi hakuri toh."

"Ban hakura ba, sai kince please."

"Ni zaka wulakanta dan zaka taimaka min?"

"A ah, amma sai kin bani hakuri da turanci."

"Kasan dai bana son shegen turancin nan? Kaga ana ciccize baki wai a dole ana turanci, mtswws! Aikin bur inji tusa."

"Shikenan tunda bakya son taimako na, kuma sai na fadawa Ya Tariq abinda kike shirya masa idan yaso ya hawo jirgi yazo ya sameki."

"Yazo din mana, tsoron sa nake? Karka taimaka din idan baka taimaka ba ai ubanka zai taimaka tunda shi na isa dashi."

"Calm down My heart beat, wasa fa nake miki, ai ban isa naki abinda kike so ba, yanzu zanje na fara aikin ki."

"Yawwa dan albarka, yi maza ka gama kai ma na samo maka taka ko a karkara ne."

"Wait what? Wallahi kar ma a fara dan ina da fine babe dita idan ba haka ba kuwa zan bar gari na hada kayana na tafi karkashin gada."

"Ka tafi bangon duniya ma, dan nema."

"Maimakon ki lallaba ni,o matar nan."

"Ba zan lallaba din ba, nima ba uban da ya lallaba ni da za'a auran min dunkum din kakanku."

Da sauri ya sa hannu ya toshe bakin sa saboda yadda ta bashi dariya sosai, ya mike ya fice dan idan ya biye mata ba zata gaji ba sam.

Tsohon part dinsu ya shiga, ya ciro sabuwar wayar Jidda ya bude ta, ya tura hotunan Ya Tariq masu yawan gaske sai nasu dasu Amira dan kar ta kawo komai, sannan ya kashe ta, ya maida ita kwalinta, ya nufi bangaren Auntyn.
Jidda na kwance a daki tayi rigingine taji usman na ihun ya Fauwaz, da sauri ta duro ta fito ta same shi a tsaye ya daga Usman sama yana dariya.

"Ya Fauwaz." Tace ya sauke Usman yana mata murmushi

"Jidda ce tayi kiba haka?" Yace a sigar tsokana, dariya ta saka

"Kai Ya Fauwaz yaushe ka ganni last zaka ce nayi kiba."

"Allah kuwa, idan na ganki a hanya ma ai ba zan gane ki ba."

Dariya kawai take dan tasan hadda tsokana, duk da tasan tayi mugun chanjawa sosai dan baki daya jikinta ya murje duk ramukan nan sun ciko sai wanda ba za'a rasa ba. Bangaren chest da bayanta a lokaci daya tayi su dan bata taba ma tunanin zata yi ba, girman lokaci daya yazo mata shiyasa yanzu koyaushe da Hijab dinta take yawo a cikin gidan saboda ma'aikatan da masu gadin gidan.
Ledar wayar ya mika mata ta karba tana leka ciki, tayi tsalle cike da murna,

"Sakon Baba,."

"Mungode Allah ya kara budi."

"Amin Amin, Amira ma jiya aka bata tata, number ta na ciki tace ki kirata kina kunna wayar akwai gist."

"Toh shikenan, yau ba zan iya bacci ba, kusan kwana zamuyi muna hira nasan."

"Lallai gandoki, zaku yi ku bari ne, ina Aunty ta shiga?" Ya waiga yana kallon bangaren bedroom din Auntyn

"Tana part din Baba."

"Ok, gidan shiru,kuma ku tattara ku dawo ma dinga zuwa hutu kawai."

"Aikuwa."

"Shine, dama akwai plan din Baba, amma wannan zuwan nasan har da magaanar tafiyar ma, kinga ya maida hankalin sa waje daya ya dinga zuwa ko duk after two weeks ne, yanzu kuwa yana chan hankalin sa na nan."

"Ai kamar Yaya ce bata son tafiya ko?"

"Haka zata hakura, an gama.mata part dinta ma fa."

"Lallai dole ta hakura."

"Aikam, in baki labari." Yayi kasa da murya

"Nayi new babe wallahi."

"Dan Allah, aina take?"

"A chan Abujan ne."

"Lallai, Masha Allah."

"Ki bari kawai, zuwa zan na shige daga ciki, na bar Ya Tariq tunda shi ya tsaya kure wa boko guda."

"Be gama ba har yanzu? Ya dade."

"Ya gama wani course yake, kinsan pilot ne."

"Wai, ban ma sani ba ai."

"Aiko yana chan ya kusa ma, dazu muka gama waya ma."

"Allah sarki, idan kunyi waya ka gaishe shi."

"Gaki da sabuwar wayar ki, na ma saka miki number kowa har tasa, ki kirashi kawai."

Zaro ido tayi

"Wai... Tsoron sa nake ji, ba zan iya ba wallahi."

"A ah zaki iya mana, menene abun tsoro?"

"Uh um, ka gaishe shi kawai."

"Toh shikenan, zaiji."

"Nagode."

"Bari na dubo Jamil mu gaisa, zan dawo idan aunty ta fito."

"Ok sai ka dawo."
[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**

      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*

                  Page (18)

***Tunda suka shigo mota be kara magana ba, tsoron sa daya kar Jiddah taki shi, be san ya zai yi da rayuwar sa ba idan har tace bata son shi. Da kyar ya kaisu gida suna zuwa yayi saurin yin hanyar dakin sa, jiki a sanyaye itama Safeeran tayi nata dakin tana fatan kar a samu matsala dan ta san yadda Ya Isma'il yake son Jidda.
Tunda ya shiga dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye,duk da ba wai tace bata son shi bane, amma kuma ai be kamata ta rikice haka ba, ya kamata ko yaya ne ta bashi amsa. Wayar sa ya dauka ya kira Farouk yace ya shigo dan Allah, nan da nan sai gashi, ya kwashe komai ya fada masa , shiru yayi yana nazari kafin yace

"Kila shock ne, kasan har yanzu fa da sauran su, kila bata taba tunanin hakan ba shiyasa tayi acting haka, give her some time, in sha Allah Khair."

"Kana ganin ba matsala, tari ne fa ya sarketa kamar zata shid'e."

"Calm down, ina ji a raina ba matsala bace gaskiya, ka bata time ka barta da Safeera suyi magana, kawarta ce tafi kowa sanin ta, hopely zata iya convincing dinta ma."

"I hope so, I'm just nervous ne, ba zaka gane ba. I don't think zan iya daukan rejection."

"Ba matsala fa, ka kwantar da hankali ka, as you come fine like this akwai wata babe da zata ki ka ne?"

"A ah fa, banda irin Jidda."

"Hadda wadda tafi Jidda ma."

"Kana dai fasa min kai ne kawai."

"Da gaske fa "

"Toh naji, bari na duba me akayi a kitchen yunwa nake ji yau ko breakfast ban ba."

"Kaji ko?"

"Bari kawai."

Yace ya fita shi kuma ya mike kafarsa yana tausayin Isma'il din idan har aka samu matsala.

***Zaman jiran Baba yayi tayi har bayan isha, sannan ya shigo a gajiye duk da haka sai da ya tsaya a wajen Yayan dan yasan tana nan tana jiran sa, a zaune kuwa ya sameta tana kallo tana dan gyang'adi, sallamar sa ta sakata wartsakewa ta mike da sauri

"Yaya baki bacci ba, Allah yasa bani na rike ki ba nasan da wuri kike kwanciya."

"Kai nake ta jira wallahi, sannu da hanya."

"Yawwa, ai da kin kwanta idan Allah ya kaimu da safe sai muyi maganar."

"Ba zan iya hakura bane ai, magana ce me muhimmanci."

"Toh, Allah yasa lafiya "

Yace yana zama a kasan carpet din,daga gefen kafarta, baya taba zama kujera da mahaifiyar sa tunda ya taso, yana bala'in so da kaunar Yaya dan baya hada duk wani abu da ya shafe ta da kowa har kuwa da yayan cikin sa, shiyasa duk abinda take so shi yake mata. Gaba daya ya tattaro hankalin sa waje daya ya kara tankwashe kafarsa, dan yasan idan ba fada masa matsalar Yaya tayi ba ko baccin kirki ba zata iya ba.

"Maganar yaran nan ce Alhaji."

"Ina jinki Yaya."

"Ajiye 'yaya mata a gaba haka be kamata ba, ba daya ba har su biyar rigis, wanda duk cikin su babu wadda akayi wa aure ba zata zauna ba, abun nan kullum dashi nake kwana nake tashi, ya zama lallai duk su fito da miji ko da za'a yi karatun dai ya zama akwai maganar aure."

"Haka ne Yaya, dama dai akwai maganar Safiyya da Umaima a k'asa."

"Ah toh Masha Allah, ai ban sani ba, sai ayi abinda ya kamata, daga su sai azo maganar na k'asan."

"Wai da suma su fara jami'ar, tunda Maryam ta fara yanzu tana ajin farko, Amira da Hauwa'u kuma zasu fara suma bana,sai a hade su, su uku idan sun kai ajiye biyu ."

"Hakan ma yayi, amma ni ina da wata alfarma da nake nema a wajenka, buri na kenan idan ka cika min burin nan ka gama min komai."

"Babu alfarma a tsakanin mu Yaya, me kike so ayi? Fada kawai zakiyi ni kuma zan cika miki da yardar Allah."

"Magaanar yaron nan ce Tariq, da yarinyar nan Jiddah."

"Na'am!"

"Na duba na dubo gaba daya dangi kaf banga wadda ta dace dashi ba, sannan na gamsu da tarbiyyar yarinyar nan dari bisa dari, ina kaunar ta har cikin raina bana so mu rasa ta, shine nake so ka kaini wajen mahaifinta na nema wa Tariq auren ta."

"Toh Yaya, duk yadda kika ce haka za'a yi, da ni da yaran nan duk ikon ki ne."

Washe baki tayi cikin tsananin jin dadi tace
Chapter 22 · 0% Book details