← Book details Mayrah Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 145

Sashe 31

Mayrah Complete Hausa Novel · about 2 min read

A gigice Aunty Mariya ta shigo dakin Ammi tana kallonta tace "Ammi dama baƙi na shiga dakin Usman ne?" Ammi da lokaci daya hankalinta ya tashi ganin yanayin kanwar tata ta mike tace "Me ya faru Mariya?" Aunty Mariya da zufa ke karyo mata tace "Kinsan a dakinsa na ajiye jakata da akwatina tun ran da na zo..." Ammi tace "To me ya faru? Ai babu wanda yake shiga dakinsa a gidan nan sai Maheer shima ba ko da yaushe ba" Aunty Mariya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku Ammi ban ga zinarin akwatin lefen Mayraah da na saka a handbag dina ba na kai dakin dazu bayan da aka nuna ma Hajja" Sosai gaban Ammi ma ya fadi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aunty Mariya ta kasa ci gaba da tsayuwa ta zauna gefen gado tace "Yanzun nan na shiga dakin zan dau kudi a jakar naga babu kudin, kusan dubu talatin, nan na duba inda na ajiye zinarin da sauri, naga wayam babu an dauke har shi" Tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai, Ammi tsabar confusion ta kasa cewa komai, Aunty Mariya ta mike ta fice daga dakin tana kuka tace "Waye ya mana wannan aika aikan...."

*Start making ur payment before the end of free pages fans, kar a ji ni shiruuuu*

07087865788✍🏻
WhatsApp only
[6/4, 7:47 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻

10.....
Chapter 31 · 0% Book details