Sashe 22
Lu'u Lu'u Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri suka fara riga rigan bud'e mata k'ofar, d'aya a ciki ce ta d'ora hannu a k'ofar tare da danne wani mab'alli dake k'asan hannun k'ofar, bud'ewa tayi ta kauce mata a hanyar, ai kam ficewa tayi da sauri tana k'arewa tabkeken falon kallo, tsaye tayi ta shiga bin ko ina da kallo dan gaskiya d'akin ya birgeta sosai, tab'e baki tayi ta ci gaba da tafiyarta ta nufi inda take ganin nan ne mafitar.
Zata bud'e k'ofar kenan aka bud'e daga waje, cak ta tsaya ta zubawa mai shigowa ido, saidai sab'anin d'azu da fuskarshi ke d'auke da fara'a da annashuwa, yanzu kam fuskar a had'e take tam, yanda ta lura yana ta kallon bayanta ne yasa ta d'an juyawa, matasan matan nan ta gani duk sun zube k'asa kawunansu sadde jikinsu sai b'ari yake.
Juyawa tayi ta kalleshi sai kawai ta ja tsaki ta kula juyawa ta kallesu tace "Ku mik'e tsaye kunji, me ye na wani rusunawa har k'asa gaban mutum d'an uwanku."
D'aya a ciki ce tayi k'arfin halin d'aga kan ta ta kalketa sai kula ta sunkuyar, muryar Bukhatir ce ta sa ta juyo sanda yake fad'in "Me na fad'a muku a kan ta?"
Jiki na kyarma d'ayar tace "Yallab'ai mun yi iya k'ok'arinmu amma ta k'i..."
Kashe fuskarta yayi da marin daya sakaya girgiza kamar zata fad'i kwance, a mugun hassale ya nunasu da yatsa yace "Ba k'ok'ari ba, abinda yasa na d'auko ku shi ne dan..."
Gauuuu! Ayam ma ta d'auke fuskar Bukhatir da mari, a wani irin razane matan da kuma dattijon ne dake bayansu suka kalleta, dan su kam yanda suke girmama Bukhatir ko sarkin Egypt basa girmamawa haka, idonshi da suka kad'a sukayi jajajir ya d'aga ya kalleta, ido cikin ido suka kalli juna babu mai alamar rusunawa.
Tunanin hanyar da zai fara hukunta ta yake, tunanin kalar muguntar da zai mata yake, hasaso hukuncin da zai mata yake wanda zaiyi sanadiyar ta fara kakkarwa sanda ta ji sautin muryarshi, amma ikon Allah sai ya ji ya kasa aiwatar da komai, sai ya ji wani tausayinta a zuciyarshi ya malayeshi sanda suka had'a ido, sai kawai ya d'auke hannunshi daga kuncin yana murmushin takaici, dan ko iyayenshi ba zai tuna ranar da suka tab'a marinshi ba, ba dan kar ya zama mak'aryaci ba sai yace tun na k'uruciya wanda bai san anyi ba ma.
Sake kallon fuskarta yayi yana lashe leb'enshi kafin yace "Idan har kina son barin nan sai ki fara bin duk wani umarnin da zan gindaya miki."
A zabure tace "Kai a wa da zan bi umarnin ka?"
Sunkuyar da kai yayi k'asa yana murmushi kafin ya kalleta yace "Mijin da zai aureki."
Da wani mamaki tace "What!"
Ba tare daya daina murmushin ba yace "Ba zaki gane komai ba a yanzu, ki fara shiga ciki ki shirya dan ki samu ki suturta min jikinki, idan kin fito zamuyi magana dake."
Rumgume hannaye tayi tace "Kafin nan ka fara amsa min wad'annan tambayoyin nawa."
Girgiza kai yayi yace "Zafeera mahimmanci gareki a wajena, idan na mayar dake sarauniyata ko fuskarki bana so kowa ya gani, ta ya zan yarda ki tsaya a haka wasu na kalleki? Kin san wacece ke kuwa? Kin san girma da matsayin darajar da kike da shi? Allah ya karramaki dan haka zan tayaki karrama kan ki."
Cikin jin haushi tace" Tukuna ma wane banzan suna kake kirana da shi ne?"
Murmushi yayi mai kama da dariya ya juya zai fita yana fadin" Ki fara shiryawa sannan, zan amsa duk wata tambayarki."
Da wata matsiyaciyar harara ta bi bayanshi har ya b'acewa ganinta, juyawa tayi a masifance tace wa matan" Sai ku tashi mu tafi ko? Zaku tsaya k'aton gardi na dukanku kamar ubanku, wahe shi ma tukuna?"
Yanda tayi tambayar tana rik'e k'ugu yasa d'aya a ciki tace" Kamar d'a yake ga sarkin k'asar nan."
Yamutsa fuska tayi tace" Kama ne ma yake ba d'an sarkin bane, to wace k'asar ce wannan?"
D'ayar ce ta amsa da" Egypt."
Da mamaki ta kallesu tace" Egypt? Kuna nufin nan a Egypt nake?"
Jinjina kai sukayi hakan yasa ta ita ma ta jinjina kai ta k'arasa bakin kofar d'akin, bud'e mata sukayi ta shige suka bi bayanta.
*Khazira*
A kausashe ya buga teburin yana kallon Adah da kan shi ke k'asa kamar zai fasa d'akin yace "Ta ya ya haka zai faru? Sai da na ce zan je da kai na kuka tabbatar min da zaku iya, yanzu me kuka aikata kenan?"
Cikin girmamawa Adah yace "Ka gafarce ni sarki, mun tarar da hatsaniya ne a makarantar, ga dukkan alama wasu abokan gabar ne suka fara ganota shiyasa suka tayar da zanga zangar, da haka kuma sukayi nasarar d'auke mana gimbiyoyinmu."
Da wani sabon mamakin yace "Me? Gimbiyoyi kuma?"
Cike da d'ar d'ar yace "E shugabana, gimbiya Zafreen da gimbiya Zafeera sun b'ata a cikin tarzomar nan."
Da bala'in k'arfi sarki Musail ya cire kambun dake kan shi na tsantsar gwal daya sa aka k'era masa dan alfahari ya jefar a k'asa, a fusace ya juya b'angaren da Dhurani yake ya kalleshi, sai kuma ya tattare rigarshi dake jan k'asa ya tunkari hanyar fita, rufa masa baya sukayi inda waziri Khatar ke fadin "Sarki na, ka nutsu mu bi komai a hankali, na tabbata sarki Wudar ne ya d'aukesu, dan shi ke da burin son d'aukar fansa a kanmu."
Dakatawa yayi ya juya ya kalli Khatar da yayi maganar, jinjina kai yayi yace "In kuwa hakane sarki Wudar ya jaza ma k'asar sa yak'in duniya na uku, dan babu abinda zai hanani shiga masarautarsa sannan nayi fata-fata da su."
Dhurani ne yace "A'a sarkina, ba da haka zamu fara ba, kafin mu farmake su buna buk'atar samun tabbaci suna hannunshi, daga bisani koma menene sai ya biyo baya."
Adah ne yace "Hakane shugabana, dan na tabbata kamar yanda muke tsananin buk'atar gimbiya Zafeera, haka shi ma sarki Wudar, ba kuma zai kamata bane dan ya kasheta."
Cikin hassala yace "To yanzu ya zamuyi? Me ye mafita? A yanzu na fi buk'atar Zafeera a kan Zafreen d'in."
Adah ne yace "Wannan mai sauk'i ne shugaba na, zanyi magana da d'aya daga cikin masu lek'en asirinmu dake sintiri a cikin fadarsa."
Nunashi yayi da yatsa yace "Ka tabbatar nan da zuwa yammacin yau ka samo min masaniyar komai."
"Angama yallab'ai." Ya fad'a yana rusuna masa, saida suka ga ficewarsa kafin su ma duk suka bar wurin babu wani mai farin ciki da yanayin da yake ciki, dan su kansu sun fi buk'atar a samu Zafeera a kuma k'ara mata gudu zuwa lahira, dan su canjin da aka ce zata kawo shi ne yafi tsaya musu a rai, a ganinsu zata rabasu da addinansu ne, muk'amarsu da martabarsu, hakan kuma ba zasu bari ya faru ba mundun ran su.
Bai zame ko ina ba sai kurkukun sabah, tsabar a rikice yake bafade d'aya ne ya take masa baya zuwa can, hannunshi rik'e da doguwar rigarshi cikin sauri har suka isa can, mai tsaron d'akin da take ne yayi saurin bud'ewa sarki Musail ya shige.
Tana zaune rakub'e a jikin bangon ta had'a kai da gwiwa, idonta a rufe suke ruf dan ko ta bud'e babu abinda take gani face dishi-dishi da jiri, har saida ya isa gabanta ya durk'usa irin tsugunnon maza ya finciki gashin ta sakamakon gyalenta daya sauka a kan kafad'unta, da k'arfi ya d'ago kan ta har saida ta saki yar k'ara saboda zafin da ta ji, da k'yar ta d'aga idonta ta kalleshi.
Cikin gadara da cika baki ya mata murmushi yace "To ya kike sarauniyata?"
Kamar wacce ke cikin maye tayi luuu da idonta ta saki wani murmushi ita ma tace "Yan...da kake, haka na ke."
Tura kanta yayi da k'arfi har saida ta bugu ga bango ya fashe da dariya yace "K'arya kike sarauniyata, ni ina lafiya kuma ina cikin farin ciki."
Cikin layi tace "Kai ma ba gaskiya ka fad'a ba sarkina, hankalinka a tashe yake kamar yanda muryarka ke b'arin tsoro saboda ka fara jiyo k'amshin mutuwarka."
Da sauri ya mik'e tsaye yana lumshe idonshi dan gaskiya ta fad'a kam hankalinshi a tashe yake, cike da k'arfin hali ya kalleta yana nunata da yatsa yace" Ki zuba ido ki gani Juman, gobe warhaka ke da 'yarki duk zaku mutu, wannan alk'awari na ne."
Malalacin murmushi tayi ba tace komai ba har saida ya fita a wurin, a zahirinta kam bata nuna damuwa ko tsoron abinda ya fad'a ba, amma k'asan zuciyarta cike take da tsoro da alhini da zulumin abinda zai iya aikatawa.
*Larhjadin*
Ko da Umad ya isa ya samu Haman a masaukinshi fad'a masa abinda ya faru a makaranta yayi, saidai haka kawai ha k'i yarda ya fad'a masa batun auren nan, dan dama yayi ne saboda yasa hankalinsu Habbee ya kwanta su ji nutsuwar zuci su tabbatar tana hannu na gari, duk da dai yasan ba lallai sun yarda da shi ba musamman da suka san waye, amma dai yanzu a tunaninsu tana tare da shi kuma ba zai bari a cutar da ita ba kamar yanda ya fad'a musu, dan haka a sanin da yake da shi yasan aurenshi da Ayam zai cika k'aida ne idan da amincewar iyayenta mahaifa tunda suna raye, shaidu da kuma sadaki.
Cikin tashin hankali Haman yace "Me? Yanzu kana nufin ta sake b'ata kenan?"
Jinjina kai yayi ya kalleshi yace "Hakan alamu suke nunawa, amma a yanzu zamu iya cewa mun san inda take."
Cike da k'aguwa yace "A ina kenan?"
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Zan koma gida yanzun nan, ta hakane zan san inda take."
Da mamaki Haman yace "Kana nufin zaka koma masarauta kenan?"
Jinjina masa kai yayi alamar e, cikin d'ar d'ar yace "Bana tunanin sarkinmu ya sameta, me zai hana ka fara saka ido akan Bukhatir?"
Da wani mamaki Umad ya kalleshi ya d'aga labb'enshi da k'yar yace "Bamu tab'a maganar Bukhatir da kai ba, ya akayi ka san shi?"
Zaro ido yayi alamar firgici, a take kuma ya had'e komai ya saki murmushi yace "Haba dai, ka manta ka min maganar sa? Daga gareka na ji batunsa ai."
Zata bud'e k'ofar kenan aka bud'e daga waje, cak ta tsaya ta zubawa mai shigowa ido, saidai sab'anin d'azu da fuskarshi ke d'auke da fara'a da annashuwa, yanzu kam fuskar a had'e take tam, yanda ta lura yana ta kallon bayanta ne yasa ta d'an juyawa, matasan matan nan ta gani duk sun zube k'asa kawunansu sadde jikinsu sai b'ari yake.
Juyawa tayi ta kalleshi sai kawai ta ja tsaki ta kula juyawa ta kallesu tace "Ku mik'e tsaye kunji, me ye na wani rusunawa har k'asa gaban mutum d'an uwanku."
D'aya a ciki ce tayi k'arfin halin d'aga kan ta ta kalketa sai kula ta sunkuyar, muryar Bukhatir ce ta sa ta juyo sanda yake fad'in "Me na fad'a muku a kan ta?"
Jiki na kyarma d'ayar tace "Yallab'ai mun yi iya k'ok'arinmu amma ta k'i..."
Kashe fuskarta yayi da marin daya sakaya girgiza kamar zata fad'i kwance, a mugun hassale ya nunasu da yatsa yace "Ba k'ok'ari ba, abinda yasa na d'auko ku shi ne dan..."
Gauuuu! Ayam ma ta d'auke fuskar Bukhatir da mari, a wani irin razane matan da kuma dattijon ne dake bayansu suka kalleta, dan su kam yanda suke girmama Bukhatir ko sarkin Egypt basa girmamawa haka, idonshi da suka kad'a sukayi jajajir ya d'aga ya kalleta, ido cikin ido suka kalli juna babu mai alamar rusunawa.
Tunanin hanyar da zai fara hukunta ta yake, tunanin kalar muguntar da zai mata yake, hasaso hukuncin da zai mata yake wanda zaiyi sanadiyar ta fara kakkarwa sanda ta ji sautin muryarshi, amma ikon Allah sai ya ji ya kasa aiwatar da komai, sai ya ji wani tausayinta a zuciyarshi ya malayeshi sanda suka had'a ido, sai kawai ya d'auke hannunshi daga kuncin yana murmushin takaici, dan ko iyayenshi ba zai tuna ranar da suka tab'a marinshi ba, ba dan kar ya zama mak'aryaci ba sai yace tun na k'uruciya wanda bai san anyi ba ma.
Sake kallon fuskarta yayi yana lashe leb'enshi kafin yace "Idan har kina son barin nan sai ki fara bin duk wani umarnin da zan gindaya miki."
A zabure tace "Kai a wa da zan bi umarnin ka?"
Sunkuyar da kai yayi k'asa yana murmushi kafin ya kalleta yace "Mijin da zai aureki."
Da wani mamaki tace "What!"
Ba tare daya daina murmushin ba yace "Ba zaki gane komai ba a yanzu, ki fara shiga ciki ki shirya dan ki samu ki suturta min jikinki, idan kin fito zamuyi magana dake."
Rumgume hannaye tayi tace "Kafin nan ka fara amsa min wad'annan tambayoyin nawa."
Girgiza kai yayi yace "Zafeera mahimmanci gareki a wajena, idan na mayar dake sarauniyata ko fuskarki bana so kowa ya gani, ta ya zan yarda ki tsaya a haka wasu na kalleki? Kin san wacece ke kuwa? Kin san girma da matsayin darajar da kike da shi? Allah ya karramaki dan haka zan tayaki karrama kan ki."
Cikin jin haushi tace" Tukuna ma wane banzan suna kake kirana da shi ne?"
Murmushi yayi mai kama da dariya ya juya zai fita yana fadin" Ki fara shiryawa sannan, zan amsa duk wata tambayarki."
Da wata matsiyaciyar harara ta bi bayanshi har ya b'acewa ganinta, juyawa tayi a masifance tace wa matan" Sai ku tashi mu tafi ko? Zaku tsaya k'aton gardi na dukanku kamar ubanku, wahe shi ma tukuna?"
Yanda tayi tambayar tana rik'e k'ugu yasa d'aya a ciki tace" Kamar d'a yake ga sarkin k'asar nan."
Yamutsa fuska tayi tace" Kama ne ma yake ba d'an sarkin bane, to wace k'asar ce wannan?"
D'ayar ce ta amsa da" Egypt."
Da mamaki ta kallesu tace" Egypt? Kuna nufin nan a Egypt nake?"
Jinjina kai sukayi hakan yasa ta ita ma ta jinjina kai ta k'arasa bakin kofar d'akin, bud'e mata sukayi ta shige suka bi bayanta.
*Khazira*
A kausashe ya buga teburin yana kallon Adah da kan shi ke k'asa kamar zai fasa d'akin yace "Ta ya ya haka zai faru? Sai da na ce zan je da kai na kuka tabbatar min da zaku iya, yanzu me kuka aikata kenan?"
Cikin girmamawa Adah yace "Ka gafarce ni sarki, mun tarar da hatsaniya ne a makarantar, ga dukkan alama wasu abokan gabar ne suka fara ganota shiyasa suka tayar da zanga zangar, da haka kuma sukayi nasarar d'auke mana gimbiyoyinmu."
Da wani sabon mamakin yace "Me? Gimbiyoyi kuma?"
Cike da d'ar d'ar yace "E shugabana, gimbiya Zafreen da gimbiya Zafeera sun b'ata a cikin tarzomar nan."
Da bala'in k'arfi sarki Musail ya cire kambun dake kan shi na tsantsar gwal daya sa aka k'era masa dan alfahari ya jefar a k'asa, a fusace ya juya b'angaren da Dhurani yake ya kalleshi, sai kuma ya tattare rigarshi dake jan k'asa ya tunkari hanyar fita, rufa masa baya sukayi inda waziri Khatar ke fadin "Sarki na, ka nutsu mu bi komai a hankali, na tabbata sarki Wudar ne ya d'aukesu, dan shi ke da burin son d'aukar fansa a kanmu."
Dakatawa yayi ya juya ya kalli Khatar da yayi maganar, jinjina kai yayi yace "In kuwa hakane sarki Wudar ya jaza ma k'asar sa yak'in duniya na uku, dan babu abinda zai hanani shiga masarautarsa sannan nayi fata-fata da su."
Dhurani ne yace "A'a sarkina, ba da haka zamu fara ba, kafin mu farmake su buna buk'atar samun tabbaci suna hannunshi, daga bisani koma menene sai ya biyo baya."
Adah ne yace "Hakane shugabana, dan na tabbata kamar yanda muke tsananin buk'atar gimbiya Zafeera, haka shi ma sarki Wudar, ba kuma zai kamata bane dan ya kasheta."
Cikin hassala yace "To yanzu ya zamuyi? Me ye mafita? A yanzu na fi buk'atar Zafeera a kan Zafreen d'in."
Adah ne yace "Wannan mai sauk'i ne shugaba na, zanyi magana da d'aya daga cikin masu lek'en asirinmu dake sintiri a cikin fadarsa."
Nunashi yayi da yatsa yace "Ka tabbatar nan da zuwa yammacin yau ka samo min masaniyar komai."
"Angama yallab'ai." Ya fad'a yana rusuna masa, saida suka ga ficewarsa kafin su ma duk suka bar wurin babu wani mai farin ciki da yanayin da yake ciki, dan su kansu sun fi buk'atar a samu Zafeera a kuma k'ara mata gudu zuwa lahira, dan su canjin da aka ce zata kawo shi ne yafi tsaya musu a rai, a ganinsu zata rabasu da addinansu ne, muk'amarsu da martabarsu, hakan kuma ba zasu bari ya faru ba mundun ran su.
Bai zame ko ina ba sai kurkukun sabah, tsabar a rikice yake bafade d'aya ne ya take masa baya zuwa can, hannunshi rik'e da doguwar rigarshi cikin sauri har suka isa can, mai tsaron d'akin da take ne yayi saurin bud'ewa sarki Musail ya shige.
Tana zaune rakub'e a jikin bangon ta had'a kai da gwiwa, idonta a rufe suke ruf dan ko ta bud'e babu abinda take gani face dishi-dishi da jiri, har saida ya isa gabanta ya durk'usa irin tsugunnon maza ya finciki gashin ta sakamakon gyalenta daya sauka a kan kafad'unta, da k'arfi ya d'ago kan ta har saida ta saki yar k'ara saboda zafin da ta ji, da k'yar ta d'aga idonta ta kalleshi.
Cikin gadara da cika baki ya mata murmushi yace "To ya kike sarauniyata?"
Kamar wacce ke cikin maye tayi luuu da idonta ta saki wani murmushi ita ma tace "Yan...da kake, haka na ke."
Tura kanta yayi da k'arfi har saida ta bugu ga bango ya fashe da dariya yace "K'arya kike sarauniyata, ni ina lafiya kuma ina cikin farin ciki."
Cikin layi tace "Kai ma ba gaskiya ka fad'a ba sarkina, hankalinka a tashe yake kamar yanda muryarka ke b'arin tsoro saboda ka fara jiyo k'amshin mutuwarka."
Da sauri ya mik'e tsaye yana lumshe idonshi dan gaskiya ta fad'a kam hankalinshi a tashe yake, cike da k'arfin hali ya kalleta yana nunata da yatsa yace" Ki zuba ido ki gani Juman, gobe warhaka ke da 'yarki duk zaku mutu, wannan alk'awari na ne."
Malalacin murmushi tayi ba tace komai ba har saida ya fita a wurin, a zahirinta kam bata nuna damuwa ko tsoron abinda ya fad'a ba, amma k'asan zuciyarta cike take da tsoro da alhini da zulumin abinda zai iya aikatawa.
*Larhjadin*
Ko da Umad ya isa ya samu Haman a masaukinshi fad'a masa abinda ya faru a makaranta yayi, saidai haka kawai ha k'i yarda ya fad'a masa batun auren nan, dan dama yayi ne saboda yasa hankalinsu Habbee ya kwanta su ji nutsuwar zuci su tabbatar tana hannu na gari, duk da dai yasan ba lallai sun yarda da shi ba musamman da suka san waye, amma dai yanzu a tunaninsu tana tare da shi kuma ba zai bari a cutar da ita ba kamar yanda ya fad'a musu, dan haka a sanin da yake da shi yasan aurenshi da Ayam zai cika k'aida ne idan da amincewar iyayenta mahaifa tunda suna raye, shaidu da kuma sadaki.
Cikin tashin hankali Haman yace "Me? Yanzu kana nufin ta sake b'ata kenan?"
Jinjina kai yayi ya kalleshi yace "Hakan alamu suke nunawa, amma a yanzu zamu iya cewa mun san inda take."
Cike da k'aguwa yace "A ina kenan?"
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Zan koma gida yanzun nan, ta hakane zan san inda take."
Da mamaki Haman yace "Kana nufin zaka koma masarauta kenan?"
Jinjina masa kai yayi alamar e, cikin d'ar d'ar yace "Bana tunanin sarkinmu ya sameta, me zai hana ka fara saka ido akan Bukhatir?"
Da wani mamaki Umad ya kalleshi ya d'aga labb'enshi da k'yar yace "Bamu tab'a maganar Bukhatir da kai ba, ya akayi ka san shi?"
Zaro ido yayi alamar firgici, a take kuma ya had'e komai ya saki murmushi yace "Haba dai, ka manta ka min maganar sa? Daga gareka na ji batunsa ai."