← Book details Lu'u Lu'u Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 86

Sashe 15

Lu'u Lu'u Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon Umad tayi irin kallon tsanake ta sauke numfashi tace "Wane addini ne wannan? Ya ake a shiga? Ina so ni ma na zama d'aya daga cikin mabiyansa, na fi son ubangijin da zan bautawa ya zama mai jin buk'atuna, zan so ubangijin da zan bautawa ya zama shi ne ya samar da ni ba wai wanda kakanninmu suka samar ba, zan so ubangiji na ya kasance a tare da ni a ko yaushe ba wai sai na sha wahalar d'aukarsa a cikin jakata ba, kuma ina so ubangiji ya zama mai amsa rok'ona a sanda na rok'eshi, kuma wanda ba ya gajiya da amsa buk'ata ta bare ya min gori wata rana, wannan ubangijin nake da buk'ata, shiyasa ban tab'a bautawa kowa ba."

Gyara tsayuwa Umad yayi sai ma ya rasa bakin magana, kallonta kawai yake ita kuma tana ganin haka ta kyab'e baki tace" Haka dayawa ke ta fad'a, wai ina tsoratasu, wasu ma sun daina kulani saboda launin ido na da kuma wasu abubuwan, kai ma idan ka tsorata zan saka a layin ragwayen maza."

A karon farko da murmushi ya sub'uce masa a gabanta, sosai yayi murmushi har hak'oransa na bayyana a fili, ganin haka sai ita ma ta saki murmushin tace" Karka damu malam, ba zan yarda kowa ya ji major Umad matsoraci bane."

Iskan daya fara kad'awa mai k'arfi had'e da k'ura da kuma k'arar jirgi a sama yasa Umad d'aga kan shi, ita ma d'aga kan tayi sama suna kallon jirgin helicopter d'in, da kai ya mata alama yace" Muje."

Zaro ido tayi tace" Kai ka kira jirgi? Ina zamu je?"

Kallon shegantaka ya mata yace" Ba zaki kike son gani ba?"

Jinjina kai tayi alamar e, saka gilashin shi yayi a ido hakan ha k'ara fito masa da kyawusa, hannun hagu ya mik'a mata yace" Muje to."

A hankali ta d'aga siririn hannunta na dama ta d'ora akan tafin hannun Umad, da k'arfi ya jimk'e hannuta sakamakon shock d'in da ya ji irin na ranar, sai ya bar hakan a matsayin dan bai cika tab'a jikin mace ba tunda ai ita bata ji komai ba a ganinshi.

Fuskarta ya kalla da kyau yana sake nanato kalaman malaminshi akan yarinyar daya fito nema, musamman inda yake fad'in _"Akwai b'oyayyar jarumta a tare da ita, abinda ya cancanci ya bata tsoro ba shi ke tsorata ta ba, wanda kuma kai zai iya kayar maka da gaba, sai ka ga ita abin ado ne a gareta..._"

Tabbas ya fara jin wani abu a kan yarinyar nan, inba haka ba ta ya zata amince da shi haka a sauk'ak'e, lallai da ita xe wacce yake nema sai yace mata "Jarumtarki ta ban haushi, amma kuma raunin da kika nuna na yarda da ni ya birgeni."

Jan ta yayi suka nufi inda jirgin ya tsaya, suna isa k'ofar dama a bud'e take, taimaka mata yayi ta fara shiga sannan ya shiga shi ma, d'amara suka d'aura a k'ugunsu, tashin jirgin aka fara su kuma suka fara k'ok'arin saka abun sauraron magana a kunnayensu saboda basj damar jin maganar juna ba tare da k'arar iskan ta kawo cikas ba.

Zura kan ta tayi ta d'aya k'ofar tana hangen k'asa ta taga, murmushi ta shiga saki ita kad'ai musamman yanda ta ga bishiyu na kad'awa su kuma suna k'ara haurawa sama.

Kafad'arta ya daddab'a tana juyowa yace "Kin tab'a shiga jirgi ne?"

Girgiza kai tayi tace "Ban tab'a tsayawa gani ga shi ba sai yau."

Girarshi d'aya ya d'aga sama da mamakin kuma shi ne babu tsoro a tare da ita? Tafiya suka yi mai nisa saidai duk a cikin dajin suke, saida suka kai inda aka saka allon sanarwa dan daga nan zuwa inda mutum zai k'ara a cikin had'ari zai yi shi, dan dabbobi ne iri iri masu cutarwa a wurin.

Jami'in tuk'in jirgin ne yace wa Umad "Yallab'ai a shirya sauka mun iso."

Kallonta Umad yayi yace "Kin shirya?"

"E yallab'ai." Ta fad'a da karsashinta, jinjina kai yayi sannan ya ba matuk'in umarnin sauka, saida ya tabbatar sun tsaya sannan ta ga ya zura hannu a k'asan kujerar da yake zaune ya d'auko bindiga, wacce ke k'ugunshi ta aiki ya aje ya duba alburansan waccen ya d'auka, d'anata yayi ya saita mata komai tana kallonshi baki sake, yanda yake wasa da bindigar sai ta ji ya birgeta, kallonta yayi yana shirin fita yace "Mu je."

Shi ne ya fara fita, za ta diro shi kuma daidai ya juya tare da rik'o k'ugunta da duka hannayenshi bayan ya soka bindigarshi a k'ugu, cak ta ji ya d'agata ya sauko da ita, kunya ce ta rufeta dan hakan bai tab'a faruwa da ita ba, kaa had'a ido tayi da shi haka shi ma sai ya ji kamar yayi gaggawa a lamarin.

Bindigar ya ciro sannan ya kalleta da kulawa ya shiga mata kurmanci wanda dama dole suke koya saboda irin haka, dan wata dabbar sauti zata ji ta farmake ka wata kuwa sautin tafiyarka ma, jinjina kai Ayam tayi dan ta fahimci abinda ya fad'a mata wato ta biyoshi a baya a hankali sannan ta kula.

Cikin sand'a suke tafiya Umad na gaba tana binshi a baya sai kalle kalle suke, k'wari da k'ananan dabbobi kam suna ta had'uwa dasu wanda ba sa cutarwa, suna cikin tafiyarsu a hankali cikin ciyayi koraye ya mata alama da hannu cewa ta tsaya. Tsayawa kam ta yi tana lek'awa ta ga me ya gani, a wuyanta ta ji motsi daf da hular kan ta, da sauri ta zura hannu da niyyar d'an sosawa, tudun abun da ta ji mai tabbatar mata da k'waro ne yasa bata ankara ba kuma bata shirya ba ta kwamtsa k'ara iya k'arfinta.

*Alhamdulillah*
01/01/2022 脿 11:33 - Mom Khalid: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
_*LU'U LU'U*_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�

*NA*

_SAMIRA HAROUNA_

_SADAUKARWA GA_

*'YA'YA NA*

馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃

鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah, hak'ik'a Allah abun godiya, bayan share wata uku na dogon nazari da samun gamssashen hutu, hazik'ar ta sake dawo mu ku da wani sabon nagartacce kuma zak'wak'urin labari mai taken *LU'U LU'U*, kai dai daga jin lu'u lu'u kasan akwai magana a ciki, rubutun littafin zai zo muku daga alk'alamin marubuciyar nan dai da kuka sani mai *Badak'ala*, *Jihadi* da kuma *Matar mutum*,ma'ana dai ta ku *Samira Harouna* (Meeranku馃榿, Yasin ta ku ce), nasan kunsan labaran kuma kunsan me suka k'unsa, Dan haka zan ce ku garzaya da gudu Dan ku samu rabon karanta n'a ku Lu'u lu'u._

_Farashin mai sauk'i ne masoya, ga duk mai son ta samu n'a ta zata biya naira 200 kacal, ga Yan k'asa ta Niger kuma abar alfahari na zaku biya 400f cfa kawai, soyayya Dan Allah tana saka komai, k'awaye na ku zo mu tafi tare da ku, Dan ba zan Bari a barni a baya ba._

_Yan Niger zaku tura katin Airtel ko Moov akan wannan lambar, *94-98-56-52* sai ku tura shaidarku ta wannan lambar *88-35-50-01*._

Yan Nigeria kuma zaku tura ta wannan asusun *3120244299*
Amina Maikudi Abdullahi
First bank. ko kuma Recharge card na Mtn Akan lamba
080-38-85-69-44.

_Masoya Yan mutan Niger sai mun ji daga gareku, mutanenku ne dai._

_Bismillahir rahamanir rahim_

*9*

Da fari kam zabura Umad yayi dan abun bai yi tsammaninshi ba, bugu da k'ari kuma k'arar a cikin kunnenshi na hagu ta sauka, amma yana ankara a cikin salo da k'warewa yayi azamar had'ata da bangon da suke tsaye kusanshi, hannu d'aya yasa ya rufe mata baki d'aya hannun dake rik'e da bindiga kuma ya zagaye k'ugunta da shi, duk da idonshi cikin gilashi suke amma yanda tayi shiru dole suka k'urawa juna ido, d'an motsa wuyanta tayi tana lumshe ido, a hankali ya d'auke hannunshi daga bakinta ya mayar kan wuyanta, yana jin ya tab'a abu yayi k'ok'arin cireshi a jikinta, gam ya ji alamar k'waron mai kakkausan k'afafu ne da tsini hakan yasa ya mak'ale mata a dogon wuyanta.

Yatsu biyu yasa still idonshi cikin na ta duk da ita ba wani ganin na shi take sosai ba, tana dai hangen kamar ita yake kallo kuma kamar ba ita yake kallo ba, cire k'waron yayi tamkar fara ce ta lak'e mata a jiki.

Wani numfashi ta sauke a take idonta suka kawo ruwa dan koma dai menene tabbas ya cijeta, lumshe ido tayi ta sauke kan ta k'asa, k'waron ya nuna mata cikin masifa yace "Dubi, k'waron da zai iya wucewa ta hudar hncinki, shi ne fa ya hau jikinki kika shaidawa duka jejin nan cewa mun shigo, amma a haka kike cika mana baki ke zaki kike son gani."

Kallon k'waron tayi bak'i wulik da shi kamar suffar gizo kuma kamar hankaka, marairaiccewa tayi tace" Sorry."

A tsawace yace"Shet up, kika sake min maganar zaki wallahi sai na fasa bakinki da hannun bindigar nan."

Turo baki tayi gaba alamar rashin jin dad'i, kafin ta shirya yin wani abun Umad ya fizgi hannunta da k'arfi suka juya dan komawa inda suka fito yana fad'in" Dole muyi gaggawar barin nan, dan hankalin kowace dabba yanzu ya tashi da tunanin an shigo farautarsu, dan haka su ma zasuyi k'ok'arin farautar rayuwarmu, ni kuma ban shirya rasa raina tare da ke ba."

Bin shi take kamar zata fad'i k'asa dan sosai yake jan ta, ba tace komai ba face biyarsa da take kawai, sunyi kusa da inda allon sanarwar nan yake na a kula akwai had'ari a nan daga cikin ciyayin suka ji motsi, cak ya tsaya tare da sakin hannunta, d'ora hannunshi yayi a kan k'irjinta da niyyar mayar da ita baya, dan ya fi ta tsayi sosai a iya d'agawar da ya ma hannunshi dole kan k'irjin zai sauka.

Da k'arfin tsiya ta buge hannunshi tare da saka hannayenta ta rufe nonuwanta tana fad'in "Me ye haka?"

Kan shi kawai ya juyo ya kalleta ya kuma kalli k'irjin, dan shi sam bai ma san me ya tab'a ba bare ka tabbatar da niyyarshi, juya kanshi yayi ya sakar mata tsaki yana girgiza kai yace "Allah tsare ni, b'erayen?"

Cike da masifa ta shiga gatsina baki tana fad'in "B'erayen, amma a hka suka birgekahar kake k'ok'arin yi min..."
Chapter 15 · 0% Book details