Sashe 55
Duba Min Baya Fakon Biri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
lanqwashe yace "Bibi na fiki jin rashin dadin dabi'un sultana,na kuma taras da ku ba masu goyon baya na ba wajen maidata hanya,bazan canza ba indai sultana ba zata canza ba,dole ta koma kamar kowanne yaro dake gidan nan" kai bibi ta gyada,tun ba yau ba tasan irin nasa halin. Yan a da tarin kafiya da taurin kai akan dukkan abinda ya sanya a gaba ko ya furta zai aikata. Fadin zaiyi abu yana da wuyar ji daga bakinsa,amma muddin ya furta din to babu sauyi,komai dadi komai wuya. Sake gyara goyon school bag dinta tayi dake bayanta,tana jin kamar ta fada dakin ta rufe yaa maina da duka,ai ita batasan haka yayi nisa wajen qinta ba,batasan haka zuciyarsa tayi zurfi wajen son quntata mata ba,lallai Allah baya bacci da har kunnuwanta suka jiye mata komai. Indai yana tunanin iya tsare gidansa,daci da baqin ransa,fada da hararraminsa zai bashi abinda yakeson yaga ta koma din to tabbas zata tabbatar masa ita din ba tsoronsa takeyi ba,kuma bai isa tabuka komai ba "Sultana kibi a hankali,kinfi kowa sanin waye fr re" wani sashe na zuciyarta ya gaya mata sanda take qissima da irin salon da zata shiga falon "Idan garwashi ne shi ni wuta ce" ta baiwa kanta da kanta dama zuciyar dake gargadinta amsa,bata kuma sake tsayawa sauraron kowacce shawara daga zuciyarta ba ta sanya kai falon da waqar data zame mata madadin sallama. Idanunta saman fuskarsa tana nazarin furucinsa daya bayan daya,dai dai sanda siririyar muryarta dake cike da tsiwa ta isa ga kunnuwansu tana rera waqar ado isa gwanja _Allah ka aika munafukinmu qarshen nesa,tafiyar qasa koda lafiya ko babu,kaishi garin da ko kuyanga babu,barshi a can da arziqi ko babu,ni nasha tabara nasha yasin,kuma nasha rigakafin alatsine_ . Sai ta juya zuwa waqar wani mawaqin qasarsu ta nijer _Munafuki Alla kasheshi,koda safe koda rana ko ma dare ne_ Tana maganar ne kanta yana kallon lobby na dakunansu tana kuma nufar can,tamkar batasan da zaman mutane a wajen ba. Mutuwar zaune bibi tayi,ana kukan targade ga karaya ta samu,ana neman gyara ga sabon ruwa ya ballo. Ko waye kai,komai girmanka muddin ba iyayensa ba baka isa ka ratsa waje bakayi masa sallama ba,kamar yadda duk yadda yake da buqatar shiga guri muddin ba'a amsa sallamarsa an kuma masa izini ba yana juyawa ne ya koma inda ya fito. Wannan ya samu asali ne daga cikakken karatu da tarbiyyar daya samu daga islamic school din da yayi masu kyau a Nigeria. Har ta kusa shigewa ya kirayeta cikin tsawa,kaman ta wuce ciki sai narkakken tsoronsa dinnan da take qoqarin binnewa ya motsa mata. Tunga taja ta tsaya kana ta waiwayo tana dubansu ba tare data iso inda suke ba "Koma ki yima mutane sallama" idanunta masu kama da digon zaiba ta dan juya tana bata fuskarta,ta motsa qaramin bakinta dake cike da tsiwa tace "Nifa na riga nayi sallamata ehe" daga wannan ta juya tana shirin wucewa dakin tare da sake maimato waqoqinta a sarari sosai saboda saqon ya isa gareshi. Wata baqar zuciya ce ta motsa masa,tabbas sultana dashi take,shi takewa wadannan waqoqin. Uwa uba yau shine zaiyi mata magana tasa qafa ta shure?,tama maidashi mahaukaci?. Daga sultana har bibi babu wanda yasan lokacin da ya isa dakin. Dai dai sanda take wurgi da komai na makarantarta kamar yadda ta saba tana sake sakin waqoqinta cikin harshen faransanci,ranta fes tana jin ta fara samun nasarar rage haushinsa cikin ranta. Cire hijabinta yayi daidai da dauketa da marin da yayi,babban dukansa shine marin,bai iya wani duka ba idan ransa ya baci bayan shi. Sanin darajar da fuska take da shi ya sanya bai cika yin dukan ba,zaiyi wuya kaga ya daki wani cikin qannensa,amma wajen iya bada horo su kansu sun tabbatar babu na biyunshi kaf cikin family. Wata irin gigitacciyar qara ta saki tana dafe kuncinta da hannayenta bibbiyu ba tare data fuskanci meye ya sameta ba. Sautin muryarsa saman kanta kwanyarta tayi saurin ingizo mata me yake faruwa da ita,saidai kafin ta gama daidaita tunaninta ya sake aje mata wani Marin hade da qatotuwar tambayar da batasan da wanne zataji ba,marin ko amsa masa tambayarsa "Saikin gayamin wanene munafukin cikin gidan nan" yayi maganar yana zare belt din dake jikinsa. Dukka jikinta rawa ya fara yi,saboda ganin fushi muraran saman fuskarsa,uwa uba tunda take bazatace ga ranar da aka sanya madoki aka daketa ba,shine ma mutum na farko kaf fadin rayuwarta da ya taba taba lafiyarta tunda tazo duniya,wannan ya sanya take matuqar razana duk sa'ilin da ya shimfide mata dogayen yatsunsa saman fuskarta "Waye munafukin nace?!" Ya maimaita tambayarsa yana ware mata lion eyes dinsa da suka sake gigitata,sai ta ware dukka muryarta tana qwalawa bibi da tanja kira "Wayyo Allah na bibi,zai kasheni,zai kasheni,wayyo na shiga uku" Yatsansa ya dora saman lips dinsa yana sake fidda mata idanunsa dake danqare da bacin rai "Kika sake buda bakinki a nan sai na miki dukan da ba zaki qara iya daga yatsarki ba,tais toi idiot(shut up idiot)!" Ya qarasa fadi a tsawace. Dole qanwar naqi ta sakaya ihunta,duk da tana jiyo bibi na bugun qofar hadi da kiran sunanshi da bashi umarnin ya bude,saidai kuma bata da ikon cewa komai. Stool dinta ya jawo ya zauna a gabanta,ta qanqame jikinta guri daya tamkar me jin sanyi. Ba sanyi takeji ba,tsantsar tsoro ne ya sanya jikinta ke shivering,amma batason yaga hakan daga gareta,hawaye kwance saman fuskarta,ilahirin fuskar tata radadi take mata "A fr re dinki kika sanni ko?,to daga yau ki saka a ranki maina nake a wajenki kamar yadda nake a wajen kowa na gidan nan,zan fiddo miki ainihin kalata tunda na fuskanci kin zama graduate a fannin rashin kunya [3/3, 20:08] Aishatu Aliyu Musa : DUBA MIN BAYA FOKON,,,, ZAINAB IDRIS MAKAWA GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , , YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , , HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO. Haduwana da hauwa a yanzu yasa na dan sake wani lokaci har banson mu rabu don tana sakani dan walwala idan muna tare kobaka so hauwa saita saka magana ko dariya. Sannu a hankali wata yar sokoto itama ta hade damu saidai ita auren ta ya mutu a lokacin duk da tana cewa damu zata komawa mijinta ai don ko yaushe tana maganan hakan haihuwanta daya dashi suka rabu ta dalilin kishiya sai yayanta ya daukota zuwa kano ya kadata karatu a nan kano din. Sai Fatima kawata ta secondary da wani lokaci tana zama damu itama don haka ko ina mu hudun zaki ganmu a tare don department din mu daya ba yawa ke garemu ba kuma dama hakan yasa muke tare da juna. Duk zaman mu basu taba sanin cewa ni matar aure bace don ban fada masu komai ba akaina sun dai san cewa ni yar jahar katsinace kawai . Su a zatinsu ina zama da yan uwanane kawai a nan kano din duk da suna ganin malam isah driver na zuwa daukana kullum amma basu kawo zancen aure a gareni ba. Don a lokacin bamu da lokaci karatun mu yadau zafi zamuyi jerabawan canza ajine ba wani wasa ko shiririta agaremu gashi sun gane ina da fahinta don haka suka kara like min muka hade sosai dasu. Ban kiran kowa a gida yanzu saidai su kirani don tun ranan da nakira mum ta furta min kunyanama take ji a yanzu don bata san me zata iya furta min ba na daina kira saidai su idan sunjini shiru daddy kesa ta kirani mu gaisa. Ya ban hakkuri yace na kara hakkuri akwai abinda yake jira yasa ban jisu ba amma insha Allahu komai zaizo daidai a garemu nikan ban damu ba don yanzuma da nake zaman kaina nafi jin dadin karatuna tunda banda wani takura . Bamai sakani aikin komai gidane ni kadai ke cikinsa don haka kwana bibiyu nakeyi na bata lokaci tunda safe na gyara gida kafin malam isah yazo daukana. Dan abinda zanci kuma wani lokaci a waje muke tsayawa hanya in saya in dawo gida dashi ba sai nayi girki ba a ranan gashi ban saka damuwa ba yadda mutane suke zata sai wani haske da kyau dana kara a yanzu din. Ma,ana dai sannu a hankali na fara gogewa ina ganin kwaliyan gayun makaranta yadda suke dresse dinsu don haka nima ban bari an barni a baya ba duk damu kayan mu da lap cort a sama don a bambantamu da sauran dalibai. Da farko nayi rakin karatun nawa saidai yanzu ina jin dadinsa yadda muke samun shawara da kulawa yadda ya kamata sai nake jin kara son karatun likitan a yanzu. Mahaifana da suka haifeni kuma kusan ko yaushe da dare idan na dawo nakan kirasu a waya mu gaisa mukan dade da baba yana ban magana har banson ya dauko min zancen auren hafiz dake kaina duk lokacin daya dauko min wai yana ban hakkuri nakan shiga wani yanayi na daban a lokacin. Muyi hutu da kyar duk da hutun ba wani mai yawa bane dai amma mun samu dan sauki a lokacin saida nayi sati daya a gida ban leko ko get ba iyakata da waje in nafitowa maigadin gidan da abincinsa shine fitana. Ranan na shirya don in kai masu ziyara gida a karo na farko ke nan wata shidda da auren mu kuma ke nan don a gaskiya nayi tunane kada wanan auren ya tabarbare muna zumuncin mu da iyayyena. Tsab na shirya nayiwa malam isah waya tunda dare yazo da safe ya daukeni saiko gashi don inason inyi sammako in samu daddy a gida kafin ya fita kasuwa. Don har zazzabi daddy din yayi amma yace kada a fada min shine baba ya kirani yana sanar dani don haka na shirya don zuwa gida din bayan nayi tunane akai. Cake da zubo da kunnu ayyah mai dadi na hada nasa a basket sai gida