Sashe 39
Duba Min Baya Fakon Biri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
abinsa yaci saida ya koshi. ZAINAB IDRIS MAKAW [2/18, 19:48] Maman K: DUBA MIN BAYA FOKON,,,, ZAINAB IDRIS MAKAWA GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , , YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , , HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO. Fitowan jerabawan mu ya fara jagula komai a rayuwana don ko jerabawa ya fito kowa na kururuwan jerabawan yayi kyau kamar yadda na fada da baya gareki. Wanan yasa Hjy mum samun daddy akan zancen karatuna tunda jerabawa yayi kyau sosai zan iya shiga jami,a ai dan dagowa daddy yayi zaune kafin yace ina sane da hakan a raina kubura. Saidai tsarin nawa a yanzu so nake ya canza dubaga lamarin Nafisa agidan nan ko ban fada ba kinsan dai abin yana damuna azuciya zamanta haka a gida babu aure yana cimun zuciya wallahi. Donshi nake son na koma tsarin iyayye a yanzu bance ya mace bata boko a gidana ba a,a zasuyi amma iya secondary zasu tsaya agidan nan na aurar dasu su karasa karatun su can a dakunan mijinsu idan suna son haka ban hana ba kuma zan taimaka idan ya kama. Wani ajiyan zuciya Mum ta sauke kafin tace wai akwai matsala yadda mama ta kwallafawa karatun nan rai yanzu kuma ace aure za,ai mata da rana tsaka gaskiya akwai matsala don ita ko irin dan saurayin nan da sukeyi sam bata da ra,ayin hakan ita. Wanan ba matsala bane don lamarin na riga dana tsara komai azuciyana lokaci kawai nake jira in gabatar maku kudasu ku sani don haka zancen karatu a yanzu a jayeshi kawai sai indan sunyi aure . Mum tayi shiru a wajen tana faman tunanen abinda zata fada min da yadda zan dauki zancen kafin ta motsa tace duk da hakan Alh ai za,ayi sayen form din kada shekara ya wusu kuma ko ? Wanan abari sai nayi tunane zan zauna da yan uwana mu tatauna akai muga yadda ya dace ayi din tace Allah yasa muji alheri tana nisawa ya amsa da amin shima. Sam mum bata fada min komai ba taja bakinta tayi shiru saidai abin yana ci mata zuciya har dai idan ina haukana ko shirme kome aka ban zan boye nace saina fara fita makaranta zanyi amfani dashi. Nikan bata tausayi da har yakai ta kasa boye hakan azuciyanta don yanayinta kan canza idan ina zancen karatun har yakai nima na fara gane hakan. A yanzu don nakanyi tunanen ko bata aon nayi karatun ne yasa haka to me zaisa haka kuma bayan itace ta kara karfafamin rai ga wanan karatun har ta zaba min likita take son in zama ba lauya ba kamar yadda nace. Ranan muna hira da ya Nasir daya samu aiki a world bank branch dake nan Nigeria wanda dan uwansa yashiga ya fita aikin ya samu ta bin hanyoyim ganin manya har abin ya tabbata yanzu suke zance a kai da mahaifiyarshi. Nikan na huta ai mum idan na kare karatuna ba saina sha wahalan neman aiki ba tunda gani dasu yaya a hannu kalloni mum tayi tana murmushi tace aikan ke ai yar lelece mama don dole su samo maki aikima ko ban raye kuwa. Balle kina raye mum sai tsufa na futuf zai rabamu insha Allahu sai na kaiki makka da kudi ko in daukeki mu koma wajena ki huta da hjy mummy da fadanta. Humm wawiya shi mijin naki zai yarda da hakan ai saiki bari sai kinyi karatun kafin ki tsara haka bayan daddy yace baku karatu aure zai maku dukkanku. Wani zabura nayi don gabana daya fadi lokaci guda nace aure na kallo mum din nace wai mum haka daddy yace ? Tace rabu dashi kinji ai harshi idan yana ganin ya tsirane to baka tsira ba ai don gaba dayan ku yace zai aurar dakune ba matan ba kawai da kake mata sheri. Wani abu naji ya fito daga kafana zuwa kai lokaci daya na ji numfashina yana batun dauke min ga mum dake kusa dani ta fara gano hakan nan ta fara kiran sunana da dan karfi tana fadin mama fa ke mama yau ga tsiya. Kaima Nasir da sheri kake meya kaika fada mata wanan zancen yanzu bayan kansan halinta akan karatun nan yadda ta kwallafa rai na fadama ina son har Alh ya saukone in rarasheshi ko zai yarda ta fara . Kai kuma yanzu kazo ka fada mata haka kai tsaye baka kyauta min ba gaskiya ka tashi ka fita ka bamu wuri tunda banga abinda kake nema a nan yanzu ba. Zubur na samu wani karfi yazo min na mike nashige daki sai lokacin na samu kuka yazo mi mai karfi ina toshe bakina kan hakan amma ban iya controlling din kaina dole sauti ya fito waje. Hankalim mum ya tashi sosai bata iya shigowa dakin ba ranan nayi bakin ciki da nadaman kasancewana a karkashinsu nayi nadama babba a ranan. Don da ace a karkashin kulawan iyayyena nake saibidan nace boko ya isa a bangarena don baba yai min alkawarin hakan tun ina karama wanan nahau na zauna a kai zancen mahaifina din sai gashi kuma yan zun yadda abin ke nema ya kasance dani kuma. Haka na dauki tsawon lokaci mai nisa ina fama da kuka da tunane azuciyata har da tambayan kaina nayi towama zan aure ni da a tsawon tarihina ban taba yin wani saurayi ba kona wasa balle na gaskiya. Wasa wasa har zaxzabi mai karfi ya sauka min ajiki nan na koma dunkule jina shiru da mum tayi ta leko bayan azahar tana fadin wai har yanzu fushin karatunne akeyi. Rufe ta hangoni cikin bargo a kwance ikon Allah abin har yakai ga rufa hakane takaraso gareni tana fada tare da yaye bargon ido ya kadai min yayi ja sai rawan sanyi nakeyi ina neman taimako alokacin. Salati ta saka tana fadin yau me zangani haka daga zancen kararu ki fadi ciwo haka meke damunki kuma haka lafiya lau kika tashi fa dazun ? Aikuwa wani aman kummalone yazo min lokaci guda na yunkura da niyar zuwa bayi ai kafin nakai na sake har da guntun boli a wajen amai sosai nayi dan kunun tofiyokan danasha duk shi na amaye zalla alokacin. Aiko ba zan gani ni kadai ba ta fada tana danna wayan dake hannunta anty nafisa ce ta kira lokacin suna tare da Dada a part dinta itace suka shigo da sauri tana fadin. Hjy Mum maman Amir ba lafiya kuma gaskiya banji duriyanta ba yau mum dake duke tana goge aman ta dago tana fadin kedai bari Nafisa. Lafiya kalau fa muka tashi da yarinyar nan me shegen bakin surutun nan Nasir ana zance yake fada mata wai Alh yace ba zasuyi karatu ba ai aure zai masu. Shinefa zancem har yakaita da nadewa yanzu haka ni abin mamaki ma ya ban na rude kar yar mutane ta mutu nace barin kira mutanen gida su sheda. Ai ba a mamaki da ikon Allah Dada dake bayan anty nafisa ta fada sai gani na bude bayin na fito ina makyarkyatan dari da sauri na nemi abin rufa na dunkule kaina. Sama sama nakejin zantukansu akaina haka baisa na iya mikewa sai tashin hankali da zancensu ya kara ingizani ciki a lokacin donko Dada sai fada takeyi tana fadin. Akan karatun boko da iyakarsa duniya za ki nemi kashe kanki a banza ki mutu mushe ki mutu kafira yarinya haka da shegen son karatu nagabama da sukai karatun meya tsinana masu ? Nidai naji anty ta tallabani mun fita sai wajen mota wai ashe har suma nayi me karatu abin zai baki mamaki kan zancen karatu har dasu suma kuma. Abindaya kara firgitani shine zancen aure wazan aura ko nima irin auren da nake jin labarin cewa iyayyen mu sunayi a family din mune yanzu zai hau kaina . Wanan ne har ya kaini ga fita hankalina na dan wani lokaci na some harda su zazzabi mai karfi wasa wasa sai gashi an ban gado ana ta karin ruwa. Da dare su daddy sukazo su uku suka dubani fuskan babana ba sauki kallo daya nayi mashi ban sake ba don na karanci halin babana dole akwai abindake damunsa a lokacin kwana daya nayi aka sallamoni da yamma muka dawo gida wanda anty Nafisa ce ta zauna dani asibitin lokacin. Kodana dawo gida ban wani kara sakewa ba kamar yadda na saba saidai abinda ke ban mamaki shine har na kwanta na taso asibiti mummy bata lekani ba hakama yayanta. Sai bayan kwana biyu da dawowana sai gata part din mum din wai sun shigo gaidani mum ke fadin ai mama taji sauki ko saidai dan abinda ba,a rasa ba kuma amma ta mike insha Allahu. Murmushin yake hjy mummy tayi kafin tace ku dai jaye maganan ku tun kan akai ga hasaran wani acikin su don wanan zance ba mai yuyu bane kuma kun sani. Meye naw a ciki hjy malka iyakata nima ido Alh ne inya tashi abinsa baijin shawara yadda ya hau din nan waya isa yace masa kar yayi ai gamu gani ta fada ta juya shine gaisuwan da aka tursasata tazo tayi min shi tayi ta fita lokacin. Haukan baza sai kace dan naki yafi dauran yayane agidan inba dole ba wake son hada zuri,a dake sai dole wallahi mum ta fada a cikin takaici duk ban fahinci me zancen yake nufi ba. Nidai naga sun canza min dama kuma kusan haka muke dasu wata rana tayi muna dadi ana shiri wataran kuma kowa ya debi iska ya hau a tsakanin mu dasu sunce sun iya nace muje haka zaman namu dasu yake. Yadda iyayyen mu ke kishi haka nima muke zubawa a tsakanina dasu duk hanyan da zasu nuna min jiji da kai ko wani gani gani nasan shi tun a kauye sun gaza don nima na sanshi. Ina kwance daki da yanzu na saba