← Book details Duba Min Baya Fakon Biri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 61

Sashe 36

Duba Min Baya Fakon Biri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

zeey take gudun danta tun jiya mum dake daki ta fito acikin mamaki tana kallonsu. Tace ina kuka fito haka tace gashi na kawowa uwarshi shine don tun jiya tayi muna yaji bansan abinda mukai mata ba shine mukazo biko. Murmushi mum tayi tana karban jaririn a hannun uwarshi tace kinsan hjy malka idan ta tashi abinta bata ganin gaba balle baya nan tazo jiya da safe ta kare muna zari. Mummy din nikan nayi tunanen akwai matsala tace wallahi muna zaune da dan uwanki sai gata walahi Allah dagashi har mama din amma sai gata tashigo da cin mutumci wai yayanki na nufin kada ta saka mama komai ko yana nufin wani abune dayake kokarin kulla mata sheri ta kwashe zancen yadda akayi ta fada mata sai hakkuri take ba mum din. Karshe dai mum tace ta kyaleta kada taje tayi mata zancen kuma rayuka sukai ga baci ga mutane a gidan ta kare da fadin tana nan zuwa idan ta gama abinda takeyi tana muna breakfasts ne. Tamike tana fadin kizo kiga dinkunan da aka kawo min mu zabi wanda zan fara sakawa a ciki nace to cikin tashin dadin rai a nan tabar baby din zata fita saiga mairo ta shigo tana fadin mummy tace kizo ga mutane sun shigo ta juya kai tsaye bata ko tsaya gaida mum ba. Ko yar uwan tayi mata fada sai gata ta dawo tana fadin sorry mum banko gaida ke ba mummy ta azalzaleni nakira mata anty har na rudi karbi dan ki kai tunda ga yan barka sun shigo . Fuska ta bata kafin tace barshi kawai mum ni banga kowa a gidan ba zancen mummy ne kawai don Allah ta juya ta fice ta bar dan a hannun mum din. Karshe dau zuwa din akayi aka karbi taron nasan ko ita ta aiko a karbeshi saboda rashin yarda da bata dashi a zuciyanta gudun ai masa wani abin wai. Saida nagama da kitchen har girkin rana nayi wanka na shiga part din nasu don mu gaisa daita a falon ta take sun baza kaya ni banko kallah ba amma kiri kiri naji tana fadin rufe min kayan nan har anjima nagani. Ina gaida ita na juya zuwa dakin anty Nafisa din tana zaune ita da wanan tsohuwar da Dada kunune irin na gargajiya a hannunta tana shana shigo. Wallahi zeey baki da kirki sai yanzu kikaga daman zuwa har tela yazo ya wuce na dai bashi samfur yayi maki dogon buje da riga ko dogon riga kikeso nace a,a ina juyawa don gaida tsofin dake dakin. Nan Dada take fadin bansan meya samu yar nan ba yanzu da bata son shiga mutane kamar da yanzu ma abin ya kara rikice mata in anyi magana tace karatu kamar al,hudahuda uwarta kuma ta kama mata. Dada aiko ba zakice min haka ba na fada na juya zuwa wajen yaron yana barci amma haka na daukoshi ina dubawa ina kare masa kallon kwata hilla har uwar ta lura dani tace. Wanan kallo haka zeey nace yaron nan naga kamar ya rame mun a ido kafin uwar tayi magana Dada tace keko dai yasha iskan duniya ya bazai rame ba. A,a Dada yaron nan kamar baya da lafiya fa nake gani duba yadda ma yake numfashi a wahale ina dan juya hannun yaron a hankali daya tsohuwar tace mikoshi mu gani na mika mata ta karbeshi Dada sai fadi take wanan yar kamar tashin tsofi take fa. Gaskiyan yar nan Dada yaron nan baida lafiya ikon Allah amma duk bamu lura ba wanan abinda ba a so gashi duk ya shedo masa a ciki zubur anty Nafisa ta mike tsaye. Cikin rikicewa tana fadin ina mummy mu kaishi asibiti ke kwantar da hankalim ki abi sannu ina fita tayi daga dakin ko minti biyu ba,akai ba sai gasu tafe gaba dayansu a rikice dakin. Anty Nafisa sai fadi take badon shigowan sister dakin nan ba ba wanda ya kula da hakan yanzu fa kuka dawo dashi tun dazun yana falo wurin ku ke iya ya akai haka kuma nan Dada ta tare da fadin kamar ya kuma ya akai haka ? To hjy za ace gaku zaune amma baku gane hakan ba sai shugowan maamah saboda Allah bamu da amfani ke nan ko itako iya sai fadi take ita dai Allah ya turo ta gane muna dama. Caraf anty Nafisa ta karbe yaron daga hannun tsohuwar tana fadin sister dauko min jakata mu tafi wanan ba zai fissheni ba da sauri na juya saman gado inda jakkarta yake ina kokarin daukowa naji uwar tace mata. Ke banson rashin kunya kinji dukkan mu nan bamu damu dashi ba ke nan kike nufi ko me ko sai kin nuna muna ke kika haifesa tau gamu ganin ikon Allah dai Dada ta fada tana tashi. Sai rana naji mummy ta yiwa anty Nafisa fada irin gyara kayanka a gabana duk zamana dasu gidan ban kare mamakin haka ba saida naji tace ke mairo kira min hjy kubura. Nace ashe ko mugu yana da rana ke nan yau ga ranan mum ke nan ashe itama mum a rude tazo hankali tashe part din tana fadin asha meke faruwane kuma ? A nan dai aka yanke shawaran tafiyansu da mum din asibitin bayan an kira daddy an sanar dashi yace su hadu asibitin gasu nan zuwa suma hankalin gida ya tashi dan Adam mai tsada da kima kan dan jariri hankalin kowa ya daga a gidan mutum ke nan. Bayan tafiyansu dakin nakoma na gyara masu shi tsab don a karshe hjy mummy itama ta bisu don bata yarda ba hakan ya ban dama tsayawa na gyaro mata dakin na rufo na koma part din muna jiran abinda za ace game da yaron. Gashi duk aka tashi magana za,ace ai zeey ce tagane hakan ga tsofi basu gane ba sai kuma hakan yake sosa min rai idan na tuna don halimatu a gabana ta fara fadin kwarkwasa ke nan ai tasan komai ita dama. Watau har abinda ba ai tsamani ba duk na sani ke nan take nufi amma na kyaleta don ba lokacin musayan baki bane ana cikin tashin hankali haka din. Su mum suka dawo suna fadin an basu gado don an kwantar da yaron wai ya fito da shawara har tayi masa yawa a jiki ta hudu shi wanda suke kira da Jondis. Acewansu likitocin sunyi fada sosai na rashin kawo yaron da ba,ayiba da wuri akabarshi gida haka ciwo na batun masa illa. Banda wani aiki don haka mum tace in shirya in bisu naje don hankalina ya kwanta a can muka samu su maito dasu halima da Asiya don banko sanda fitansu bani. Ina shiga Anty ke fadin ehh sister badon ke dake da kula ba da yaron nan ya mutu muna zaune ana faman surutu a daki ba wanda ya kula da hakan gareshi. Mum tace haba bai mutuwa ai sai idan kwanansa sun kare wahala dai akewa gudu amma kowa ya mutu dama iya abinda ya debo ke nan a rayuwanshi. Mun jima a nan take min hira cewa dan iskan uban nasa dazun daddy ya buga mai waya yana sanar mashi gamu asibiti sai cewa yayi Allah ya sauwaka kawai. Mum ta kara kada baki garemu tace to me zaice Nafisa dole dama ai addu,an samun lafiya zai masa tace ki bari kawai hjy mum habib dan iskane na gaske dama ya fadi ya barmin cikin duk abinda na haifa inje inji dashi tunda nace ban yarda a zubar da cikin ba. Kinga dan nan dayaki anty idan Allah ya bamu raida lafiya wata rana shine mai tallaban rayuwansa saukin abin agaremu bakece baki kaunar yaron ba ai kuma yan family din mu kowa yana kaunarsa kauna mai tsanani. Yarone fa amma ki duba daga dakin nan har waje duk yan uwane suka taru akan dan nan insha Allahu sai yaji kunyar wanan abin dayayi wata rana. Kwatsam ya hafiz ya fado dakin kallo daya nayi masa na dukar da kai ina tuna irin yanayin da naganesa a ciki a dakinsa sai naji girmansa da kimarsa da nake gani yazube min ga ido. Gashi tsab zakice mutumin kirkine a fili ashe a boye mutumin banzane irin na bugawa a jarida din nan muryan anty nafisa ce yakatse min tunane a lokacin take fadin wai baki gaidashi ba sister. Firgigit nayi tare da fafin wa hafiz mana ta fada nace ai nagai dashi daya shigo na kara fadin ina wuni tsuki yaja yaci gaba da magana da yar uwarshi ya fita zance na. Mummy ce ta fado dakin da kawayenta kallon yadda muka hade kai da anty muna magana kus kus kus ga iya zaune a saman tabarma bata ko jin me muke fadi tashigo. Kallo mu ta sakeyi tana fadin to rakwato aisai ki fita ga bakina nan sunzo duba yaro kar kuma a kaimu haba mummmy please ki dainawa yarinyar nan haka a gaban mutane mana sai a dauka haka halintane ai yar ta fada ciko bacin rai. Ban san ya sukayi ba don na bi driver nakoma gida sai washegari na sake lekasu asibitin koshi da nace ba zanje ba don mummy saboda nagane dai ta tsaneni a zuciyar ta. Banje da niyar zama ba muna zaune saiga ya Addel da budurwansa sun shigo wanan gulma ya zaunar dani muna kallon ikon Allah yadda ake soyayya nami sai a barshi kawai akan soyayya don idonsu kan rufene a lokacin. Donko abinda ya Addel keyi ba zakice shine ba ko don iyamu yarane a wajen lokaci saiko yan tsofin dake zaune daga waje ga yarinyar da alama ba kunya gareta ba. Don ko garemu katsinawa wanan rashin ta idone mutum yazo gun dangin miji tun baishigo ba yana wanan kaudin haka ba nuna alkunya ga kowa sai nuna sani da iya tun a nan ta sure min a zuciyana. Shiko yana faman washe baki yana jin dadi nace kaiya anyi ba,ayi ba kenan mutum kamar ya Addil Allah ya hada da wanan kalar macen kuma ? Yar gayuce ta fada amma hade da rashin kunya ko gayun nasune yake jawo masu rashin kunya oho saidai mazan dake son su basu ganin hakan. Basu jima suka tafi ina gefe
Chapter 36 · 0% Book details