Sashe 5
Duba Min Baya Fakon Biri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kawo min na tausa don gidan ku kaje kaima kaci a can din. Ni kan ka isheni ka hana mu gaisa da yan uwanka muyi yaushe rabo dasu ta koma ta zauna dayan ya kalleta yace Dada ina farau farau din kinsa mun saka rai kin kuma zauna. To na iya ja,irin nan ya fara fadan kwano da tsatsa zan halakaku da shi haka ta kallo inda nake tana fadin kinga Abule tashi hado masu ruwa a tulun nan mai sanyi da wanan sauran furan sai na dan kallosu a sace na kuma mike zuwa yin abinda ta sakani yi din.. Nakawo nake jin tana fadin yanzu kan tunda kun karasa karatu ai sai zancen aure ga yan mata a cikin dangi ko wanen ku a bashi anma gama magana akai yanzu gabatarwa ya rage a gareku. A take fuskokinsu ya sauya kafin shi fitsararen nasu ya kalli tsohuwar yace ku baku da wani zance sai na aure karatun dama ko kammalashi ba ayi ba zaki daukowa mutane zancen aure daga mun shigo duban ki ki kawowa mutane zancen wani aure a yanzu kuma. Yana fadin haka ya mike tsaye ya kallo yan uwa yana fadin ku sameni waje don Allah tama bata min da wanan zancen Dada ta waro ido waje ta dafe kirjinta tana fadin shu,umi ba dai ka manta alkawarin malam akan ku bane tun yanzu. Dona ambaci auren zaka dauki zafi dani da ba,a aure za,a haifekane dan kawai koba aure ya haifeka ba kai . Ya kallo tsuhuwar yace ko zaki maidani ciki tunda kinyi bakin ciki a yanzu nazo duniya ta hanyar aure to ba zanyi ba ku rike duk yar da zaku ban na yafe akaiwa wani. Nifa bari kiji Dada ba wanda zaimun wanan auren hadin naku na gado tunda ba Allah da Annabi sukace kuyiwa yayan ku hakan ba balle kizo min da wanan zancen daga saukana gari ko ruwa bansha ba na huta. Yana fadin haka ya fice ta fara salati tana tafa hannaye kafin ta fara kuka irin na tsofi tana fadin kaji min dan kawai har yanzu ashe iskancin nasa yana nan yadda ya barmu girma baisa ya bar wanan halin nasa ba. Sauran hudun suka kwashe da dariya suna fadin barshi Dada yayi maki hakan ne don kiji tsoro amma ai ba hakan halinsa yake ba inma haka yake ai zai hadu da uban nan kune ida yace shi dan banane. Ina makure ina kallonsu kafin su mike da kamshinsu nabisu da kallo har suka fice daga gidan bayan sun ajewa Dada din alheri sukai gaba sai gashi tsohuwar ta koma fadin yan albarka sun gado mahaifansu wajen alheri. Yaki zoki kirga min kudin nan na boye kafin yaran banzan nan su dawo su wawashe min tare muka kirga kudin dubu goma sha biyar tana faman saka masu albarka. Ta cire dubu daya ta miko min tana fadin ki karbi wanan kyasai foda sha wanan kuma daure min shi dakyau na tura a lalita kafin su dawo su gane ina da kudi a dakin nan. Kaina girgiza kafin nace a,a Dada ki barshi nayafe rankwashi ta kai min a kai tana fadin ko uwarkice ta hanaki karban da sauri nace a,a Dada kawai ki barshi ta dangwara min kudin a jiki ta mike tana cire zip din lalitan bujenta irin na tsofi na mika mata kudin dana daure din ta tura a cikin aljihun nata. Mikewa nayi ina fadin Dada barin koma gida kada baba ya nemini ban fada mashi zan shigo nan ba na fito na barta tana fada dani akan me zance za a nemeni bayan ansan banda wajen zuwa kaf unguwa sai wajenta. A kofan gida na samu baba zaune da kanwata sadiya da dan ledan awara daya saya mata nake gaidashi yace dani daga wajen Dada ko nace eh baba naga gidan da bakine naje can. Murmushi baba ya sauke a fuskanshi yana fadin banda abinki zainab ai duk yayyunkine wa yan nan kusan abu daya kuke dasu rashin sanine kawai don baki saba dasu ba tun farko. Murmushi na sauke a fuskana ba tare da magana ba na shige gida inna tana zaune saman kujera yar tsuguno ta mata na shigo da sallamana ina gaida ita. Gunsu na nufa ina lakatan fuskan yaro nace maizuka inna wai wanan yaron naki baya gajiya da shan nono ko yaushe nono a bakinsa . Ta dago cikin haraea tana fadin ke bakya gajiya da cin abinci wayayi maki wani zance balleshi wanan meya samu har ya zuka bayan kun kwashe komai tundai ke na saka yar dariya ina cire hijjab din dake wuyana direct gun wanke wanke na nufa. Ina wanke wanken muna hira da inna jefi jefi akan islamiyan mu nake bata labari har yakai nagama na kife na dauki tsintsiya na share gidan tas kafin na dauki bucket na dibi ruwa a randa na nufi bandaki don in watsa ruwa ko ya ruwa yake da sanyi kuwa don mun saba tun a kauye. Bayan mun shirya har kannena muka fito don zuwa islamiya a daidai wanan kofan dake rufe ko yaushe na hango dandazon su ban daga ba ban kuma kallo inda suke ba haka muka shigesu zuwa islamiya. Wa yancan yaran badon a kauye suka taso ba da yanzun sun fi kowa a family din nan shanawa don yaran gasu gwanin ban sha,awa dasu wallahi. Kai uwarsu ce suka kwaso wa yan nan yaran akwai tsabta daga gefensu wasu ke fadin wai yarancan suna da girman kai basa gaida kowa fa yara kanana dasu amma sai girman kai. Haba dai wa yan nan yaran me suka sani wani girman kai dayan da duk tsayinsu wajen kowa na fadan albarkacin bakinsa sai wanan ya furta daga hakan kuma bai kara tsunkawa ba ya juya shigewa yayi ya barsu a wajen. Tunda na samu nabar wajen naci gaba da sauri ban tsaya ba na shige islamiya a kusan kullun mune farkon shiga islamiya har ma yanzun da abokan tafiyana sukai tafiya. Har muka tashi islamiya gabana sai faduwa yake ba komai yaja min hakan ba sai ganin wa yan nan matasan da baba ya kira da yan uwana duk da naji su din yan uwanane amma hakan bai hanani tsoron suba. Kodon shigar tufafinsu da yanayinsu da ban saba ganin shigar haka ba ga mutane don ko a nan katsina akasari irin shigan mutanen hausaw suke shiga wando da rigan jamfa amma wa yan nan gasu fara wasu chaculate color amma haka suke a tsuki dasu ba maiyiwa wani fada a cikinsu gashi ba zakace ga babba ga karaminsu ba komai a tare sukeyinsa. A gaban mu motarsu tazo ta wuce mu sai muka samu mutum biyun su kofan gidan Dada sun faka motar dayan yakai bakin masalaci daga nisa kaina yana duke kasa yake fadin don Allah yan matan dada karbo min ruwa wajenta nayi alwala. Sam ban dauka dani yake zance ba sai kokarin shigesu nakeyi kaina na dukr a kasa sai dayan dake gefen mota a tsayene yace ke yarinya dake ake magana koke kurmace bakya jine ,? Jin hakan yasa na dago kaina ina fadin ayya banzata dani yake ba ai don Allah kuyi hakkuri baiko tsaya bin ta kaina ba hakan yasa na nufi wajen mai miko min butan na karba daga hannunsa tare da dan rusunawa na girmama a gareshi kansacewarshi na gaba dani. Ya karba yana min turancin daba fahinta kwakwalwata zaiyi ba Dada tana zaune tana jiran ayi kiran sallah na shigo da sallamata ta amsa min tace kishiyata badai yanzun kuka dawo daga karatun Allah ba ? Yanzune Dada sauri nake in karasama gida wanan bakin birni din sukace na debo masu ruwan sallah a nan tace shu,umai ni yanzu na kare zancensu a raina har ina zaton ko sun wucene ma don ban kara jin duriyansu ba tun dazun da suka fice. Ni dai na debi ruwan nakai masu ruwan ya karba tare da furta kalman thanks ya juya nima na kama hanyan gida ina sauri kada a kira magariba ina waje kamar yadda iyayyena suka horemu dayi kullum. Ina shiga gida daidai ladanin masalaci yana dauka loudspeaker zai kira sallah wanda wanan karan ke fara fadakar da nusulman unguwa lokacin sallah yayi. Innace zaune da danta dake goye a bayanta tana jiran kiran sallah sallama na kara yi ina gaida inna din saidai bata amsa min ba bayan fadan data tareni dashi da fadin. Meyasa bakya jini ina kika tsaya har aka kira magariba baki shigo gida ba sai kannenki da kika turo min suka shigo su kadai kallonta nayi a dan maraice nace ban tsaya ba inna tare muke dasu wa yan nan bakin da baba yace yayyun mune sukace in debo masu ruwan alwala a gidan Dada. Ki dai kula ta fada taja buta ta fara alwala ganin hakan tunda na saba jin wanan kalman ba saudaya ba ba sau biyu ba a bakin inna din wanda bazance ga ma,anarsa ba a kaina yasa naje dakin mu na debe hijabin kaina na fito na dauki buta na zaga ban daki. Bayan na idar da sallah na shafa addua ban zauna ba don nasan abinda zanyi basai an tuna min ba madafi nashiga na dauko kwanon silver da muke cin abinci na zubawa su sadiya. Kafin na koma dakin inna na dauko shimfidan baba na shimfida har filo da yar redion shi da yake sauraren jakkar magori dashi da sauran shirin radio kaduna idan ya dawo daga sallah don bai kara fita idan ba wani kwakwaran dalili zai fitar dashi ba sai kuma Allah ya kai muna rai washegari yake fita kuma. Bayan naga ana tayar da sallah na shiga nayi a nan na dan jima ban fito daga dakin ba har saida baba ya shigo naji yana tambayana na amsa ina fadin gani baba na fito ina gaidashi. Yake tambaya kinci abinci kuwa nace yanzu zanci baba ina biya karatun mu na yaune kada ya shige min mallam yayi min duka gobe mai sunan iya banda abinki ai sai ki fara cin abincin kafin ki zauna karatu. Na juya zan dauko abincin naji inna na fadin ai kasam halin ta da naku naku cin abinci sai ta saka mutane yin magana