← Book details Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 82

Sashe 78

Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

     Tarba ta girmamawa Alhaji Abaan ya samu a wajen Ministar. Domin kuwa akwai sanayya batun yanzu ba, sannan akwai huɗɗar kasuwanci. Tun kuma a daren jiya ya nema ganinsa ta hanyar tura masa saƙo ta waya. Hakan yasa batare da wani kace nace ba suka haɗu a gida kai tsaye kamar yanda Ministar ɗin ya bashi dama yau da safe ta hanyar kiransa. Dan Alhaji Abaan ko shugaban ƙasa ya buƙaci gani duk da a ƙurarren lokaci ne hakan bazai gagaresa ba. Dan ya wuce duk yanda mai hasashe zai iya hangowa yanzu a ƙasar nan. To ada can baya ma da suke matasa akayi dasu balle yanzu da gwamnatin ma sune suka kafata da dukiyarsu da iliminsu.
    Bayan gaisuwa da ɗan barkwanci tsakanin dattijan guda biyu Alhaji Abaan ya nuna Mimi da Yazeed dake zaune ƙasa kawunansu a ƙasa tamkar masu neman gafara. Yazeed ya nuna da faɗin, “Nasan kasan wannan. Wannan kuma first born ɗina ce Fatima”.
     Fuska cike da murmushi Ministar dake kallon Mimi ya ce, “Masha ALLAH dota yaki nan. Wato girman dai ɗan mutum babu wahala. Yanzu Alhaji Abaan yarinyar da muka sha shagalin sunan ta ce ta girma haka oh ALLAH”.
   Murmushi kawai Daddy yay batare da yace komai ba. Yayinda Mimi ta taso a ɗarare har gaban ministar ta sake zaman gurfane. Daka ganta kasan hankalinta baya tare da ita. Gaishesa ta sake yi cike da girmamawa. Ya amsa mata da kulawa yana jera mata tambayoyi. Har suka kammala Daddy baice komai ba. Sai da sukai shiru sannan Daddy yayma Yazeed nuni da shima ya matso. Tasowa shima Yazeed ɗin yayi a ɗarare ya gurfana kusa da Mimi kansa a ƙasa kamar yanda take. Daddy ya maida dubansa ga ministar da yayma ɗan nasa kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Batare da ɓata lokaci ba Daddy ya shiga yima Ministar bayanin abinda ya faru a jiya game da fitar Mimi gida. Har bayanin da Ammie tai masa zuwa abinda ya faru yau. Sannan ya miƙama ministar wayar Mimi dake hannunsa. Shima duk sakwanin da suka shiga tsakaninsu ne ya dudduba. Bayan ya kammala ya ɗago ransa a ɓace yana kallon Yazeed. Magana yaso yi amma Daddy ya dakatar da shi.
        “Kasan miyyasa na kawosu gabanka?”.
     Kai ministar ya girgiza masa rai a jagule. Daddy yay ɗan murmushi. Sannan ya cigaba da faɗin, “Saboda mu fiskancesu tare. Da farko naso hukunta yaron dake tare da itan ne koda ɗan waye. Sai dai jin yaronka ne yasa naji bazan taɓa iya hakan ba. Sam ba soyayyar tasu ko alaƙarsu ta ɓatamin rai ba. Hanyar da suka ɗora kansu wajen gina soyayyar ne ya zafeni ya kuma tayar min da hankali. Domin hanyace mara ɓillewa. Wlhy wlhy ko ɗan maigadin gidana Fatima ta kawo gabana tace min Daddy ina son wannan da aure shima yana sona bazanji komai ba sai farin ciki, zan kuma goya musu baya na bama alaƙarsu ƙarfi ta yanda basuyi zato ba. Amma soyayya a bayan fage da ɗaukar salon cutar da iyaye koda ɗan wanene bazan ɗauka ba. Dibesu, dukansu basu haura shekaru ashirin ba a duniya amma sun san su yaudari iyaye ta hanyar barin makarantun da muka turasu su tafi lambun soyayya. A da fa iya makaranta ake bari zuwa garden, amma yanzu ta fara kaiwa matsayin barin gida babu izini zuwa gidan cin abinci. Daga haka mi kuma muke tunani zai biyo baya....” ya dafe kansa cikin takaici. Batare da ya jira cewar ministar ba ya cigaba da faɗin, “Wannan ta riga ta faru, ba kuma na fatan ta cigaba da faruwa. Dan haka nazo da su gabanka. Idan ka shirya yima Yazeed aure ka turo min magabatansa na bashi auren Fatima. Ba kuma nason komai ya wuce nan da wata biyu. Taje tai karatun a gidansa idan tana da ra'ayin hakan, idan kuma bata buƙata duk ya rage nata. Ni dai Alhmdllh nasan na sauke nauyinta da ke kaina matsayin mahaifi. Hakama mahaifiyarta na iya ƙoƙarin ta a kanta. Sai dai na sharɗantama Yazeed kar ya sake tareta a waje da sunan soyayya, kada ya sake zuwa ɗaukarta makaranta da sunan soyayya. Kada ya sake kiranta ta fita a gida saboda sunan soyayya. Na bashi dama yazo gida a duk ranaku uku na cikin mako, suyi hira a falona daga nan har zuwa randa zan bashi ita a matsayin mata. Yazeed wannan alfarmar kawai nake buƙata a gareka dan ALLAH dan ALLAH ka taimakeni”. Ya ƙare maganar yana kallon Yazeed dake hawaye kansa a ƙasa. Hakama Mimi kuka take kamar ranta zai fita dan maganganun Daddy sun matuƙar gigita mata zuciya da sata a ɗimuwa.
      Shi kansa Ministarn kallon ɗan nasa yake cike da matukar mamaki da al'ajabi. Dan da wani ne yazo ya sanar masa Yazeed ɗin zai aikata haka wlhy bazai yarda ba. Saboda kaf a cikin yaransa babu wanda ya kamo ƙafar Yazeed hankali, nutsuwa da biyayya. Yaro ne nagartacce da ƙyawawan halaye. Sannan gashi shiru-shiru kamar idan ka saka masa yatsa bazai iya taunawa ba. Cikin tsananin ɓacin rai ya rufe Yazeed da faɗa, ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba. Sai da yay masa biji-biji Yazeed ɗin na hawaye sosai sannan Daddy ya riƙo hannunsa yana ɗan murmushi da faɗin, “Ya isa haka tom”.
      Kansa ya girgiza tare da maida dubansa ga Daddy. “Nagode sosai da wannan halaccin da kaimin Alhaji Abaan. Wlhy wlhy kaji na rantse daga ni har mahaifiyarsa bamu san hakan na faruwa ba. Dan kullum ya shirya ya fita a saninmu makaranta ya nufa kawai. Yanayin rayuwa da taɓarɓarewar abubuwa yasa mahaifiyarsu bata yarda su ƙetare ƙasar nan domin yin karatu ba, musamman ma su mazan, matan kuma idan mazajensu sun amince su tafi dasu dan da sun kammala sakandare muke aurar dasu. To ashe shi shaiɗani yana can yana hurema yarinya ƙarama dake aji biyar na makaranta kunne saboda zalunci. Kai idan akaima ƙanwarka haka zakaji daɗi? Duka nawa kake ma Yazeed. Just twenty years fa, amma kake.....”
     Sake riƙo masa hannu Daddy yay yana murmushi. “Oh calm down ya isa haka. Ai kuskuren ba nashi bane shi kaɗai harda ita Fatiman. Amma in sha ALLAHU ni zan magance matsalar in dai kun shirya masa aure. Dan ita dai in sha ALLAHU bazata sake min wata biyu a gida ba koba Yazeed ba zan aurar da ita ne na riga na yanke hukunci”.
      Sake rikicewa Mimi tai da kuka.........✍️

*_WAI KINA SHIRIN WUCEWA NE BAKI KARANTA BA😨._*

*_TO MAZA DAWO BAYA KI DUBA. IN BA HAKA BA ZA'AYI BABU KE NE_*

*_INA KUKE MASOYAN ZAFAFA BIYAR DAMA WANDA BAZU TAƁA SIYA BA SAI DAI SU KARANTA A HANYA_*.

*_MAZA KU MARMATSO KU MALLAKI NAKU DAN GAB JIRGIN YAKE DA BARIN ƘASA. MA'ANA GAB ZAFAFAN SUKE DA FARA SAKAR MUKU ZAFAFAN LITTATAFAN SU NA SABUWAR SHEKARAR 2024_*

*_KAR KUYI MAMAKI IDAN NACE MUKU TAFIYAR FA TA BANBANTA DA BAYA. SABODA SALON NA DABANNE, NA KUMA MUSAMMAN NE_*.

*_TSUTSAR NAMA....!!_*
_(Bilyn Abdull)_

*_AMEENATU_*
_(Mamu gee)_

*_KWANKWASON JIMINA...._*
_(Mss xoxo)_

*_GUDUN ƘADDARA_*
_(Safiyya Huguma)_

_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._

_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_Shafi na arba'in da biyu_

*_WAI KINA SHIRIN WUCEWA NE BAKI KARANTA BA😨._*

*_TO MAZA DAWO BAYA KI DUBA. IN BA HAKA BA ZA'AYI BABU KE NE_*

*_INA KUKE MASOYAN ZAFAFA BIYAR DAMA WANDA BAZU TAƁA SIYA BA SAI DAI SU KARANTA A HANYA_*.

*_MAZA KU MARMATSO KU MALLAKI NAKU DAN GAB JIRGIN YAKE DA BARIN ƘASA. MA'ANA GAB ZAFAFAN SUKE DA FARA SAKAR MUKU ZAFAFAN LITTATAFAN SU NA SABUWAR SHEKARAR 2024_*

*_KAR KUYI MAMAKI IDAN NACE MUKU TAFIYAR FA TA BANBANTA DA BAYA. SABODA SALON NA DABANNE, NA KUMA MUSAMMAN NE_*.

*_TSUTSAR NAMA....!!_*
_(Bilyn Abdull)_

*_AMEENATU_*
_(Mamu gee)_

*_KWANKWASON JIMINA...._*
_(Mss xoxo)_

*_GUDUN ƘADDARA_*
_(Safiyya Huguma)_

_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._

_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥

_______________

........Cikin jinjina kai Ministar ya ce, “Wlhy ka birgeni, kuma hukuncinka yamun dai-dai. Aure kuwa tare da shi daya hure mata kunne zamu musu in sha ALLAHU. Suje su ƙarata dan ni dai babu ɗan da zai bani ciwon kai in sha ALLAHU Alhaji Abaan. Na kuma gode da wannan karamcin naka. ALLAH yabar zuminci. In sha ALLAHU zuwa weekend zamu shigo mu ganka. Sannan ina sake bada haƙuri da neman afuwa dan ALLAH”.
      Murmushi Daddy yay da ɗan harararsa. Daga haka sukai dariya irin tasu ta manya. Cikin kuka Yazeed ya rarrafa kusa da Daddy. Haƙuri ya rinƙa bashi da cewar ya yarda yayi kuskure. Amma dan ALLAH Daddy da Abban nasa su yafe masa. Kuma shi wlhy ba laifin Mimi bane laifinsa ne. Murmushi kawai Daddy yay da shafa kansa da faɗin, “ALLAH yay muku albarka. Ya shirya mana ku baki ɗaya.” daga haka ya miƙe abinsa.
Chapter 78 · 0% Book details