Sashe 27
Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da bibbiyu Dafeeq ke haɗa steps ɗin benan. Jikinsa na rawa kamar wani mayuncin zaki. Yanda yay wani irin kumburar ɓacin rai bazaka taɓa ɗauka yaron nan ɗan shekara ashirin da huɗu bane ba. Kai tsaye ɗakin kainaat ya nufa, sai dai yana ɗora hannunsa a handle ɗin ƙofar ya jita a rufe. Cikin ɓacin rai da ihu ya ce, “Hajiya buɗe ƙofar nan kona ɓallata!!”.
Wani shegen murmushi Kainaat ta saki tana taɓe baki. A ranta tace haba yaro bakai kana jin kai ɗan iska bane kana a ganiyar balaga. Indai takamarka kai shege ne nan ma gidan ka taras, waya gaya maka ana shiga gonar Kainaat a fita lafiya babu tabon sarin maciji koda a yatsan ƙafa ne. Ai wasan yanzu ma aka fara, da kanka zaka min abinda nake so kafin ma cikar sati ɗaya. Amma hakan bazai hanani hukunta shegiyar matarka ba tunda ita batasan taci arziƙin a rabu lafiya ba. Taja tsaki tare da fisgar wayarta ta shiga danne-danne tamkar batajin hargowar da yake da jijjiga ƙofa. Wayar na gab da tsinkewa Nadwa ta ɗauka. Cikin yanayin barci ta ce, “Hello”.
“K malama watsakke a wannan barcin nice”.
Da mamaki Nadwa dake tashi zaune tana murzar ido tace “Amarya a wannan daren, ina kika bar mijin naki ke kuwa dan ALLAH. Wai badai da gaske kike bazaki bashi kanki ba?”.
“Humm share ba wannan bane yasa na kiraki Nadwa, so nake da safe ki sanarma Mommy ina son a aika matar nan taje min wajan malamin nan da yay min aiki akan Abaan ina amarya. Ina son a gobe Dafeeq ya saki matarsa”.
“What! Haba! Haba Kainaat mi kuma ya kaiki wannan tunanin? Dan ALLAH kada ki raba ma'auratan nan Please and please. Keda ba zama kikaje yi ba miya kawo miki wannan tunanin a daren nan? Ni dai babu ruwana dan ALLAH kada kiyi haka akan yarinyar nan da abinma tausayi ce. Ki barta da zalincin da yake mata ma na zubar mata da ciki”.
“Haba kema kin san ganganne na ƙyale cuta ban rama ba. Ai rama cuta ga macuci ibada ce. Har ke kike tunanin wai babu ruwanta. Wlhy duk da ban auri mijinta dan na rayu da shi ba ita bata isa ta shiga gonata na ƙyaleta ba. Da ga safiyar yau zuwa daren nan tamun abinda sai ta san ta shiga gonata wlhy”.
“Ya ALLAH calm down mana Kainaat. Mita miki?”.
Kamar bazata faɗa mata ba sai kuma ta kwashe komai ta sanar mata. Tare da ɗorawa da wannan hukuncin nasu ne su biyu, duk da kuwa shima na tabbata dama wannan shine burinsa a kanta ƙarshe. Dan maza irinsu da sukai auren wuri kuma irin kalar auren nan daga ƙarshe mawuyaci ne basu sake su ba kosu ƙaro musu kishiya. To ni zan rabasu ne a gaɓar da suke buƙatar junansu dan ubansu. Duk da ban auresa dan na zauna dashi ba shi har ya isa ya ɗauki kwanana ya kai mata, tsabar son zubar min da mutunci a wajen ƴar cikina kwana ɗaya da auro ni. Ai wannan cin mutunci yakai cin mutunci”.
“To amma baki ganin kema akwai laifinki? Maybe a matse yake bawon ALLAH kin hanashi kanki kin bashi kuɗi tayaya kike ganin tunda yasan yanada wata matar bazaije gareta ba. Ni dai dan ALLAH ki barsu, abinda kika faɗa mata ma kawai ya isa punishment a gareta, shiko nanda sati ɗaya zaki masa nashi punishment ɗin tunda ya saki jiki aure yay kamar kowa zaici banza, bai san nan da kwanaki komai daya samu ba ma zai rasa shi. Hakan kawai ya ishesa ai”.
“Ina hakan yamun kaɗan, idan bazaki min yanda nake so ba barshi, bara na kira Mommyn da kaina dama dan naga darene bana son tadata a barci, kuma so nake tunda safe aje a amso min”.
“A'a miyay zafi, saƙonki kam zan isar in dai nice. Ni dai shawara na baki dan ina tsoratar miki abinda zai iya zuwa ya dawo. Tunda ba gama sanin halin yarinyar nan kikai ba. Koda kike ganinta ƙarama maybe itama ta iya nata kalar hatsabibancin. Kigafa yanda ta maida miki magana har sau biyu”.
“Mtsoww! Riƙe shawararki malama”.
Kainaat ta faɗa tana yanke wayar. Jefar da ita tai gefe tayi kwanciyarta batare fatabi takan Dafeeq dake cigaba da kiran sunanta yana ƙwanƙwasa ƙofar ba. Sai ma taja headphones dake cikin bedside drawer ɗin ta ta saka abinta, daga haka tabar jinsa gaba ɗaya...
Matuƙar tashin hankali Dafeeq ya shiga. Ta ina matar nan ta samo wannan sirrin nasa da yasan da ga shi sai ALLAH sai likitan nan suka sani. Sannan zuwa gida da yake yi kuwa shi kaɗai ya sani sai UBANGIJI. Dan tun bayan aurensu da wata biyar ya yanke shawarar zuwa ga iyayensa kasancewar labari ya sameshi mamansa ta samu karaya a ƙafa. Koda yaje bai wani sha wahalar shawo kansu ba dan suna son sa kamar mutuwa sakamakon shi kaɗai suka haifa a duniya. Bai yarda ya faɗa musu a ina yake ba, ya kuma sanar musu ya saki Khadijah tun kafin yazo garesu saboda yaga basa so, yanzu neman kuɗi yake yi dan ya koma karatu. Sun ji daɗi sosai suka dinga saka masa albarka. Kwanansa biyu batare da ya yarda kowa ya gansa ba ya dawo. Yayinda babansa ya shirya har gidan su Khadijah yaje yayima mahaifinta tas yace kuma su nema ƴarsu acan gidajen karuwar dan ɗansu ya sanar musu ya saketa. Hankalin iyayen Khadijah ya sake tashi, jikin babanta ya sake rikicewa sosai harta kaisa da samun paralysis. Yanzu haka yana kwance gefen jikinsa baya aiki. Karatun ƙannenta ya tsaya, sai da taimakon wani bawan ALLAH da yaga ƙanwarta mai bimata yana so ya maida yaran makaranta, ya kai Baba asibiti. Yanzu haka yana amsar magani jikinsa da ɗan sauƙi, ƙannenta biyu sun kammala secondary sun cigaba da karatu, an kuma saka musu ranar aure dan dama burin mahaifinsu shi dai su fara karatun sannan ya aurar dasu sa ƙarasa a gidan miji, amma Khadijah ta nuna masa bai isa ba. Ƴan anguwar su Khadijah kam da mutane da yawa sun yarda Khadijah tabi duniya saboda tsoron kada ta dawo gida Dafeeq ya saketa a mata dariya ko iyayenta suƙi karɓarta.
Tun daga lokacin duk wata sai Dafeeq yaje gida, dan hatta auren nan na Kainaat iyayensa sun san zaiyi, hasalima a kuɗin data dinga bashi har gidansu yaje ya gyara tare da ƙarama babansa jari........✍️
_🥱 Dafeeq anya zakaga ANNABI ALLAH kuwa🤦🥲🚶_
_Khadijah ke kuma ƙya dawo hankalinki ai yanzu. Koda yake baki ji sauran labari ba ma😩_
_Ke kuwa Kainaat bakiyi wawtaba kuwa?, dan Dafeeq fa Hummm😆_
_JJ banda abin cewa a kanka kai kam yau🥲, na barka da masu karatu da su Alimah suci min ubanka bunsurun banza🧑🦯
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na bakwai_
INA ƳAN KASUWA MASU SON ƘAWATA KASUWANCINSU TA HANYAN GRAPHIC DESIGN, DA MASU SHIRIN BIKI, KO SUNA, DA MASU SHIRIN WALIMAR SAUƘA, DA MASU SHIRIN YIN BIRTHDAY, KAI HARMA DA MASU ANNIVERSARY 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
MAZA KU GARZAYO "UMMUH FARUQ GRAPHIC DESIGN "TA TANADAR MUKU DA HAƊAƊƊUN DESIGN MASU ƘAYATAR DA MAI KALLONSU.🥰🥰🥰
KAMA DAGA
*FLYER
*3D MOCKUP LOGO
*2D MOCKUP LOGO
*NORMAL LOGO
*IMAGE LOGO
*BANA
*STICKERS
*ADVERT VIDEO
*PROFESSIONAL INVITATION
*INVITATIONS CARD
*BIRTHDAY VIDEOS
*POSTER
*CERTIFICATE.AND MORE......
CONTACT ME ON
👇
09035390383
____________
.......“Please Kainat yaya kika san duk wannan wai?”.
“Humm Nadwa kenan. Na faɗa miki Kainaat ba shashasha bace ba ai, kin san dai bazan jashi jikina ban san wanene shi ba. Inama da fiye da wannan game da shi, sai dai lokaci ne zai sa ki san sauran gaba ɗaya ba yanzu ba”.
Idanu kawai Nadwa ta zuba mata cike da mamaki da tsoro. Maganar gaskiya bata son ƙawar tata tace zata shiga tsakanin waɗan nan ma'auratan dake tsaka da cin ƙuruciyar soyayyarsu. Amma ta santa tasan halinta, in har tace tana son abu sai ta cimma burinta a kansa, dan ita shaidace ko akan Don Abaan da yanda ya fara sonta har sukai aure shirine babba...
★★★.....
Wani shegen murmushi Kainaat ta saki tana taɓe baki. A ranta tace haba yaro bakai kana jin kai ɗan iska bane kana a ganiyar balaga. Indai takamarka kai shege ne nan ma gidan ka taras, waya gaya maka ana shiga gonar Kainaat a fita lafiya babu tabon sarin maciji koda a yatsan ƙafa ne. Ai wasan yanzu ma aka fara, da kanka zaka min abinda nake so kafin ma cikar sati ɗaya. Amma hakan bazai hanani hukunta shegiyar matarka ba tunda ita batasan taci arziƙin a rabu lafiya ba. Taja tsaki tare da fisgar wayarta ta shiga danne-danne tamkar batajin hargowar da yake da jijjiga ƙofa. Wayar na gab da tsinkewa Nadwa ta ɗauka. Cikin yanayin barci ta ce, “Hello”.
“K malama watsakke a wannan barcin nice”.
Da mamaki Nadwa dake tashi zaune tana murzar ido tace “Amarya a wannan daren, ina kika bar mijin naki ke kuwa dan ALLAH. Wai badai da gaske kike bazaki bashi kanki ba?”.
“Humm share ba wannan bane yasa na kiraki Nadwa, so nake da safe ki sanarma Mommy ina son a aika matar nan taje min wajan malamin nan da yay min aiki akan Abaan ina amarya. Ina son a gobe Dafeeq ya saki matarsa”.
“What! Haba! Haba Kainaat mi kuma ya kaiki wannan tunanin? Dan ALLAH kada ki raba ma'auratan nan Please and please. Keda ba zama kikaje yi ba miya kawo miki wannan tunanin a daren nan? Ni dai babu ruwana dan ALLAH kada kiyi haka akan yarinyar nan da abinma tausayi ce. Ki barta da zalincin da yake mata ma na zubar mata da ciki”.
“Haba kema kin san ganganne na ƙyale cuta ban rama ba. Ai rama cuta ga macuci ibada ce. Har ke kike tunanin wai babu ruwanta. Wlhy duk da ban auri mijinta dan na rayu da shi ba ita bata isa ta shiga gonata na ƙyaleta ba. Da ga safiyar yau zuwa daren nan tamun abinda sai ta san ta shiga gonata wlhy”.
“Ya ALLAH calm down mana Kainaat. Mita miki?”.
Kamar bazata faɗa mata ba sai kuma ta kwashe komai ta sanar mata. Tare da ɗorawa da wannan hukuncin nasu ne su biyu, duk da kuwa shima na tabbata dama wannan shine burinsa a kanta ƙarshe. Dan maza irinsu da sukai auren wuri kuma irin kalar auren nan daga ƙarshe mawuyaci ne basu sake su ba kosu ƙaro musu kishiya. To ni zan rabasu ne a gaɓar da suke buƙatar junansu dan ubansu. Duk da ban auresa dan na zauna dashi ba shi har ya isa ya ɗauki kwanana ya kai mata, tsabar son zubar min da mutunci a wajen ƴar cikina kwana ɗaya da auro ni. Ai wannan cin mutunci yakai cin mutunci”.
“To amma baki ganin kema akwai laifinki? Maybe a matse yake bawon ALLAH kin hanashi kanki kin bashi kuɗi tayaya kike ganin tunda yasan yanada wata matar bazaije gareta ba. Ni dai dan ALLAH ki barsu, abinda kika faɗa mata ma kawai ya isa punishment a gareta, shiko nanda sati ɗaya zaki masa nashi punishment ɗin tunda ya saki jiki aure yay kamar kowa zaici banza, bai san nan da kwanaki komai daya samu ba ma zai rasa shi. Hakan kawai ya ishesa ai”.
“Ina hakan yamun kaɗan, idan bazaki min yanda nake so ba barshi, bara na kira Mommyn da kaina dama dan naga darene bana son tadata a barci, kuma so nake tunda safe aje a amso min”.
“A'a miyay zafi, saƙonki kam zan isar in dai nice. Ni dai shawara na baki dan ina tsoratar miki abinda zai iya zuwa ya dawo. Tunda ba gama sanin halin yarinyar nan kikai ba. Koda kike ganinta ƙarama maybe itama ta iya nata kalar hatsabibancin. Kigafa yanda ta maida miki magana har sau biyu”.
“Mtsoww! Riƙe shawararki malama”.
Kainaat ta faɗa tana yanke wayar. Jefar da ita tai gefe tayi kwanciyarta batare fatabi takan Dafeeq dake cigaba da kiran sunanta yana ƙwanƙwasa ƙofar ba. Sai ma taja headphones dake cikin bedside drawer ɗin ta ta saka abinta, daga haka tabar jinsa gaba ɗaya...
Matuƙar tashin hankali Dafeeq ya shiga. Ta ina matar nan ta samo wannan sirrin nasa da yasan da ga shi sai ALLAH sai likitan nan suka sani. Sannan zuwa gida da yake yi kuwa shi kaɗai ya sani sai UBANGIJI. Dan tun bayan aurensu da wata biyar ya yanke shawarar zuwa ga iyayensa kasancewar labari ya sameshi mamansa ta samu karaya a ƙafa. Koda yaje bai wani sha wahalar shawo kansu ba dan suna son sa kamar mutuwa sakamakon shi kaɗai suka haifa a duniya. Bai yarda ya faɗa musu a ina yake ba, ya kuma sanar musu ya saki Khadijah tun kafin yazo garesu saboda yaga basa so, yanzu neman kuɗi yake yi dan ya koma karatu. Sun ji daɗi sosai suka dinga saka masa albarka. Kwanansa biyu batare da ya yarda kowa ya gansa ba ya dawo. Yayinda babansa ya shirya har gidan su Khadijah yaje yayima mahaifinta tas yace kuma su nema ƴarsu acan gidajen karuwar dan ɗansu ya sanar musu ya saketa. Hankalin iyayen Khadijah ya sake tashi, jikin babanta ya sake rikicewa sosai harta kaisa da samun paralysis. Yanzu haka yana kwance gefen jikinsa baya aiki. Karatun ƙannenta ya tsaya, sai da taimakon wani bawan ALLAH da yaga ƙanwarta mai bimata yana so ya maida yaran makaranta, ya kai Baba asibiti. Yanzu haka yana amsar magani jikinsa da ɗan sauƙi, ƙannenta biyu sun kammala secondary sun cigaba da karatu, an kuma saka musu ranar aure dan dama burin mahaifinsu shi dai su fara karatun sannan ya aurar dasu sa ƙarasa a gidan miji, amma Khadijah ta nuna masa bai isa ba. Ƴan anguwar su Khadijah kam da mutane da yawa sun yarda Khadijah tabi duniya saboda tsoron kada ta dawo gida Dafeeq ya saketa a mata dariya ko iyayenta suƙi karɓarta.
Tun daga lokacin duk wata sai Dafeeq yaje gida, dan hatta auren nan na Kainaat iyayensa sun san zaiyi, hasalima a kuɗin data dinga bashi har gidansu yaje ya gyara tare da ƙarama babansa jari........✍️
_🥱 Dafeeq anya zakaga ANNABI ALLAH kuwa🤦🥲🚶_
_Khadijah ke kuma ƙya dawo hankalinki ai yanzu. Koda yake baki ji sauran labari ba ma😩_
_Ke kuwa Kainaat bakiyi wawtaba kuwa?, dan Dafeeq fa Hummm😆_
_JJ banda abin cewa a kanka kai kam yau🥲, na barka da masu karatu da su Alimah suci min ubanka bunsurun banza🧑🦯
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na bakwai_
INA ƳAN KASUWA MASU SON ƘAWATA KASUWANCINSU TA HANYAN GRAPHIC DESIGN, DA MASU SHIRIN BIKI, KO SUNA, DA MASU SHIRIN WALIMAR SAUƘA, DA MASU SHIRIN YIN BIRTHDAY, KAI HARMA DA MASU ANNIVERSARY 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼
MAZA KU GARZAYO "UMMUH FARUQ GRAPHIC DESIGN "TA TANADAR MUKU DA HAƊAƊƊUN DESIGN MASU ƘAYATAR DA MAI KALLONSU.🥰🥰🥰
KAMA DAGA
*FLYER
*3D MOCKUP LOGO
*2D MOCKUP LOGO
*NORMAL LOGO
*IMAGE LOGO
*BANA
*STICKERS
*ADVERT VIDEO
*PROFESSIONAL INVITATION
*INVITATIONS CARD
*BIRTHDAY VIDEOS
*POSTER
*CERTIFICATE.AND MORE......
CONTACT ME ON
👇
09035390383
____________
.......“Please Kainat yaya kika san duk wannan wai?”.
“Humm Nadwa kenan. Na faɗa miki Kainaat ba shashasha bace ba ai, kin san dai bazan jashi jikina ban san wanene shi ba. Inama da fiye da wannan game da shi, sai dai lokaci ne zai sa ki san sauran gaba ɗaya ba yanzu ba”.
Idanu kawai Nadwa ta zuba mata cike da mamaki da tsoro. Maganar gaskiya bata son ƙawar tata tace zata shiga tsakanin waɗan nan ma'auratan dake tsaka da cin ƙuruciyar soyayyarsu. Amma ta santa tasan halinta, in har tace tana son abu sai ta cimma burinta a kansa, dan ita shaidace ko akan Don Abaan da yanda ya fara sonta har sukai aure shirine babba...
★★★.....