Sashe 77
Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
___________________
.......“Minene sunansa?”.
A matuƙar rikice Mami ta ɗago ta kalli Daddy da yay maganar. Sai dai a mamakinta hankalinsa nakan tv ne da ake labarai ma. Juyawa tai ta kalli inda Ammie take. Itama dai ba ita take kallo ba shayi ma take ƙoƙarin zubama Daddy ɗin. Sashin su Muhammad ta juya, sai taga wayam alamar sun tashi gaba ɗayansu daga falon....
“Nace minene sunansa?”.
Daddy ya sake maimaitawa a karo na biyu yana mai katse Mimi dake dube-dube. Kuka ta fashe da shi tana girgiza masa kanta. “Dan ALLAH Daddy kayi haƙuri natuba. Wlhy bazan sake kulashi ba. Na maka alƙawari”.
“Fateema! Nace minene sunansa?”.
Kaɗan ya rage kam a yanzu zuciyar Mimi ta ɓaro jin ainahin sunanta a bakin mahaifin nata. Abu mai wahalar gaske kaji ya faɗa kuwa. Ƙaruwa rawar jikinta ta ƙara. Cikin matuƙar rawar harshe ta ce, “D...d...daddy Ya...zee...d!”.
“Waye babansa?”.
“Abdul-kareem Waziri. Ministarn Abuja”.
“Tun yaushe kuke tare?”.
Kuka ta fashe da shi har sai da Daddy ya daka mata tsawa.
“Nace tun yaushe kuke tare?!”.
“Ka k....kayi haƙuri Daddy wata huɗu kenan. A wajen dinner ɗin bikin Uncle Awwal”.
“Fateema aure kike so?”.
“Daddy wlhy wlhy kaji na rantse maka a'a. Shima na faɗa masa ya daina zuwa ni karatu zanyi. Amma yaƙi yarda Daddy. Shine yake bini har school. Ko nace bazanje ba sai yayta roƙana kamar zai yi kuka. Wataran ma har kukan yake min. Amma wlhy Daddy ba aure nake so ba. Kuma wlhy na maka alkawarin bazan sake binsa ba”.
“Bani Number sa”.
“Daddy Dan ALLAH na roƙe ka...”
Tsawa ya sake daka mata mai firgitarwa da har sai da ta sakata zabura tana sake fashewa da kuka. Cikin ɓacin rai da bata taɓa sanin Daddyn nasu ma da shi ba dan shi mutum ne mai saukin kai sosai. Yakan zauna yay hira yay wasa da dariya da su. Wani lokacin ma Ammie ta fisa zafi. Wayarta gaba ɗaya ya amshe ma. Sannan yace ta tashi ta bashi waje. Haka ta tashi tana kuka da magiyar roƙon suyi haƙuri su yafe mata shi da Ammie bazata sake ba. Amma babu wanda ya saurareta ya korata.
Koda tabar falon da ga shi har Khadijah babu wanda yace da ɗan uwansa komai. Dan wayar tata ma gefe ya ajiye ta ya cigaba da kallon labaransa. Sai goma dai-dai suka tashi suka haye sama bayan sun leƙa ɗakunan yaran nasu har Mimi ɗin. Sun sameta a saman sallaya tana karatun Alqur'ani. Babu wanda yay mata magana a cikinsu suka maida mata ƙofar suka rufe. Sama suka haye. Sai bayan sunyi shirin barci Khadijah na daga jikin mirror tana saka turare shi kuma yana a bakin gadon zaune ya ɗauki wayar Mimi. Bincike ya farayi lungu da saƙo na wayar dan babu password, hakan dokace da ga Ammie. Sai da ya gama bincike wayar tsaf yana ɗan sauke ajiyar zuciya ganin babu wani abin tada hankali sai text messages na soyayya mafi yawa ma yaron ne ya tura mata. Sai wasu ta WhatsApp da hotunanta data tura masa shima ya tura mata nashi. Dukansu kuma da hijjab ma tayi su. Shima kuma cikin kamala yake. Iskar samun nutsuwa ya furzar. Kafin a hankali ya ɗago ya kalli Khadijah dake kallonsa. Hannu ya miƙa mata alamar tazo gareshi. Babu musu ta nufesa. Jikinsa ya jawota suka faɗa saman gadon. Da ga haka yaja musu bargo yana sumbatar kumatunta da faɗin, “Ki ɗan yi murmushi mana Baɗɗo am”.
Murmushin ta ɗanyi da sake shigewa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. Shima sai ya sauke tasa ajiyar zuciyar yana sake rungumeta da ƙyau...
*_WASHE GARI_* kamar yanda suka saba duk suka fita aiki. Yaran kuma makaranta har Mimi. Sai dai yau Daddy da kansa ya kai su makarantar. Ya kuma hana Mimi fita. Suna zaune a mota ita da shi sai ga kira ya shigo a wayarta dake hannunsa. Miƙa mata yay babu alamar wasa a fuskarsa yace “Ki amsa masa kamar yanda kika saba”. Kanta ta jinjina tana share hawaye. Ganin yanda mahaifin nata ya tsareta da ido dole ta amsa ɗin. Suna gamawa ya amshe wayar yace mata taje inda yake. Kuma koda wasa ta sanar masa tare suke sai ya mata dukan mutuwa. Tana hawaye ta amsa masa. Tsawa ya mata akan ta share hawayen. Haka ta gogesu tsaff ta gyara yanayinta sannan ta fita bisa umarninsa.
Tana shiga motar suka bar wajen . Bayansu yabi har garden ɗin da Ammie ta dinga bibiyarsu. Sai da suka fita a motar suka sami wajen zama Mimi dai duk a ɗarare sannan ya fita zuwa inda suke. Koda Yazeed yay tozali da Alhaji Abaan gabansa rikicewa yay. Dan kuwa mahaifin Mimi ba ɓoyayyen mutum bane. Sannan duk wanda ya kalleta ya kallesa yasan shine mahaifinta. Jikin Yazeed na rawa ya kai har ƙasa yana gaida Abaan. Amsa masa yay tare da masa nunin ya tashi. Batare da yace komai ba yace su biyosa. Ganin babu alamar wasa a tattare da shi Yazeed ya bisa babu musu. Ita dama Mimi yasan bata isa yin musun ba. A motarsa ya ɗebesu su duka aka bar ta Yazeed anan. Mami na baya Yazeed na gaba kusa da Daddy.
Hankalin Yazeed ya tashi ganin gidansu suka zo. Bai sake ruɗewa ba sai da aka buɗe musu gate yaga motocin mahaifinsa na nan alamar bai fita ba. Ita dai Mimi bata san nan ne gidan su Yazeed ba. Sai da akai musu iso ciki suna shiga tai tozali da mahaifin Yazeed ɗin. Duk sai itama taji ta sake rikicewa.
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
___________________
.......“Minene sunansa?”.
A matuƙar rikice Mami ta ɗago ta kalli Daddy da yay maganar. Sai dai a mamakinta hankalinsa nakan tv ne da ake labarai ma. Juyawa tai ta kalli inda Ammie take. Itama dai ba ita take kallo ba shayi ma take ƙoƙarin zubama Daddy ɗin. Sashin su Muhammad ta juya, sai taga wayam alamar sun tashi gaba ɗayansu daga falon....
“Nace minene sunansa?”.
Daddy ya sake maimaitawa a karo na biyu yana mai katse Mimi dake dube-dube. Kuka ta fashe da shi tana girgiza masa kanta. “Dan ALLAH Daddy kayi haƙuri natuba. Wlhy bazan sake kulashi ba. Na maka alƙawari”.
“Fateema! Nace minene sunansa?”.
Kaɗan ya rage kam a yanzu zuciyar Mimi ta ɓaro jin ainahin sunanta a bakin mahaifin nata. Abu mai wahalar gaske kaji ya faɗa kuwa. Ƙaruwa rawar jikinta ta ƙara. Cikin matuƙar rawar harshe ta ce, “D...d...daddy Ya...zee...d!”.
“Waye babansa?”.
“Abdul-kareem Waziri. Ministarn Abuja”.
“Tun yaushe kuke tare?”.
Kuka ta fashe da shi har sai da Daddy ya daka mata tsawa.
“Nace tun yaushe kuke tare?!”.
“Ka k....kayi haƙuri Daddy wata huɗu kenan. A wajen dinner ɗin bikin Uncle Awwal”.
“Fateema aure kike so?”.
“Daddy wlhy wlhy kaji na rantse maka a'a. Shima na faɗa masa ya daina zuwa ni karatu zanyi. Amma yaƙi yarda Daddy. Shine yake bini har school. Ko nace bazanje ba sai yayta roƙana kamar zai yi kuka. Wataran ma har kukan yake min. Amma wlhy Daddy ba aure nake so ba. Kuma wlhy na maka alkawarin bazan sake binsa ba”.
“Bani Number sa”.
“Daddy Dan ALLAH na roƙe ka...”
Tsawa ya sake daka mata mai firgitarwa da har sai da ta sakata zabura tana sake fashewa da kuka. Cikin ɓacin rai da bata taɓa sanin Daddyn nasu ma da shi ba dan shi mutum ne mai saukin kai sosai. Yakan zauna yay hira yay wasa da dariya da su. Wani lokacin ma Ammie ta fisa zafi. Wayarta gaba ɗaya ya amshe ma. Sannan yace ta tashi ta bashi waje. Haka ta tashi tana kuka da magiyar roƙon suyi haƙuri su yafe mata shi da Ammie bazata sake ba. Amma babu wanda ya saurareta ya korata.
Koda tabar falon da ga shi har Khadijah babu wanda yace da ɗan uwansa komai. Dan wayar tata ma gefe ya ajiye ta ya cigaba da kallon labaransa. Sai goma dai-dai suka tashi suka haye sama bayan sun leƙa ɗakunan yaran nasu har Mimi ɗin. Sun sameta a saman sallaya tana karatun Alqur'ani. Babu wanda yay mata magana a cikinsu suka maida mata ƙofar suka rufe. Sama suka haye. Sai bayan sunyi shirin barci Khadijah na daga jikin mirror tana saka turare shi kuma yana a bakin gadon zaune ya ɗauki wayar Mimi. Bincike ya farayi lungu da saƙo na wayar dan babu password, hakan dokace da ga Ammie. Sai da ya gama bincike wayar tsaf yana ɗan sauke ajiyar zuciya ganin babu wani abin tada hankali sai text messages na soyayya mafi yawa ma yaron ne ya tura mata. Sai wasu ta WhatsApp da hotunanta data tura masa shima ya tura mata nashi. Dukansu kuma da hijjab ma tayi su. Shima kuma cikin kamala yake. Iskar samun nutsuwa ya furzar. Kafin a hankali ya ɗago ya kalli Khadijah dake kallonsa. Hannu ya miƙa mata alamar tazo gareshi. Babu musu ta nufesa. Jikinsa ya jawota suka faɗa saman gadon. Da ga haka yaja musu bargo yana sumbatar kumatunta da faɗin, “Ki ɗan yi murmushi mana Baɗɗo am”.
Murmushin ta ɗanyi da sake shigewa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. Shima sai ya sauke tasa ajiyar zuciyar yana sake rungumeta da ƙyau...
*_WASHE GARI_* kamar yanda suka saba duk suka fita aiki. Yaran kuma makaranta har Mimi. Sai dai yau Daddy da kansa ya kai su makarantar. Ya kuma hana Mimi fita. Suna zaune a mota ita da shi sai ga kira ya shigo a wayarta dake hannunsa. Miƙa mata yay babu alamar wasa a fuskarsa yace “Ki amsa masa kamar yanda kika saba”. Kanta ta jinjina tana share hawaye. Ganin yanda mahaifin nata ya tsareta da ido dole ta amsa ɗin. Suna gamawa ya amshe wayar yace mata taje inda yake. Kuma koda wasa ta sanar masa tare suke sai ya mata dukan mutuwa. Tana hawaye ta amsa masa. Tsawa ya mata akan ta share hawayen. Haka ta gogesu tsaff ta gyara yanayinta sannan ta fita bisa umarninsa.
Tana shiga motar suka bar wajen . Bayansu yabi har garden ɗin da Ammie ta dinga bibiyarsu. Sai da suka fita a motar suka sami wajen zama Mimi dai duk a ɗarare sannan ya fita zuwa inda suke. Koda Yazeed yay tozali da Alhaji Abaan gabansa rikicewa yay. Dan kuwa mahaifin Mimi ba ɓoyayyen mutum bane. Sannan duk wanda ya kalleta ya kallesa yasan shine mahaifinta. Jikin Yazeed na rawa ya kai har ƙasa yana gaida Abaan. Amsa masa yay tare da masa nunin ya tashi. Batare da yace komai ba yace su biyosa. Ganin babu alamar wasa a tattare da shi Yazeed ya bisa babu musu. Ita dama Mimi yasan bata isa yin musun ba. A motarsa ya ɗebesu su duka aka bar ta Yazeed anan. Mami na baya Yazeed na gaba kusa da Daddy.
Hankalin Yazeed ya tashi ganin gidansu suka zo. Bai sake ruɗewa ba sai da aka buɗe musu gate yaga motocin mahaifinsa na nan alamar bai fita ba. Ita dai Mimi bata san nan ne gidan su Yazeed ba. Sai da akai musu iso ciki suna shiga tai tozali da mahaifin Yazeed ɗin. Duk sai itama taji ta sake rikicewa.