← Book details Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 82

Sashe 14

Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da ƙyar aka iya tara-tara wajen kamashi, wani dattijo maƙwafcinsu ya cire babbar rigarsa aka sakamasa. Gudun da yaci yasa numfashinsa gaba ɗaya ya koma fita da ƙyar, da ga ƙarshe ma ganin yana neman shiɗe musu dole akai gaggawar wucewa asibiti mafi kusa da shi, dan ya matuƙar birkice musu tamkar mai Asthma. An amshesu da gaggawa aka saka masa oxgyn kafin likita ya tsaya a kansa. Da ga ƙarshe dole akai masa allurar barci mai nauyin gaske dan doctor ya tabbatar da in har aka barsa ido biyu brain ɗinsa na gab da susucewa. Zuciyarsa kuwa bugunta ya wuce musali alamar yana cikin matsanancin tsoro ko tashin hankali.
Bayan likita ya tabbatar musu su kwantar da hankalinsu sun ɗan samu nutsuwa, sai a lokacin suka samu tattaunawa akan batun wannan tashin hankali haka. An yanke shawarar barin wasu anan asibitin, wasu kuma suka nufi gidan JJ ɗin domin bincika abinda ke faruwa.

Sun sami gidan kaca-kaca tamkar anyi yaƙi a cikinsa musamman ma falon. Dan komai an birkitashi da ga mazauninsa zuwa wani waje daban. Ba mamaki kawai ba harda birkicewar tunani ya samesu. Musamman ma Baba da yasan a jiya sune na ƙarshen barin gidan, kuma sun bar komai tsaff da shi tamkar an zana. Amma yanzu gaba ɗaya ya koma kamar ɗakin ajiye shara. Ruɗani na biyu shine rashin ganin Alimah da basuyi ba, hakan na nufin itama tabar gidanne kokuwa yaya ne?. Suna tsaka da dube-dube sukaji kamar ana kuka, da sauri Yaya Mujee ya nufi inda yake jiyo sautin kukan. Can bayan ɗakunan ne, fitowa sukai su duka zuwa inda kukan ke fitowa, tun daga nesa suka hangota a wani ɗan lungu takure.
“Subahanallahi! Alimah kece anan?”. Yaya Mujee ya faɗa har yanayi kamar zaici tuntuɓe sai da Yaya Inusa ya ruƙosa. Su duka inda take suka isa suna kiran sunanta, sai dai babu alamar zata ɗago. Kusan mintuna uku suna faman lallashi da lallaɓata amma taƙi tako motsa sai ƙarama ƙarfin kukanta take.
“To ko dai za'a kira iyayenta ne?”.
Cewar Baba yana kallon ƴaƴan nashi. Yaya Inusa ne ya amsa masa da, “To gaskiya kam Baba hakan zaifi nake ga. Dan al'amarin naga ba ƙarami bane ba”.
Waya Baba ya zaro da shirin kiran mahaifin Alimah, tamkar wadda aka zabura sai gata tai wani irin ɗagowa gashinta dake wargaje yayi bulahh fuskarta ta bayyana. A kusan tare Baba, Yaya Mujee, yaya Inusa suka zabura jikunansu na rawa. Dariya ta kwashe da shi tare da miƙewa tsaye gaba ɗayanta. Ai kafin ma kace takk ƙafa mi naci ban baki ba. Tuni tsakanin Baba da su Yaya Mujee an fara gudun wuce sa'a. Kowa burinsa ya kai ga ƙofa. Babu mai tunawa da girman na gaba da shi ko ƙanƙanta. Faɗuwar Baba biyu kafin suje gate, amma babu wanda yako waigo domin taimakonsa tsakanin Mujee da Inusa. Sai shi ke taƙarƙarawa ya tashi har dai ALLAH ya taimakesu suke fice.
Tofa, ƴan anguwa da dama ke'a ɗari-ɗari tun daga fitowar JJ yanzu fa sun sake tabbatar da babu lafiya. Tuni aka fara ƴar rere ƴaƴa da mata kasancewar mazan duk sun fice wajen nema. Ga shi sabuwar anguwa ce dama. Bakajin komai sai ihun mata da kukan yara. Ga shi su Baba sunƙi tsayawa, dan suma kansu sun rarrabu kowa yayi titi. Duk wanda kuma ya samu abin hawa baya neman ɗan uwansa yake afkawa kawai..........✍️

_😂To gaskiya akwai matsala. Uncle JJ anya kuwa ba sarauniyar aljanu ka kwaso mana ba a family 🤣🙏_.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_Shafi na tara_

......Da ɗai-ɗai suka dinga isowa gidan. Hakan ya sake ɗaga hankalin mata dake cike da gidan ana jajantawa. Dan duk yanda akaso suyi bayani kasancewar an san sunje can gidan haka ya gagara. Baba ne kawai ke iya maimaita kalmar, “Akwai matsala. Gidan Jazool babu lafiya ƙwarai da gaske”.
     Zugum-zugum akai kowa na sauraren baba cikin ƙara tsorata da jimantawa. Sai da suka samu nitsuwa kusan ta awa ɗaya sannan suka bada labarin abinda ya faru. Yanda Yaya Mujee ke siffanta sunga Alimah tamkar irin horror ɗin nan ya hargitsa zukatan mutane. Yanda wasu suka firgice ma sai ka ɗauka da su aka gano. Yaya Inusa da baice komai ba tun ɗazun cikin damuwa ya ce, “Baba dole ne fa a nema iyayen yarinyar nan akan lokaci. Dan abinda na fahimta gidan nan na Jazool akwai aljanu, kuma da alama sun shiga jikin matarsa”.
      “Gaskiyarka Inusa dole aɗauki mataki da wuri kam, dan barin yarinyar can a wannan halin ita kaɗai akwai tashin hankali. Bari muga a lalubo mahaifin nata”.
   Kowa dake wajen ya gamsu da zancen Baban. Yayinda tausayin Alimah da JJ ya sake mamaye zukatan kowa. Sam Baba ya kasa samun number ɗin mahaifin Alimah, dole ya yanke hukuncin idan sun idar da sallar la'asar zaije shi da Yaya Mujee gidan su Alimah ɗin.

       Bayan idar da sallar la'asar suna shirin wucewa gidan su Alimah kira ya samesu daga asibiti cewar JJ fa ya farka a wani yanayi. Dan a yanzu haka ma rirriƙe ake da shi. Dole su Baba suka saki zancen zuwa gidan su Alimah suka tafi asibiti. A yanayin da suka sami JJ kam abun akwai tausayi, ga likitoci sun tabbatar da su basuga komai a tattare da shi ba. Brain ɗinsa lafiya lau take. Hakama fatarsa babu wata damuwa amma ga wasu irin ƙananun ƙuraje sun maidashi butsaaa babu ƙyawun gani tamkar jikin kada. Su baba da suka fahimci komai a yanzu roƙonsu sukai kan su masa allurar barci kawai zasu wuce da shi gida. Dan sun gano bakin zaren shafar aljanu ce. Wannan shine dalilin dawo da JJ gida aka nemo malamai suka rufu a kansa.
         An masa addu'oi sosai duk da yana barci, sai aka kuma yanke shawarar bari har sai ya tashi. Har dare babu alamar JJ zai farka. Dan takai amma fara tsorata da barcin nashi. Ga su Baba ana idar da magrib suka fantsama gidan su Alimah, sai dai sun sami gida a garƙame da kwaɗo, da sukai tambaya kusan mutum uku suka sanar musu ai wannan gida ya kai shekara huɗu a rufe tun bayan rasuwar masu gidan, hasalima a yanzu ƙarƙashin kulawar ƴan sanda yake. Matuƙa kansu baba ya kulle, sai dai rashin lokaci ya sakasu yanke shawarar ajiye wannan batun har safiyar gobe suka nufi gidan JJ domin ceto Alimah tare da malam nan dan a barota da gidan. Dan malam ne suka bada shawarar a fara zuwa a ceto yarinyar da safe sai a nema iyayen nata saboda dare ya riga ya fara. Haka dole badan Yaya Mujee yaso ba suka nufi gidan JJ. Sun sami gate ɗin gidan yanzu a rufe. Iya ƙoƙarin suga sun buɗe hakan ya gagara. ALLAH ya taimaka akwai extre kay a hannun maƙwafcinsa, dan haka ya ɗakko. Da yawansu suka shiga gidan kasancewar mazan anguwa duk sun dawo, sai dai suna gama shiga ƙofar gate ta tafi da kanta ta datse ji kake gammm!!!. Gaba ɗayansu babu wanda gabansa bai mahaukacin faɗi ba. Dan duk a birkice suka juyo suna kallon ƙofar gate ɗin. Yayinda masu ƙarfin hali suka ɗauki addu'a a bakunansu.
     Cikin ƙarfin hali maƙwafcin JJ ya ce, “Iska ce ta rufe ƙofan, dama tanayin hakan tun ana aikin gidan”. Wasu sun ɗan ji mutsuwa, yayinda wasu dai sun haƙurane kawai dan ganin sunada yawa. Akwai wuta a gidan tako ina dan anguwar suna samun wutar nepa sosai. Cikin gidan suka nufa kowa na addu'a. Baba da malaman ne a gaba, sai ƴan anguwa da masu son ganin ƙwaf da suka biyosu daga can gida. Basu sami Alimah a inda suka bartaba ɗazun, sai dai inda ta zauna duk jini ne, sai kuma sawun ƙafarta da tambarin jinin ya tafi har hanyar back door na kitchen. Hankalin kowa ya tashi da ganin jinin nan, amma cikin ƙarfin hali haka aka ɗuru cikin falon kowa na karanta addu'a.
     Bbaaammmm!! Kake jin ƙofa ta datse kanta anan ma. A yanzu kam ai babu batun yarda da cewar iska ce ta rufe. Kusan gaba ɗayansu suka kalli ƙofar falon hankali a tashe. Bammm!! Ta Back door ɗin itama ta bada sautin rufewa harda ƙarar saka sakata. Yanzu kam rawar jiki ɗan gaske kowa ya fara, musamman ma ƴan son ganin ƙwaf ɗin nan da mazan anguwa. Malaman nan kam sun fara karatu cikin ƙarfin hali. Tsitttt babu wani abu da ya sake motsa kansa a gidan, zamaka iya ɗauka hatta iskar dake kaɗawa ta tsaya ne itama. Farrr-farrr wutar gidan ta fara rawa. Cikin sauri suka fara dunƙulewa waje guda, masu tsoron tsiya a cikinsu har fitsari ya cika musu mara, masu ƙarfin hali na taya malaman nan addu'oi. Ɗifff wutar ta ɗauke gaba ɗaya, duhu mai tsanani da ko tafin hannunka baka iya gani ya mamaye gidan duka. Sai ga mazajen fama na rungumar juna masu guntun fitsari na fara ɗiga.....

       🚴🚴taɓ bara na fece alkur'an. Yo ƴan maza na cikin wanga yanayi mu ƴan mata sai muyi yaya, ai fecewar kawai ta ragemun tunda ni mai ɗaukar rohoto ina iya tashi sama kamar jirgi🤣🤣.

_________★★★★

*_Aslm hajiyata miye matsalar gashinki? Rashin tsawo ne ko cunkushewa gareshi ko kuma baqi kikeso yayi da santsi ne? Ga garin itatuwa na kawo maki mai fito da gashi har har gadon baya cikin sati biyu kacal._*

*_Sannan na kawo maki back to virgin wanda ko haihuwa nawa kikayi zaki matse cikin qanqanin lokaci ki koma kamar budurwa, har oga sai ya rasa gane shin wani aure yayine ko canza mashi mata akayi._*

*_Daɗin daɗawa kuma ga saiwar breast wanda zata gyara maki boost ɗinki cikin qanqanin lokaci ki koma kamar budurwa abinki.....hmmm hajiyata wani abun sai kin gwada zakiyi man godiya......ke dai tuntubarni ta wannan number ɗin domin qarin bayani 09032237835._*

___________★★
Chapter 14 · 0% Book details