Sashe 52
Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Sosai kayan sukaima Khadijah ƙyau tamkar ka saceta. Ga shi itama kuma ALLAH ya azurtata da gashi, dan har Aunty Firdausi na tsokanarta da ai da ansan zasuyi wannan wasan da an mata kitson fulanin itama tunda dai ta alaƙantu da su ta fannin uwa. Dariya wanda ke ɗakin sukayi kowa na faɗin albarkacin bakinsa. Ita dai Khadijah bata tanka musu ba dan takanta take. Ga zazzaɓi ga fargabar tunanin kowane irin miji kuma zata tarar a yanzu. Shin shima irin Dafeeq ne ko yamafi Dafeeq abubuwan mamaki. Dan itakam a yanzu bata jin bayan mahaifinta al'amarin wani namiji na birgeta a wannan rayuwar. Kawai dai ayi sha'ani ne.
Sai da aka yafa mata gyale aka rufe mata fuska sannan suka fito. Duk da ba ganin fuskarta akeba sai ambaton masha ALLAH dangin ango keyi ganin yanda kayan sukai matuƙar zama a jikin amaryar tasu. An zaunar da itane kusa da surukarta daketa faman jin daɗin sake ganin wannan rana da ranta, ta riƙe hannunta cikin nata. Zafi taji sosai da ya sakata ambaton “Ya Salam daughter baki da lafiya ne haka amma baku faɗa ba?”. Kasa cewa komai Khadijah tai, dan duk da bataga fuskar matar ba har yanzu wani kalar kwarjini da girmanta take ji cikin ranta. Jikinta ta ɗan saka Khadijahn tare da kiran wata ƙyaƙyƙyawar matashiya mai tsananin kamanni da ita. Gabansu ta tsugunna tana murmushi da dafa ƙafarsu su duka biyun, sai kuma ta ɗaga gyalen zata leƙa Khadijah. Harararta Mamy tayi da buge mata hannu. Tai ƴar dariya da faɗin, “Kai Mamy na ƙagarane fa naga amaryan Hamma”.
“To bazaki gani ba”.
Mamy ta faɗa tana hararta. Hannu ta ɗaga alamar surrender tana murmushi. “Shike nan na haƙura Mamy, amma kamar jikinta da zafi.”
“Eh shine dalilin da yasa ma na kiraki nan ai. Yayanki basu iso ba har yanzu, inaga kiyi magana da Yafendo ayi komai a takaice Dota ta koma ciki, sannan ki nema min number doctor”.
“Okay Mamy”.
Ta faɗa tana miƙewa. Kamar jira tashinta babu jimawa aka wangale gate. Motace ta shigo, rashin wadatacce fili kasancewar sun mamaye harabar gidan yasa sukai parking can nesa. Kowa yasan ango ne ya iso, dan can Kano suka barsa sai yanzu yake isowa. Jirgin ƙarfe bakwai suka biyo alhmdllh kuma gashi har sun iso. Driver da yaje ɗaukarsu ne ya fara fitowa. Sai Awwal dake gefensa shima ya fito. Shiko yana baya bayansa jingine da kujera idanunsa a lumshe. A kallo ɗaya zaka fahimci a gajiye yake. Dan koda driver ya buɗe masa motar ya ɓata kusan minti ɗaya kafin ya fito. Cikin rashin hayaniyar nan tasa yacema drivern “Thanks you Baba. Mun hanaka barci ko”.
Murmushi Baba yay da faɗin, “A haba Alhaji ai yima kaine. Sannunku da zuwa dai, ALLAH kuma ya sanya alkairi a cikin wannan aure. Yasa yanda muka taru anan baɗi i war haka muna nan muna shagalin suna kuma”.
Awwal ne ya amsa da amin yana ƙumshe dariya. Shiko ya ɗan murmusa kawai batare da yace komai ba sai dai a zuciyarsa ya amsa da Amin. Dan sosai yake son yara shima, kawai dai ana ganin kamar bai damu bane saboda bai cika yawan furtawa ba. Idanunsa ya kai inda ake taron, hankalin wasu duk na garesu ne, yayinda wasu kuma ke hidimarsu batare da sun farga da su ba. Tunanin ta yanda zai shige sashensa batare da wani ya tsaida shi ba yake. Sai dai bai kai ga samo mafitarba ma ƴan uwa suka fara zagayesa ana masa sannu da zuwa da jera masa kirarin ango ango kasha ƙamshi. Kamar yanda ya saba ne, murmushi kawai yake musu a taƙaice. Ganin suna neman cika wajen ya zare jikinsa ya gudu ta baya zuwa sashensa dake manne dana amarya. Sai dai da yake akwai ƙofa ta gaba da baya da basai dole yabi ta cikin falon Khadijahn ba yasa zaka iya ɗauka ma daban-daban ne. Shigewarsa babu jimawa Mammy tasa aka maida Khadijah ciki dan rawar sanyi take yi. An cigaba da gudanar da shagali Noor kuma taje ta sanar ma Yayanta amarya bata da lafiya a kira Doctor. Fitowarsa kenan daga wanka sallamarta ya sashi zira jallabiyya ya fito falon. Agogo ya ɗan kalla sai kuma ya dubi ƙanwar tasa ɗaya tilo a duniya. “Amma miyasa tun ɗazun k baki kirashi, yanzu fa kusan 10 ake tafiya. Sannan kun zo da ita a wannan sanyin ita da bata da lafiya kuma”.
“Sorry Hamma Ab. Ai ba'asan bata da lafiya bane fa sai yanzu Mamy ta gane. Kuma yanzu haka ma an maidata ciki. Na kuma kira Doctor ɗin bai ɗauka bane maybe baya kusa”. Baice komai ba face ƙoƙarin sarrafa wayar hannunsa da ya ɗauka. Inda ya fito ya koma yana kai wayar kunnesa da yima Noor alamar taje kawai...
Sai da aka yafa mata gyale aka rufe mata fuska sannan suka fito. Duk da ba ganin fuskarta akeba sai ambaton masha ALLAH dangin ango keyi ganin yanda kayan sukai matuƙar zama a jikin amaryar tasu. An zaunar da itane kusa da surukarta daketa faman jin daɗin sake ganin wannan rana da ranta, ta riƙe hannunta cikin nata. Zafi taji sosai da ya sakata ambaton “Ya Salam daughter baki da lafiya ne haka amma baku faɗa ba?”. Kasa cewa komai Khadijah tai, dan duk da bataga fuskar matar ba har yanzu wani kalar kwarjini da girmanta take ji cikin ranta. Jikinta ta ɗan saka Khadijahn tare da kiran wata ƙyaƙyƙyawar matashiya mai tsananin kamanni da ita. Gabansu ta tsugunna tana murmushi da dafa ƙafarsu su duka biyun, sai kuma ta ɗaga gyalen zata leƙa Khadijah. Harararta Mamy tayi da buge mata hannu. Tai ƴar dariya da faɗin, “Kai Mamy na ƙagarane fa naga amaryan Hamma”.
“To bazaki gani ba”.
Mamy ta faɗa tana hararta. Hannu ta ɗaga alamar surrender tana murmushi. “Shike nan na haƙura Mamy, amma kamar jikinta da zafi.”
“Eh shine dalilin da yasa ma na kiraki nan ai. Yayanki basu iso ba har yanzu, inaga kiyi magana da Yafendo ayi komai a takaice Dota ta koma ciki, sannan ki nema min number doctor”.
“Okay Mamy”.
Ta faɗa tana miƙewa. Kamar jira tashinta babu jimawa aka wangale gate. Motace ta shigo, rashin wadatacce fili kasancewar sun mamaye harabar gidan yasa sukai parking can nesa. Kowa yasan ango ne ya iso, dan can Kano suka barsa sai yanzu yake isowa. Jirgin ƙarfe bakwai suka biyo alhmdllh kuma gashi har sun iso. Driver da yaje ɗaukarsu ne ya fara fitowa. Sai Awwal dake gefensa shima ya fito. Shiko yana baya bayansa jingine da kujera idanunsa a lumshe. A kallo ɗaya zaka fahimci a gajiye yake. Dan koda driver ya buɗe masa motar ya ɓata kusan minti ɗaya kafin ya fito. Cikin rashin hayaniyar nan tasa yacema drivern “Thanks you Baba. Mun hanaka barci ko”.
Murmushi Baba yay da faɗin, “A haba Alhaji ai yima kaine. Sannunku da zuwa dai, ALLAH kuma ya sanya alkairi a cikin wannan aure. Yasa yanda muka taru anan baɗi i war haka muna nan muna shagalin suna kuma”.
Awwal ne ya amsa da amin yana ƙumshe dariya. Shiko ya ɗan murmusa kawai batare da yace komai ba sai dai a zuciyarsa ya amsa da Amin. Dan sosai yake son yara shima, kawai dai ana ganin kamar bai damu bane saboda bai cika yawan furtawa ba. Idanunsa ya kai inda ake taron, hankalin wasu duk na garesu ne, yayinda wasu kuma ke hidimarsu batare da sun farga da su ba. Tunanin ta yanda zai shige sashensa batare da wani ya tsaida shi ba yake. Sai dai bai kai ga samo mafitarba ma ƴan uwa suka fara zagayesa ana masa sannu da zuwa da jera masa kirarin ango ango kasha ƙamshi. Kamar yanda ya saba ne, murmushi kawai yake musu a taƙaice. Ganin suna neman cika wajen ya zare jikinsa ya gudu ta baya zuwa sashensa dake manne dana amarya. Sai dai da yake akwai ƙofa ta gaba da baya da basai dole yabi ta cikin falon Khadijahn ba yasa zaka iya ɗauka ma daban-daban ne. Shigewarsa babu jimawa Mammy tasa aka maida Khadijah ciki dan rawar sanyi take yi. An cigaba da gudanar da shagali Noor kuma taje ta sanar ma Yayanta amarya bata da lafiya a kira Doctor. Fitowarsa kenan daga wanka sallamarta ya sashi zira jallabiyya ya fito falon. Agogo ya ɗan kalla sai kuma ya dubi ƙanwar tasa ɗaya tilo a duniya. “Amma miyasa tun ɗazun k baki kirashi, yanzu fa kusan 10 ake tafiya. Sannan kun zo da ita a wannan sanyin ita da bata da lafiya kuma”.
“Sorry Hamma Ab. Ai ba'asan bata da lafiya bane fa sai yanzu Mamy ta gane. Kuma yanzu haka ma an maidata ciki. Na kuma kira Doctor ɗin bai ɗauka bane maybe baya kusa”. Baice komai ba face ƙoƙarin sarrafa wayar hannunsa da ya ɗauka. Inda ya fito ya koma yana kai wayar kunnesa da yima Noor alamar taje kawai...