← Book details Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 82

Sashe 29

Cuta Ta Dau Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

A cikin abinda bai wuce mintinan arba'in ba ya iso. Sakatariyar ta ce ta tarosa har cikin office ɗin duk da kuwa shima ya sani tunda Companyn ba baƙonsa bane ba. Tunda ya shigo Kainaat ke masa wani irin shu'umin kallo a ƙasan ido. Tabbas Dafeeq ƙyaƙyƙyawa ne. Dan daka ganshi kaga bafulatanin usil. Duk da har yanzu shekarunsa basu gama tsayar da shi a namiji ba, amma kai daka ganshi kasan nan gaba ba ƙaramin ingarma za'ayi ba. Sai dai fa duk da wannan ƙyawun nashi ko kama ƙafar Abaan ɗinta baiyi ba. Dan Abaan dabanne a cikin dubun mazaje tsararsa ma balle Dafeeq da'a gabansa bai wuce ɗan tsako haihuwar jiya ba. Wajen zama ta nuna masa tana mai tattare komai zuwa gefe. Batace da shi komai ba har sakatariyarta ta ajiye masa lemo da ruwa ta fita. Taja wasu mintuna tana rubuce-rubucen ta kafin ta ɗago. Ganin bai taɓa komai ba ta ce, “A'a babban mutum ya haka? Ko kana tsoron karna zuba maka wani abu ne na sace ka”.
Murmushi yayi yana girgiza kai. “Kai haba hajiya wane sacewa kuma. Kawai dai bana jin shan komai ne dan yanzu na fito daga gida”.
“Okay kace uwargida ce ta cika maka ciki dai kawai”.
Murmushi kawai shi dai yayi baice komai ba. Itama bata sake cewarba sai tasowa da tai ta dawo kujerar kusa da shi suna facing juna. Lemon da aka ajiye masan ta ɗauka tare da ɓalle murfin takai baki, sai da tasha kusan rabi sannan ta miƙa masa. Kasa musa mata yay ya amsa yana godiya. Tai murmushi kawai da gyaɗa kanta.
“Nasan kanata makin dalilin wannan kira na ujila. Dan haka bazan so barinka a duhu ba ko lalube muje kai tsaye ga abinda yasa na kirakan, dan ni macece mara son kwana-kwana ko kwalo-kwalo. Dafeeq nasan ka sanni kasan wacece ni a companyn nan. Ka mun tambayoyi bila adadin akan ƙyautar mota da gida danai maka sati ɗaya data wuce. Hakama shekaranjiya kamin tambaya akan waya duk dai ban amsa maka ba. To ina ganin yau ya kamata na baka amsa da kuma dalilin komai. Da farko dai magana ta gaskiya *_SONKA_* nakeyi.....”
Da wani irin sauri Dafeeq ya ɗago manyan idanunsa yana kallonta. Sai kuma ya nuna kansa alamar (Ni). Kanta ta jinjina masa na tabbatarwa. Batare data bashi damar cewa wani abu ba. Ta ɗaura da faɗin, “Tabbas kai kuwa Dafeeq. Na kuma jima ina jin hakan a kanka tun randa na fara ganinka a company ɗin nan. Sai dai nata tunanin ta yanda zan tunkareka da batun gudun kada ka baɗa min ƙasa a ido. Amma dai na baka dama kaje gida kayi tunani dan ALLAH. Da gaske ina sonka kuma aure nake so muyi nanda ƙanƙanin lokaci. Dan banama son mu wuce sati biyu. Kada kuma ka damu da duk abinda za'ai na shagalin biki. Aikinka kuma zaka iya fara zuwa wannan Monday ɗin dan na tanadar maka kayan da duk zaka buƙata da kamfani ya bada umarnin ai amfani da su. Dan ALLAH kada kace a'a. Amma dai kaje kayi tunani akan maganata Please. ALLAH dai yasa bazakace na maka tsufa ba”. Ta kamo hannunsa tana murmushi tare da ɗora masa bandir na dollers. “Ga wannan ka riƙe a hannunka sai na jika. Ni yanzu zan tashi dan na gaji jikina ciwo yake mun ina buƙatar hutu.” Ta sakar masa hannu tana miƙewa fuskarta ƙawace da murmushi. Handbag nata mai azabar ƙyau kawai ta ɗauka da tarkacenta batare da ta sake cewa da shi komai ba tai ficewarta a office ɗin tana murmushi..........✍️

_😣🤌🏻Na rasa mima zance akanki Kainaat_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_Shafi na goma sha bakwai_

_________

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr

*_Assalamualaikum warahmatullah_*

*_Kin dade kina neman gurin da zaki siya kaya amintattu masu quality cikin farashi me sauqi?_*

*_ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,WANNAN GIDANNA HUGUMA CLOSET NA BUDESHI NE SABODA NA BAKU DAMAR SIYAN KAYA MASU KYAU QUALITY DA KUMA SAUQIN KUDI CIKIN AMINCI DAGA GURINA,MASU SIYAN D'AI D'AI DA MASU SARI,NATION WIDE DELIVERY cikin aminci da izinin Allah,Kayan haihuwa na jarirai har zuwa girmansu,ina muna fatan alkhairi ni da ku gaba daya_*
____________________________

........Duk yanda taso daurema zuciyarta haƙurin zuwa safiya ta gagara haka. A haukace ta fice a ɗakin zuwa upstairs da take jiyo hargagin Dafeeq. Yanda take tako steps ɗin da gudu-gudu ya sashi juyowa. Ɗauke kansa yay yana jan wani shegen tsakin takaici, sai dai me, a bazata, matuƙar bazata garesa yaji Khadijah ta wani irin fisgoshi baya har sai da yay taga-taga zai faɗi. Da ƙyar ya iya dafe bango yana bala'in zaro idanun mamakinta.
       “K! Kinada hankali kuwa?”.
    “Banda shi! Ka ɗauka banma san minene shi ba Dafeeq. Amsa kawai nake son ji daga gareka. Shin da gaske ne abinda matarka ta faɗa ko kuwa?”.
   Tsaki ya ja mai ƙarfi yana balla mata hararar takaici. Cikin matuƙar kaifin harshe ya furta, “Amma k jaka ce wlhy. Akan wannan banzar tambayar taki kika min wannan fisgar kamar wani sa'anki ko ɗanki.”
       “An fisgeka ɗin kayi abinda duk zakayi azzalumi macuci. Ka zugani nabar iyayena saboda kai amma ka zagaye kana zuwa wajen naka batare da sani na ba munafuki. Wlhy bazan taɓa yafe maka ba maci amana....”
   Tauuuu!!! Kake jin saukar mari, hannu biyu ta dafe kuncinta wata irin azaba na ratsata. Cikin rufewar ido itama ta ɗaga hannu ta sauke masa lafiyayyen marin tare da watsa masa jajayen idanunta dan Khadijah akwai zuciyar masifa. Tsabar kiɗimewa da mamakinta ya sashi sumar tsaye ya zuba mata ido kawai. Ta nunasa da yatsa jijiyoyin kanta na sake tashi ruɗu-ruɗu. “A da dai ka daka Dafeeq saboda ƙarfin soyayya. Amma a yanzu kaima kasan baka isa ba. Na rantse maka da ALLAH koda zaka kasheni ne da duka sai dai mu mutu tare a wajen ramawa azzalumi. Kai yanzu bakaji kunya ba? Ashe duk abinda kake faɗamin a iya fatar bakinka suka tsaya, na dinga wahalar ɓari a gabanka ashe kaine ke zubarmin da ciki saboda kai jahiline mara ilimi addini. Nayi dana sanin saninka a rayuwata Dafeeq. Nayi dana sanin barin iyayena waɗanda basu taɓa nuna gajiyawarsu a gareni ba tun daga haihuwa har girma saboda kai.....” wani irin kuka mai ƙona zuciya ya sarƙeta. Cigaba tai da nunasa da yatsa tana son yin magana amma hakan ya gagara.
       Wata shegiyar shaƙa Dafeeq daya gama cika tab da zagin da tai masa ya kawo mata. Kafin tai wani yinƙuri ya buga kanta da bango. Ƙarar azaba ta saki jikinta na rawa, yayinda hannunta ke kan nasa tana kiciniyar ƙwatar kanta amma hakan ya gagara, dan gaba ɗaya haushinta dana Kainaat ne ya tattara a kanta. Yanda yake jin kansan nan har shi wannan yarinyar zataima wannan zagin. Dolene ya nuna mata banbancin mace da namiji. Sai da ya tabbatar ta galabaita da irin shaƙar da yay mata sannan ya shiga jibgarta tamkar an aikosa. Bata da wani ƙarfin koda guduwa, dan tamkar ma numfashinta na barazanar barin gangar jikinta ne. Cikin abinda bai wuce mintuna biyar ba Dafeeq ya jima Khadijah ciwuka tako ina sai jini ke fita gashi ta galabaita ko motsin kirki bata iyayi balle kuka. Ga zagi yana mata na rashin mutunci ta yanda duk wanda ya kallesa yasan yana a cikin matsanancin fushi...
Chapter 29 · 0% Book details