← Book details Baya Da Kura Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 48

Sashe 16

Baya Da Kura Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Muje ko?." Jin abinda yace bata yi  musu ba ta saki hannu Mama ta fito yana binta a baya har ta koma Wakin da take ta zauna, shima bai fita ba ya duba gefe ya sauke Waukar glucometer ya sake auna sugar ta har lokacin bai yi yadda ake so ba ya kalle ta har lokacin tsayan ta yana hannun sa yace, "kin ci abinci?." Kai ya girgiza alamun A'a yace, "ina ´a  uwan ki?." Murya a shake tace, "basu zo ba."

Kai ya girgiza ya saki hannun ta ya fita. Tana nan zaune ba jimawa sai ga nurse mace da abinci ta shigo dashi tace, "Sannu, ga abinci Dr yace a kawo miki." Ajjiyewa tayi abincin a pack anyi selling Win sa da cleamfim. Kai kawai Manal ta Waga amma baza ta iya ci ba nurse Win ta fita.

Tana kwace ta sake gwada kiran Baba amma har lokacin wayar a kashe, take ta ajjiye wayar tana juya kanta har ta kawo bata gani ma sosai komai guda biyu yake ganin sa. Bebi koda ya koma office aiki kawai yake na ganin marasa lafiya dan yasan Huzaifa da Hamza suna babban asibiti sai azahar zasu je. Abubuwa sun masa yawa yana nan yana can duk da akwai taimakon nurses ga kuma sauran likitocin da suke aiki tare.

Glucometer ya koma Wakin Manal dan ya Wauka ya gwadawa wata mara lafiya nata jinin ya ganta kamar a sume take. Da hanzari ™arasa inda take yaga idom ta kulle. Hannun sa ya kai wuyan ta yaji zafi sosai yace, "Subahanallahi." Abincin ya kalla yaga da alama ba'a ci bama, da gaggawa ya fara taimaka mata saboda yanayin jikin yayi weak sosai kuma ya tabbatar sugar tane yayi ™asa da yawa.

Ganin ya saita komai sai ya fita ya kira nurse Win da ya tura ta bata abinci ta shiga office Win da sallama kafin tayi magana yace, "aikin nurse ne kula da mara lafiya ko ba aikin sa bane?." Jin hakan sai tayi shiru tasan tayi wani abun yace, "na baki abinci ki kaiwa patient sai ki ajjiye baza ki tabbatar taci ba? Wanne irin aiki ku ke yi wannan? Kin manta duk wata kulawa ta mara lafiya a kan ku take?, meyasa baku san aikin ku bane wani lokacin?."

"I'm sorry Sir!."

"Sorry for what? Sorry for your mistake?." Shiru tayi bata amsa ba daman in aka taSo shi yan faWa baya tsayawa. Shigowa office Win akayi Huzaifa ya kalli nurse Wim da take tsaye ya kalli Bebi kafin yayi magana a Bebi yace, "In baku canja ba gabaWayan ku zan ajjiye ma Wauki wasu, wannan ai shirme ne da rashin hankali. Ku shiga medication baza ku yiwa patient fbs ba kawai sai bashi magan kun san diabities patient ne?." Shiru bata ce komai ba yayi tsaki yace, "out!." Ta juya ya fita jiki a sanyaye.

Huzaifa yace, "laifin ta sake yi?." Tsaki yayi kawai baice komai ba kafin ya kalle shi yace, "har ka gama da can?."

Zama Huzaifa yayi yace, "A'a, nazo nan ne naga jikin Manal then na koma. Hankalina yana nan gabaWaya." Wani irin kallo Bebi yayi masa har sai da Huzaifa yace, "wannan kallon da kake min na meye?." Bebi ya Wage gira yace, "saboda ita ka baro wanda suke jiran ka kazo nan?."

"Yes, but I will go back now."

"What kind of relationship do you have with her?. Wacece ita Win ka?."

Huzaifa yayi murmushi yac, "nothing is going on between us, i simply adore her." Bebi ya jingina a jikin kujerar yana kallon sa yace, "™arya ka ke, akwai wani abun a ranka akan ta."

Huzaifa yayi murmushi yace, "babu komai a tsakanin mu ina mata kallo kamar ™anwata ne, mun saba da ita sosai tunda ni suke gani duk sanda suka je asibiti. Tana kula da Mama ta sosai shiyasa nake mata kallon kamar ™anwata. Baka ji itama Yaya take cemin?." Bebi yace, "hmmm! kai dai ka sani." Huzaifa yace, "na shiga Wakin sai naga itace kawai a kwance, any problems?."

Bebi yace, "jiya an samu problem akanMaman ta, a yanzu ma Maman ta tana kwance babu lafiya sosai. Itama ™anwar taka blood sugar Win ta is very hypo, shine dalilin faWan da kaji ina yiwa wannan yarinyar."

Huzaifa yace, "mostly daman ita blood sugar Win ta bai cika zama so hyper ba gaskiya, yana tafiya daidai tana ™o™ari wajan kiyayewa that's why ban Worata akan magani ba, iya diet Win is okay dan bai fi sau biyu naga sugar ta yayi high ba, shima tace min cake  taci."

"Okay" abinda Bebi ya faWa kenan dan shi bai ga amfanin bashi wannan labarin ba.

Huzaifa yace, "kuma har yanzu babu wanda yazo daga gidan su?."

"Ni zaka tambaya ko kai zan tambaya? ˜anwar ka ko ™anwata?."

"Kai ma ™anwar kace tunda kana da kamar ta." Bebi ya yi shiru baice komai ba, Huzaifa ya girgiza kai shima  baice komai ba kafin Bebi ya tashi ya fita shima ya biyo bayan sa.

Hanyar Wakin sukayi a tare suka hango Surayya a tsaye a wajan ganin Huzaifa sai ta ™araso wajan su tace, "ina kwana?." Huzaifa ya amsa dan suna yawan zuwa asibiti da ita da Manal  tace, "Dan Allah milky beauty ma bata da lafiya? Naga banga Mama ba kuma naga itama an saka mata ruwa." Huzaifa yace, "wacece Milky Beauty?."

"Manal nake nufi." Huzaifa yace, "eh, kin san tna da ciwon sugar ko?."

"Eh na sani."

"Shine yayi ™asa, in ta farka ki tabbatar kin bata abinci taci." Surayya tace, "to, Maman fa ya jikin ta?."

Huzaifa ya kalli Inda Bebi yake yaga baya wajan ya kalle ta yace, "da sau™i, kar ki damu zata dawo daidai." Kai kawai Surayya ta Waga ta shiga inda Manal take, gani tayi  ta bud'e ido sai ta koma ta fita dan ta faWawa Huzaifa amma baya wajan sai Bebi.

"Likita ta farka." Jin haka sai ya juyo ganin fuskar sa sai taji wani iri domin baiyi kama da mai mutunci ba gabaWaya. Baice komai ba ya wuce zuwa Wakin ya kalli Manal da take kwance idanun ta a buWe ya kalli ita Surayya Win yace, "abinci zaki bata taci." Zatayi magana yace, "kar ki damu ki bata ko wanne ma."

"Amma Milky bata cin abinci in bata sha tea ba, in taci bata sha ba amai take yi. Gashi ban zo da ruwan zafi ba." Ya kalle ta jin tana kiran ta da wani suna wai milky, shi baya son iyayi a rayuwar sa yafi son mace sak komai za'a yi ayi shi kai tsaye, yayi tsaki ya nuna mata inda kettle take baice komai ba kawai ya fita.

Da kallo ta bishi kafin ta Wauke ido Huzaifa ya shigo yace, "ta farka?."

"Eh ta farka, na faWawa wannan likitan wanda na ganku Wazu." Baice komai ba yaje inda Manal Win take ya kalli Surayya tace, "abinci zaki bata taci, in da dama a bata ko wanne ma."

"Na faWawa wancan likitan bata cin abinci sai ta sha tea wallahi, amma sai yayi tsaki yana nuna min can wajan kuma ban gane ne yake nufi ba. Ka fishi mutunci walalhi."

Huzaifa yayi murmushi yace, "kar ki damu yana nufin ga abin dafa ruwan zafi nan, ina da tea leave da sugar a office zan aiko a kawo miki sai ki haWa mata tasha, amma sugar din kaWan zaki saka mata ba mai yawa ba. Amfanin sa dan ya farfaWo da blood sugar Win ta da ya sauka sosai."

Surayya ta amsa ya fita yana dar1ya, wato  in baka san Bebi ba nan take zaka tabbatar da bashi da kirki da fuskar sa batayi kama da ta masu kirki ba ko kusa. Amma da ka san waye shi kun saba a nan zaka tabbatar da kirki ma a wajan sa ya samu mafaka, musamman ma ace ke mace ce, Allah ya saka masa tausayin mace da kishin ta.

Mubeena a safiyar suna cikin makarantar Yusuf mai tama sule ta ™ofar nasarawa, fitowar su daga class kenan Bily ta kalle ta tayi dariya tace, "ke dai Mubeena wani lokacin kin yi asara wallahi, an kore ki daga school amma baki daina zuwa kina zaman lectures na banza da wofi ba." Mubeena tayi dariya tace, "zaman gidan mu ne bana so ke kin sani, kuma ni ko Manal bata san an kore ni ba."

Bily tace, "wataran zata sani ai." Waya ta Wauka tana dannawa Bily tace, "dawa kike magana ne kina tafiya?."

"Baby ne, zai aiko a Wauke ni kin san yau zai canja min waya." Bily da mamaki tace, "ke  wai baza ki hankali dashi ba? Ke kika faWa min kallon da yake miki da yadda ya ri™e ki bakya jin tsoro ne wai ke?. Kuma in ya canja miki waya ki cewa Mama waye ya baki?. Ni wallahi duk ya sire min."

"Meye na tsoron? Falaqi da nasi kawai zan karanta ta zama makami akan ko wanne shege, dan ya ri™e ni wannan kin san normal ne ai ba wani abun bane, kawai na tsorata ne kasancewar hakan shine na farko amma bayan nan ai bai min komai ba ko?."

Bilkisu tace, "ki dai yi a hankali wallahi, domin somi somin hauka zubar da yawu." Mubeena tace, "kar ki yi min baki, aurena zaiyi in sha Alalh." Bily tace, "Allah yasa, zan fi kowa murna indai da gaske auren naki zaiyi. Yauwa yanzu mu je mu duba Mama daga nan sai mu wuce gida" ta faWa a lokacin da suke zuwa wajan motar Bily.

Mubeena tace, "ai ni ba bin ki zan yi ba, na faWa miki zai aiko a Wauke ni, ke kije kawai ai na baki address Win wajan." Bily da mamaki tace, "kee Mubeena kiji tsoron Allah, yanzu baza ki koma wajan Mama ba?."

Mubeena tace, "to naje nayi me dan Allah? Naje jiya ban samu ta ganni ba to me zan koma nayi?, in naje bama ba lafiya zan bata ba kuma Manal zata yi mata komai." Girgiza kai Bily tayi tace, "lallai rashin jin ki ya wuce inda nake tunani, ni na wuce" ta faWa tana shiga mota taja motar ta barta a wajan. ba jimawa aka zo da ™atuwar mota aka Wauke ta suka bar cikin makarantar.
Chapter 16 · 0% Book details