Sashe 63
Shakuwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Momma ta soma gani bibbiyu lallai Shema'u ta wuce tunanin mutum cikin kuka take gungura kekenta ta k'arasa tana kai duka ma Shema'u dake faman dariya ta ko ina.... K'arfen abin drip Shema'u ta jawo ta shiga ruza wa Momma a tsakar ka duka zogin ciwo dake addabanta... K'arshe ta k'are ta hankad'e Momma ta fad'i akan zuciyarta lokaci guda ta Saki wani k'ara...
Gaba d'aya suka nufo d'akin nan suka ga Shema'u sai dariya take ga Momma rik'eda k'irji tana salati.. Shema'u kuwa sai dariya take uwa tab'ebb'iya k'arshe fiffincike bandage d'in da aka rufa mata da jikinta ta ringa yi tana had'awa harda naman jikinta tana ihu....." Dole aka kwasheta aka canza mata asibiti....
Momma kuwa mintoci kad'an ta k'ara tace ga garinku, rai yayi halinsa.... A gidan AT akai ma Momma komai taredasu Hajiya, gaba d'aya sunsha kuka barin su Sajida, haka su Maryama da Hajiya suka ringa lallashin Su suna basu baki....
*****
Hannun Mommy ya rik'e yana kuka tana kuka sanda ya sanar da ita duk yanda sukayi da Daddy... Haidar yaci gaba da fad'in "Mummy pls ki sanar dani asalina , wanene ni....?"
Mummy ta shafi gashin kansa tana mai ci gaba da kuka take fad'in "Gaskiya ne Haidar Juwariyya itace ta haifeka, ta kasance tana yimin aikatau a lokacin dtazo da kai kana jariri domin mahaifinka ya rasu tun kana ciki ma'ana tun ba'a haifeka ba, ni kuma tuntuni inada son yara saidai Allah bai bani haihuwa ba.... A dalilin haka ta damk'a mana kai kyauta ko bayan ranta, koda nazo na sami cikin Nabila na haifeta sai na damk'a mata rainon Nabila gaba d'aya har zuwa ranar da muka wayi gari wuta ya k'one su..."
Haidar ya share hawayen sa kafin yace "Mummy basu k'one ba, Daddy bai cimma burinsa akansu ba Allah Ya tseratar dasu kuma suna rayuwa a wani waje nasan watarana Allah zai had'a mu...."
Mummy ta gyad'a kai kafin tace "Haka ne Haidar, sai yanzu nasan dalilinka na bijire wa Mahaifinka, hak'ik'a mutane sun zama mushirikai sabida neman duniya, sun fifita duniyar su sama da lahiransu wacce lahira itace rayuwa ta har abada, Fu'ad ya zalunce ni, ya cutar damu.... Bana k'aunar na kuma ganin fuskar sa har abada...." ta k'arashe cikin tsananin kuka...
*******
Gida suka zo ita da Hajiya don d'iban kaya sabida Tahir da iyalansa suna tsananin buk'atar su, nan Maryama ta wuce sashen Maama Juu ta d'auko d'an akwatin tan nan na sirri... Hannunta dafe a wuyanta tana shafe sark'anta tana mai mata addu'a cikin zuciyarta ta shiga bud'e akwatin... 'yan kunnaynta ne yawanci tun tana Baby irin a yaye lafiya d'in nan, abun har saida yasanya Maryama yin murmushi... Har zata rufe kaman ance ta karkad'e nan wata wasik'a ta fad'o....
Gaban Maryama ya yanke sanda ta d'auki wasik'ar zata soma karantawa kenan ta jiyo sallaman Ashfaq da wata Mace wanda ya sanyata fad'uwan gaba...
Hajiya ta fito daga d'aki tana fad'in wa nake ji kaman Keenafas...
Haidar na murmushi ya k'arasa shigowa Mummy ta take masa baya.. Hajiya da Haidar na ma juna barkwanci Maryama kam da Mummy tuni sun makare a kallon juna...
Idanun Mummy suka sauk'a kan sark'an dake mak'ale wuyan Maryama, take ta soma recalling komai sanda tabawa Mama Juwaira wannan sark'an tace ta ajiye mata domin a ranar Nabila wuni tayi tana wasa da sark'an...
Mummy na hawaye ta k'arasa har gaban Maryama baki na rawa take nunata tana furta "NABILA!! " Ba Maryama da tayi turus ba tana kallon Mummy gaba d'aya su Hajiya ma tsareta da idanu sukayi....
Haidar ya k'araso yana duban Mummy da kyau kafin yace "Mummy itace Nabila koh, Maryama itace Nabila koh.... Kenan matar da na zata mahaifiyarta ce wacce nake gani a mafarki itace mahaifiyata koh.... Mummy mahaifiyata ta rasu, bazan ganta ba kenan..."
Rungume Maryama Mummy tayi tana fad'in "Nabila Nabila ta, Allah yayi zan kuma ganin ki, ina Mama Juwaira...."
Hawaye Maryama keyi tana bin matar da kallo tana girgiza kai, ta kuma saurin sunkuyawa ta d'au wasik'ar da take k'ok'arin karantawa wasik'ar da Maama Juu ta fayyace mata komai a ciki, asalinta da sunan mahaifanta da kuma ita d'in ko wacece da dalilin da ya sanyasu gujewa daga gida...
Kuka Maryama take shar-shar da hawaye sanda Ashfaq ya amshi wasik'ar yana karantawa da bud'edd'iyar murya.... Gaba d'aya parlour ya kaure da kuka.....
Al'ajabi ya cika Hajiya.... Nan kuma bayan hankula sun dawo jiki aka zauna aka soma fahimtar juna, Mummy da Haidar sosai sukaji mutuwar Maama Juu, Babu kaman Haidar da bai sami Chance d'in kasancewa da ita ba a matsayinta na mahifiyar sa.. Allah Ya k'addari hakan saidai su bita da addu'a...Allah sarki Maama Juu ta cika mai halin k'warai Allah ya kai haske makwancinta..
Mummy tamkar ta maida Maryama cikinta haka take ji, gaba d'aya suka d'unguma sukayi gidan AT... Mamaki da Al'ajabi ya cika su gaba d'aya, kodashike ba'a mamaki da ikon Allah lokaci guda ya warware komai..
Mummy gaba d'aya rasa bakin godiya tayima Hajiya da Ahmad Tahir... Babban abinda yafi mata dad'i shine auren Tahir da Nabilar ta, lallai sun cika mutane masu karamci...
Maryama dai bata wani sake da Mummy ba tana nan mak'ale da Hajiyarta, saida Hajiya ta tilasta mata ta tafi wajen mahaifiyarta su kwana tare suji d'umin juna kafin Maryama ta mik'e ta tafi wajen mahaifiyarta... Hira Mummy ta ringa janta dashi na labarin rayuwarta kafin daga bisani tace maza ta tashi ta tafi wajen mijinta yafi kowa buk'atan ta a hali yanzu tunda bashida lafiya...
Maryama ta d'an turo baki had'i da zaro idanu tace "Mummy fah zai iya kwan, nidai ki barni naji d'uminki..."
Mummy tayi murmushi ta shafi kumatunta kafin tace "Baby babu kalan d'umina wanda bakiji a jikin Hajiya ba, yanzu d'umin mijinki yafi d'umina mahimmanci a gareki kinji koh..."
Cikeda kunya Maryama ta sadda kanta k'asa.. Har k'ofa Mummy tayi mata rakiya had'ida saka mata albarka...
A stirs ta had'u da Sajida zata sauk'o k'asa... Gaban Maryama ya yanke ya fad'i don gani take Sajida ta fahimci d'akin mahaifinta zata tafi...
Murmushi Sajida ta sakar mata kafin ta iso yanda take, a kunnenta ta rad'a mata... "Aunty Sis kin k'yale min Daddy na shi kad'ai bayan kinsan bashida lafiya..."
Dariya Maryama tayi ta kai mata dukan wasa tace "Zaki sani ne..."
Dariya Sajida ma tayi kafin tace "Eh mana ai gaskiya na fad'i koh, ga wannan yayan naki Keenafas d'in Hajiya ina cikin bacci na ya dameni da waya wai sai na had'a masa shayi... Likitoci akwai kad'ifiri wai basu cin solid food da dare..."
Ganin Maryama na watso mata kallo yasata k'unshe baki tace "Oh I'm sorry ashe ke matar likita ne..." ta k'arashe tana wucewa da gudu...
Murmushi kawai Maryama tayi kafin tayi wucewarta d'akin masoyinta....
Yana tsaye gaban full length mirror yana k'ok'arin cire rigarsa da hannu guda sabida ciwon sa, kaman daga sama sai jiyo hannunta yayi tana taimaka masa... Annuri ya cika zuciyar sa, gently ta k'arasa cire masa rigar...
Juyowa yayi ya d'an kamo kunkuminta da hannu maras ciwon kafin yace "Allah Ya maki albarka Baby.."
Bata iya amsa sa ba sai sadda kai k'asa da tayi domin kuwa gaba d'aya nauyinsa take ji...
AT ya murmusa kafin yayi masu masauk'i saman chaise lounge, tana zaune saman laps d'insa ya d'ago fuskar sa yana dubanta kafin yace "Why the face Baby, ko baki so zuwa wajena bane, I thought da Hajiyarki zaki kwana har na cire rai...."
Turo baki ta kuma yi kafin tace dashi a shagwab'e "Ba Mummy bace tace sai na zo..."
AT ya murmusa had'i da d'an jan hancinta kafin yace "Gaskiya Mummy ta kyauta min, ai Mummy ta fiku gaskiya keda Hajiya, ku kun faye son kanku yanzu nima kunga na sami mai sona tunda tana tausayi na..." Maryama ta kuma turo baki..
Rungumeta yayi cikin jikinsa had'i da lumshe idanu... Nan yaji hawayenta na sauk'a a kafad'ansa.... SSaurin d'agowa yayi yana tambayarta meke faruwa.. "Ko kina son ki tafi wajen Hajiya ne..."
Girgiza kai tayi kafin tace "Uncle na kasa aminta mahaifina mutumin banza ne, shin dama hakan ka iya kasancewa ga mutum, meyasa mahaifina why him... Rayuwa ta mana sauk'i, mun zama family d'in da muke mafarkin zama na samu Mahaifiyata, na auri mijin da nake so but.... I'm still hurting deep inside....."
AT da jikinsa yayi sanyi saurin rungumeta yayi kafin yace "Ki daina irin wannan tunanin Baby, Allah yakan jarabci bayinsa tako ina, babu laifinki ko na mahaifiyarki don mahaifinki ya kasance haka, kar ki manta Allah yana cire rayayye a cikin matacce sannan yana cire matacce a cikin rayayye wannan fad'insa ne, kasancewar mahaifinki haka doesn't mean you can't be accepted by other people, because we all are imperfect no one's perfect sannan babu wanda zai sami irin rayuwar da yake so perfectly dole ta wani wajen ka sami nak'asu.... Kar ki manta Annabi Nuhu alaihissalam Annabi ne kuma manzo sannan d'ansa da matar sa sun kasance 'yan wuta... Asiya matar fir'auna wanda yafi kowa kafirci a duniya ta kasance cikin mataye masu daraja kuma 'yan aljannah dukda cewa daga iyalan gidan Fir'auna take.. So ki daina damuwa Baby wannan shike tabbatar wa mu 'yan Adam ne bazamu sami komai yanda muke so ya kasance ba kinji koh..."
Murmushi tayi had'i da gyad'a masa kai kana ta kwanta cikin jikinsa a hankali ta furta "Ina sonka Uncle..." Ido a lumshe shima ya furta "Ina sonki nima Baby..."
"Keenafas ka k'yaleni naje nayi bacci tunda na kawo maka shayin pls..." ta k'arashe tana had'e hannayen ta waje guda..
Murmushi Haidar yayi kafin yace "Saifah kinmin labarin saurayinki Buzu kafin na k'yaleki..."
Harara ta galla masa kafin tace "Kaga ka daina tam, ni dai bana so...."
Haidar ya k'unshe dariyar sa kafin yace "Toh saurayin ki Keenafas fah...?"
Dariya itama tayi kafin tace "Kai gaskiya Hajiya ta iya saka suna sosai, kuma fah kayi kama da Kidnappers d'in...."
Dariya ya kumayi kafin yace "Gashi kuma zanyi keenafas d'inki ba...."
Kaman daga sama sai ganin Hajiya sukayi ta lek'o tana goga aswakinta kana tace "Kafin kayi keenafas d'inta ka tabbata ka biya sadaki ehe....."
Daga Haidar har Sajida dariya suka ringa yi harda sunkuyawa... Hajiya kuwa ko a jikinta ta fad'i ta koma d'aki abinta.....
ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!
*A nan na kawo k'arshen wannan littafi nawa mai taken SHAK'UWA CE, kurakuren da nayi cikinsa ina rok'on Allah Ya gafarta mani, fad'akawan dake cikinsa Allah Ya amfane mu dashi baki d'aya.*
*Dukkan yabo da godiya sun tabbata GA Ubangijin talikai wanda ya aramin rayuwa da lafiya har na kammala wannan rubutu nawa...*
*K'ungiyata ta KAINUWA na gode maku k'warai bisa goyon bayanku da jajircewan ku a gareni har wannan sak'o da nake son isawar ya kammala, Allah Ya saka maku da alkhairi ya k'ara had'e kanmu baki d'aya... Ameen!"*
*''Yar uwa aminiya k'awa a gareni RALIYA GARBA aka RALLY GARBA, banida bakin godiya a gareki saidai naci gaba da maki addu'an alkhairi.... Allah Ya rabamu da sharrin mutum ko aljan... Wannan littafi nawa mai taken SHAK'UWA CE kacaukam d'insa sadaukarwa ne a gareki My Sisi... Tabbas SHAK'UWA CE mai k'arfi abtsakanin mu, Allah Ya bar k'auna... Amen...!*
*Masoya na a duk yanda kuke a fad'in duniya nima ina sonku ina k'aunar ku... Nasan cewa SHAK'UWA CE mai tsanani a tsakanin ku da wannan labari zakuyi kewan shi kaman yanda shima zaiyi kewarku.... Alkhairin Allah Ya kai maku a duk yanda kuke...*
_*SAMEENA ALEEYOU aka QUEEN SAMY ke maku fata na alkhairi 🤝*_
Gaba d'aya suka nufo d'akin nan suka ga Shema'u sai dariya take ga Momma rik'eda k'irji tana salati.. Shema'u kuwa sai dariya take uwa tab'ebb'iya k'arshe fiffincike bandage d'in da aka rufa mata da jikinta ta ringa yi tana had'awa harda naman jikinta tana ihu....." Dole aka kwasheta aka canza mata asibiti....
Momma kuwa mintoci kad'an ta k'ara tace ga garinku, rai yayi halinsa.... A gidan AT akai ma Momma komai taredasu Hajiya, gaba d'aya sunsha kuka barin su Sajida, haka su Maryama da Hajiya suka ringa lallashin Su suna basu baki....
*****
Hannun Mommy ya rik'e yana kuka tana kuka sanda ya sanar da ita duk yanda sukayi da Daddy... Haidar yaci gaba da fad'in "Mummy pls ki sanar dani asalina , wanene ni....?"
Mummy ta shafi gashin kansa tana mai ci gaba da kuka take fad'in "Gaskiya ne Haidar Juwariyya itace ta haifeka, ta kasance tana yimin aikatau a lokacin dtazo da kai kana jariri domin mahaifinka ya rasu tun kana ciki ma'ana tun ba'a haifeka ba, ni kuma tuntuni inada son yara saidai Allah bai bani haihuwa ba.... A dalilin haka ta damk'a mana kai kyauta ko bayan ranta, koda nazo na sami cikin Nabila na haifeta sai na damk'a mata rainon Nabila gaba d'aya har zuwa ranar da muka wayi gari wuta ya k'one su..."
Haidar ya share hawayen sa kafin yace "Mummy basu k'one ba, Daddy bai cimma burinsa akansu ba Allah Ya tseratar dasu kuma suna rayuwa a wani waje nasan watarana Allah zai had'a mu...."
Mummy ta gyad'a kai kafin tace "Haka ne Haidar, sai yanzu nasan dalilinka na bijire wa Mahaifinka, hak'ik'a mutane sun zama mushirikai sabida neman duniya, sun fifita duniyar su sama da lahiransu wacce lahira itace rayuwa ta har abada, Fu'ad ya zalunce ni, ya cutar damu.... Bana k'aunar na kuma ganin fuskar sa har abada...." ta k'arashe cikin tsananin kuka...
*******
Gida suka zo ita da Hajiya don d'iban kaya sabida Tahir da iyalansa suna tsananin buk'atar su, nan Maryama ta wuce sashen Maama Juu ta d'auko d'an akwatin tan nan na sirri... Hannunta dafe a wuyanta tana shafe sark'anta tana mai mata addu'a cikin zuciyarta ta shiga bud'e akwatin... 'yan kunnaynta ne yawanci tun tana Baby irin a yaye lafiya d'in nan, abun har saida yasanya Maryama yin murmushi... Har zata rufe kaman ance ta karkad'e nan wata wasik'a ta fad'o....
Gaban Maryama ya yanke sanda ta d'auki wasik'ar zata soma karantawa kenan ta jiyo sallaman Ashfaq da wata Mace wanda ya sanyata fad'uwan gaba...
Hajiya ta fito daga d'aki tana fad'in wa nake ji kaman Keenafas...
Haidar na murmushi ya k'arasa shigowa Mummy ta take masa baya.. Hajiya da Haidar na ma juna barkwanci Maryama kam da Mummy tuni sun makare a kallon juna...
Idanun Mummy suka sauk'a kan sark'an dake mak'ale wuyan Maryama, take ta soma recalling komai sanda tabawa Mama Juwaira wannan sark'an tace ta ajiye mata domin a ranar Nabila wuni tayi tana wasa da sark'an...
Mummy na hawaye ta k'arasa har gaban Maryama baki na rawa take nunata tana furta "NABILA!! " Ba Maryama da tayi turus ba tana kallon Mummy gaba d'aya su Hajiya ma tsareta da idanu sukayi....
Haidar ya k'araso yana duban Mummy da kyau kafin yace "Mummy itace Nabila koh, Maryama itace Nabila koh.... Kenan matar da na zata mahaifiyarta ce wacce nake gani a mafarki itace mahaifiyata koh.... Mummy mahaifiyata ta rasu, bazan ganta ba kenan..."
Rungume Maryama Mummy tayi tana fad'in "Nabila Nabila ta, Allah yayi zan kuma ganin ki, ina Mama Juwaira...."
Hawaye Maryama keyi tana bin matar da kallo tana girgiza kai, ta kuma saurin sunkuyawa ta d'au wasik'ar da take k'ok'arin karantawa wasik'ar da Maama Juu ta fayyace mata komai a ciki, asalinta da sunan mahaifanta da kuma ita d'in ko wacece da dalilin da ya sanyasu gujewa daga gida...
Kuka Maryama take shar-shar da hawaye sanda Ashfaq ya amshi wasik'ar yana karantawa da bud'edd'iyar murya.... Gaba d'aya parlour ya kaure da kuka.....
Al'ajabi ya cika Hajiya.... Nan kuma bayan hankula sun dawo jiki aka zauna aka soma fahimtar juna, Mummy da Haidar sosai sukaji mutuwar Maama Juu, Babu kaman Haidar da bai sami Chance d'in kasancewa da ita ba a matsayinta na mahifiyar sa.. Allah Ya k'addari hakan saidai su bita da addu'a...Allah sarki Maama Juu ta cika mai halin k'warai Allah ya kai haske makwancinta..
Mummy tamkar ta maida Maryama cikinta haka take ji, gaba d'aya suka d'unguma sukayi gidan AT... Mamaki da Al'ajabi ya cika su gaba d'aya, kodashike ba'a mamaki da ikon Allah lokaci guda ya warware komai..
Mummy gaba d'aya rasa bakin godiya tayima Hajiya da Ahmad Tahir... Babban abinda yafi mata dad'i shine auren Tahir da Nabilar ta, lallai sun cika mutane masu karamci...
Maryama dai bata wani sake da Mummy ba tana nan mak'ale da Hajiyarta, saida Hajiya ta tilasta mata ta tafi wajen mahaifiyarta su kwana tare suji d'umin juna kafin Maryama ta mik'e ta tafi wajen mahaifiyarta... Hira Mummy ta ringa janta dashi na labarin rayuwarta kafin daga bisani tace maza ta tashi ta tafi wajen mijinta yafi kowa buk'atan ta a hali yanzu tunda bashida lafiya...
Maryama ta d'an turo baki had'i da zaro idanu tace "Mummy fah zai iya kwan, nidai ki barni naji d'uminki..."
Mummy tayi murmushi ta shafi kumatunta kafin tace "Baby babu kalan d'umina wanda bakiji a jikin Hajiya ba, yanzu d'umin mijinki yafi d'umina mahimmanci a gareki kinji koh..."
Cikeda kunya Maryama ta sadda kanta k'asa.. Har k'ofa Mummy tayi mata rakiya had'ida saka mata albarka...
A stirs ta had'u da Sajida zata sauk'o k'asa... Gaban Maryama ya yanke ya fad'i don gani take Sajida ta fahimci d'akin mahaifinta zata tafi...
Murmushi Sajida ta sakar mata kafin ta iso yanda take, a kunnenta ta rad'a mata... "Aunty Sis kin k'yale min Daddy na shi kad'ai bayan kinsan bashida lafiya..."
Dariya Maryama tayi ta kai mata dukan wasa tace "Zaki sani ne..."
Dariya Sajida ma tayi kafin tace "Eh mana ai gaskiya na fad'i koh, ga wannan yayan naki Keenafas d'in Hajiya ina cikin bacci na ya dameni da waya wai sai na had'a masa shayi... Likitoci akwai kad'ifiri wai basu cin solid food da dare..."
Ganin Maryama na watso mata kallo yasata k'unshe baki tace "Oh I'm sorry ashe ke matar likita ne..." ta k'arashe tana wucewa da gudu...
Murmushi kawai Maryama tayi kafin tayi wucewarta d'akin masoyinta....
Yana tsaye gaban full length mirror yana k'ok'arin cire rigarsa da hannu guda sabida ciwon sa, kaman daga sama sai jiyo hannunta yayi tana taimaka masa... Annuri ya cika zuciyar sa, gently ta k'arasa cire masa rigar...
Juyowa yayi ya d'an kamo kunkuminta da hannu maras ciwon kafin yace "Allah Ya maki albarka Baby.."
Bata iya amsa sa ba sai sadda kai k'asa da tayi domin kuwa gaba d'aya nauyinsa take ji...
AT ya murmusa kafin yayi masu masauk'i saman chaise lounge, tana zaune saman laps d'insa ya d'ago fuskar sa yana dubanta kafin yace "Why the face Baby, ko baki so zuwa wajena bane, I thought da Hajiyarki zaki kwana har na cire rai...."
Turo baki ta kuma yi kafin tace dashi a shagwab'e "Ba Mummy bace tace sai na zo..."
AT ya murmusa had'i da d'an jan hancinta kafin yace "Gaskiya Mummy ta kyauta min, ai Mummy ta fiku gaskiya keda Hajiya, ku kun faye son kanku yanzu nima kunga na sami mai sona tunda tana tausayi na..." Maryama ta kuma turo baki..
Rungumeta yayi cikin jikinsa had'i da lumshe idanu... Nan yaji hawayenta na sauk'a a kafad'ansa.... SSaurin d'agowa yayi yana tambayarta meke faruwa.. "Ko kina son ki tafi wajen Hajiya ne..."
Girgiza kai tayi kafin tace "Uncle na kasa aminta mahaifina mutumin banza ne, shin dama hakan ka iya kasancewa ga mutum, meyasa mahaifina why him... Rayuwa ta mana sauk'i, mun zama family d'in da muke mafarkin zama na samu Mahaifiyata, na auri mijin da nake so but.... I'm still hurting deep inside....."
AT da jikinsa yayi sanyi saurin rungumeta yayi kafin yace "Ki daina irin wannan tunanin Baby, Allah yakan jarabci bayinsa tako ina, babu laifinki ko na mahaifiyarki don mahaifinki ya kasance haka, kar ki manta Allah yana cire rayayye a cikin matacce sannan yana cire matacce a cikin rayayye wannan fad'insa ne, kasancewar mahaifinki haka doesn't mean you can't be accepted by other people, because we all are imperfect no one's perfect sannan babu wanda zai sami irin rayuwar da yake so perfectly dole ta wani wajen ka sami nak'asu.... Kar ki manta Annabi Nuhu alaihissalam Annabi ne kuma manzo sannan d'ansa da matar sa sun kasance 'yan wuta... Asiya matar fir'auna wanda yafi kowa kafirci a duniya ta kasance cikin mataye masu daraja kuma 'yan aljannah dukda cewa daga iyalan gidan Fir'auna take.. So ki daina damuwa Baby wannan shike tabbatar wa mu 'yan Adam ne bazamu sami komai yanda muke so ya kasance ba kinji koh..."
Murmushi tayi had'i da gyad'a masa kai kana ta kwanta cikin jikinsa a hankali ta furta "Ina sonka Uncle..." Ido a lumshe shima ya furta "Ina sonki nima Baby..."
"Keenafas ka k'yaleni naje nayi bacci tunda na kawo maka shayin pls..." ta k'arashe tana had'e hannayen ta waje guda..
Murmushi Haidar yayi kafin yace "Saifah kinmin labarin saurayinki Buzu kafin na k'yaleki..."
Harara ta galla masa kafin tace "Kaga ka daina tam, ni dai bana so...."
Haidar ya k'unshe dariyar sa kafin yace "Toh saurayin ki Keenafas fah...?"
Dariya itama tayi kafin tace "Kai gaskiya Hajiya ta iya saka suna sosai, kuma fah kayi kama da Kidnappers d'in...."
Dariya ya kumayi kafin yace "Gashi kuma zanyi keenafas d'inki ba...."
Kaman daga sama sai ganin Hajiya sukayi ta lek'o tana goga aswakinta kana tace "Kafin kayi keenafas d'inta ka tabbata ka biya sadaki ehe....."
Daga Haidar har Sajida dariya suka ringa yi harda sunkuyawa... Hajiya kuwa ko a jikinta ta fad'i ta koma d'aki abinta.....
ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!!
*A nan na kawo k'arshen wannan littafi nawa mai taken SHAK'UWA CE, kurakuren da nayi cikinsa ina rok'on Allah Ya gafarta mani, fad'akawan dake cikinsa Allah Ya amfane mu dashi baki d'aya.*
*Dukkan yabo da godiya sun tabbata GA Ubangijin talikai wanda ya aramin rayuwa da lafiya har na kammala wannan rubutu nawa...*
*K'ungiyata ta KAINUWA na gode maku k'warai bisa goyon bayanku da jajircewan ku a gareni har wannan sak'o da nake son isawar ya kammala, Allah Ya saka maku da alkhairi ya k'ara had'e kanmu baki d'aya... Ameen!"*
*''Yar uwa aminiya k'awa a gareni RALIYA GARBA aka RALLY GARBA, banida bakin godiya a gareki saidai naci gaba da maki addu'an alkhairi.... Allah Ya rabamu da sharrin mutum ko aljan... Wannan littafi nawa mai taken SHAK'UWA CE kacaukam d'insa sadaukarwa ne a gareki My Sisi... Tabbas SHAK'UWA CE mai k'arfi abtsakanin mu, Allah Ya bar k'auna... Amen...!*
*Masoya na a duk yanda kuke a fad'in duniya nima ina sonku ina k'aunar ku... Nasan cewa SHAK'UWA CE mai tsanani a tsakanin ku da wannan labari zakuyi kewan shi kaman yanda shima zaiyi kewarku.... Alkhairin Allah Ya kai maku a duk yanda kuke...*
_*SAMEENA ALEEYOU aka QUEEN SAMY ke maku fata na alkhairi 🤝*_