Sashe 16
Shakuwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Shema'u tayi kafin tace "Sajee ki daina min godiyar nan pls, me anfani na idan yaran tilon 'yar uwata basuji dad'i ba. Oya kar ma ki damu, Haris kaman yaso ki an gama." ta k'arashe maganar zuciyarta fari k'al, inama duka mutane can easily be manipulated kaman Sajida.
***********
A 'yan kwanakin nan sam Sajida ta canza wa Maryama, sunadai gaisawa Hi hi, amma sam bata bari suyi dogon zance, Maryama ma bata d'ago mata zancen ba sai ta share kurum, tunda yanzu jarabawar su dake gaban su yafi komai mahimmanci a garesu.
A haka kwanaki suka shud'e. Yau Shema'u na zaune a d'aki sai faman fente-fenten fuska take, don har wani alla alla take AT ya dawo yayi araba da ita. Kaman daga sama ta jiyo wayarta na ringing, k'arsawa tayi ta d'aga tana mai washe baki da kashe murya don kuwa ba kowa bane illa Bahon ta, wato Alh Aminu.
"Hello giwan mata." ya fad'i daga d'aya b'angaren yana washe baki.
Saida ta wani murmusa kafin tace "My Alhaji yaya akayi ne, naji shiru fah banji alert ba har yanzu."
Dariyar jin dad'i yayi kafin yace "Cash d'inki da ride d'inki sun sami isowa yau d'in nan."
"Wow, da gaske kake my Alhaji?" ta fad'i tana mai mik'ewa tsaye.
"K'warai kuwa Tauraruwa ta, kinsan komai idan naki ne jikina har rawa yake."
Shema'u tayi murmushin jin dad'i kafin tace "My Alhaji kenan, sam baka gajjiya da d'awainiya, toh yanzu waye ka aiko don nasan yanda zanyi na amshi aikan."
Amsar da ya bata ne ya sanyata d'aure fuska tamau, cike da b'acin rai ta soma fad'in "Haba Alhaji, haba, yaya zaka min haka, me zai kawoka Kano, nida nace maka zanje har gida na sameka, kasan Momma bata san da kai ba har yanzu, kuma kaga gidan wani nake, bana so su soma zargina."
Alh Aminu ya tattare naman goshin sa had'i da fuzar da iska kafin yace "Shema'u a gaskiya I'm tired of your excuses, why are you hiding me from your family, meyasa baki so 'yan uwanki su San dani, Shem'au sonki nake da aure ba zallan daduro ba ke kinsan da hakan."
Sam bataso ta sami sab'ani da Alh Aminu a yanzu, don kuwa yanzu ne take buk'atansa more than ever, she really needs to put up with his stupidities ... D'an gajeren murmushi tayi kafin tace "My Alhaji kenan, sam baka fahimce ni bane, amma yanzu text me your location I'll be on my way."
Cike da jin dad'i yana baje saman gadon hotel yana shafa tunbinsa yake k'yalk'yale dariya kafin yace "Shiyasa nake k'ara sonki, yanzu zan turo maki right away." Daga haka sallama sukayi.
Wata uwar tsaki Shema'u taja cikeda takaici, yanzu shikenan wannan kwalliyan a iska tayishi her AT bazai gani ba. K'arasawa tayi jikin bagrag ta d'au jaka ta zari mayafinta, saida ta lek'a parlorn AT tana mai tunanin watarana da yardan Allah suna cikin nan suna shan soyayyar su, wani murmushi tayi kafin ta nufo downstairs fuskar nan tasha heavy makeup.
A farfajiyan gidan ta hangi Momma na zaune saman faran kujera, k'arasawa tayi tana dubanta daga yanda take tsaye kafin tace "Momma ni zan fita."
Baki sake Momma tace "Ke wannan kwalliya da kikayi haka ai gwara ki tsaya Tahir ya gani tunda ya kusa dawowa, ina mai tabbatar maki har kama yau kikayi da marigayiya Aisha ta."
K'atutun bak'in ciki ne ya tokare mak'oshin Shema'u jin Momma na had'ata da Aysha, wato dukda ta mutu baza'a daina kawo tunaninta first ba, harta kamanni ma wato ba'ason nata sai na Aysha, miji ma sai sauran na Aysha ake neman lik'a mata, kodayake ai ta riga Aysha fara son AT don haka dama AT nata ne since from the very beginning. Kai ta tsani Aysha wllhi, dolema ta d'aid'aita rayuwar Sajida kota halin k'ak'a ne.
"Momma kenan kinsan nace maki zanje gidan k'awata a Sabon gari, tun d'azu taketa min waya.... Ba jimawa zanyi ba insha Allah." Ta k'arashe maganar tana ciro waya a jaka tana duba sak'on Alh Aminu da ya shigo mata.
"Toh ai shikenan, kardai kiyi dare kuma ki kula da kwalta."
D'an murmushi Shema'u tayi kafin tace "Momma kenan wani sa'in idan kinyi magana kina bani dariya, yanzu ni ce sai an fad'a min na kula da kwalta, kodayake tun bayan accident d'in nan sai kin fad'i haka kullum idan zamu fita, ki kwantar da hankalin ki Mommata yau kam ma da taxi zan fita don motata babu enough fuel kuma yanda zanje kinga da d'an nisa."
Momma ta jinjina kai kafin tace "Shikenan Allah Ya tsare,." ko amsa mata Shema'u batayi ba taci gaba da tafiyarta.
Momma tayi jigum tana kallon Shema'u, a kullum idan ta tuna bata sanar da Shema'u asalin wanene mahaifin ta ba, hankalin ta yana matuk'ar tashi, gani take kaman duk randa Shema'u tasan asalinta zata tsaneta na har Abada. Allah sarki Alh Mukhtar marigayi mijinta mai rasuwa kuma mahaifin Ayshan ta, ya rik'i Shema'u amana, har ya koma ga ubangiji Shema'u batasan bashine mahaifinta ba,. Momma tasa bayan hannunta ta share k'wallan da suka zubo mata tunowa datayi yau babu Mukhtar babu Aysha, duk sun tafi sun barta. Jikinta yayi sanyi sosai da wannan tunani ta mik'e ta nufi cikin gida.
Sauri-sauri ta soma tafiya da sawu a layin, alla-alla take ta sami abun hawa ta d'ale amma shiru bata samu ba, kaman daga sama ta hangi motar AT na shigowa layin, k'irjinta ya yanke ya fad'i. Gaba d'aya daburcewa tayi don bataso suka had'u da AT ba, tasan zai iya cewa ta shigo ya ajiyeta.
Parking ya d'anyi sanda ya hangeta, cike da murmushin k'issa ta k'araso yanda yake, d'an rage glass yayi suka gaisa kafin ya tambayeta ina zataje.
A d'an daburce ta sanar dashi gidan k'awarta zataje kaman yanda ta sanar da Momma,. AT ya d'an murmusa wanda yake kashe Shema'u kafin yace "Toh banda abinki Shema'u me anfanin motar ki, kije a ciki mana."
D'an murmushin yak'e tayi kafin tace "Dr kenan, ai motar tawa tana buk'atan ziyartan gareji ne ma, amma babu matsala zan sami ko taxi ko adaidaita ne na shiga."
AT ya d'an dubi agogon jikin motar sa kafin yace "Toh shigo na ajiyeki, ko kuma ki karb'i tawa motar kije da ita."
Shema'u ta k'walalo ido waje, dad'i kaman ya karta, wai yau ita AT kema magana haka har yana cewa zai kaita anguwa. "Em... Em wllhi ka barshi kawai Dr I can manage, haba ka dawo daga office ga gajjiya, kana buk'atan hutu pls ka shiga ka huta."
Murmushi ya kuma yi a karo na biyu kafin yace "Karki damu ni nace zan kaiki ai, this is the least I can do after all the sacrifices you've done for my family. Pls ki shiga na ajiyeki."
Murmushi ta d'anyi zuciyarta fari k'al lallai AT yana appreciating abubuwan da takeyi wa yaransa, tabbas sune her key to his house.
Suna tafe babu mai cewa komai, sai binsa da mayen kallo take da wutsiyar idanu, wayyo Allanta gaskiya ta matsu tana tsananin buk'atar AT a shimfid'arta, sosai take kwad'ayin shi... Muryarsa ne ya katse mata tunanin ta.
"Na gode da devoting lokutanki masu anfani da kikayi ma iyalai na sannan ina fatan hakan won't affect your job." Idanunsa naga kwalta yayi maganar.
Rausayar da idanu tayi kafin tace "Haba Dr, saikace wani abin nayi, yaran nan fah are my obligation tunda yaran 'yar uwatace, ko a shari'a ne sunada hakki akaina a matsayina na yayar mahaifiyar su, Dr bazan b'oye maka ba wllhi ina son yaranka so na hak'ik'a, soyayyar da nakejin sam bana son rabuwa dasu."
Saida ya d'an kaikaito da fuska ya dubeta kafin ya maida idanunsa ga kwalta.
A tak'aice ya furta "Na gode da soyayyar da kike masu." tundaga haka bai kuma cewa komai ba har suka isar unguwar da suka nufa.
Gaba d'aya ta daburce ta soma tunanin ina zata sauk'a, wata dabara ta fad'o mata, Shagon gyaran gashi dake a bakin titi ta hanga, tayi saurin ciro wayarta tamkar mai karanta sak'o kafin ta d'anyi murmushi ta furta "Kai Salma dai akwai shirirta, waifa kaga tun d'azu nake jira ta turo min location na gidan nasu amma shiru. Sai yanzu take ce min na jirata a wancan saloon d'in."
Baice komai ba don kuwa sam bashida hayaniya, karya kan motar kurum yayi ya k'arasa bakin shagon gyaran gashin yayi parking.
Sai wani kwarkwasa take sanda take masa godiya had'i da sallama, shikam sam hankalinsa ma baya gareta, a tak'aice ya amsata kafin ya tada motar sa ya bar wajen.
*************
Aaa'ah, mamaki ya cika Ashfaq ganin tulin fake d'in magungunan da akayi ordering, kai anmayi banning wasu magungunan an hana amfani dasu. Cikin sauri ya shiga neman layin AT.
AT yana gama parking motar sa wayar Ashfaq ya shigo masa, nan take Ashfaq ya fad'a masa halin da ake ciki.
"What!" AT ya furta cikeda tashin hankali kafin yace "Ina Hisham ya bari hakan ta kasance, shine alhakin sayan magunguna suke wuyarsa..... Okay, ka gane zamu gudanar da bincike, zan kira Hisham d'in, kar ka bari a sauk'e kayan ko k'wayar magani ce.
Sosai hankalin AT ya tashi wannan ka iya jefa asibitinsa cikin had'ari mai girma, amma yasan Hisham bazaiyi haka ba, duk yanda akayi hakan ta faru ne bada saninsa ba. Neman layin Hisham ya shiga yi.
"Hisham ya akayi hakan ta faru, kasan irin had'arin da hakan ka iya jefa hospital d'inmu?" In a furious tune yayi maganar.
Gaban Hisham ya yanke ya fad'i amma yayi saurin saita kansa kafin yace "Tahir kasan dai da sanina bazanyi hakan ba, amma kar ka damu zanyi magana dasu distributors d'in, in short zamu daina sayan magunguna a company d'insu... Oh my god I'm really sorry Friend, nasan hakan zai janyo fad'uwa sosai."
Gajeren tsaki AT ya d'anyi kafin yace "Ba kud'in da za'a rasa bane damuwar, what matters shine b'ata sunan asibitin da hakan ka iya haifarwa da kuma amfani da magungunan... Thank goodness Ashfaq was there sanda suka delivering, kasan meye zai faru mu had'u a asibitin yanzu." Daga haka katse wayar sa yayi.
***********
A 'yan kwanakin nan sam Sajida ta canza wa Maryama, sunadai gaisawa Hi hi, amma sam bata bari suyi dogon zance, Maryama ma bata d'ago mata zancen ba sai ta share kurum, tunda yanzu jarabawar su dake gaban su yafi komai mahimmanci a garesu.
A haka kwanaki suka shud'e. Yau Shema'u na zaune a d'aki sai faman fente-fenten fuska take, don har wani alla alla take AT ya dawo yayi araba da ita. Kaman daga sama ta jiyo wayarta na ringing, k'arsawa tayi ta d'aga tana mai washe baki da kashe murya don kuwa ba kowa bane illa Bahon ta, wato Alh Aminu.
"Hello giwan mata." ya fad'i daga d'aya b'angaren yana washe baki.
Saida ta wani murmusa kafin tace "My Alhaji yaya akayi ne, naji shiru fah banji alert ba har yanzu."
Dariyar jin dad'i yayi kafin yace "Cash d'inki da ride d'inki sun sami isowa yau d'in nan."
"Wow, da gaske kake my Alhaji?" ta fad'i tana mai mik'ewa tsaye.
"K'warai kuwa Tauraruwa ta, kinsan komai idan naki ne jikina har rawa yake."
Shema'u tayi murmushin jin dad'i kafin tace "My Alhaji kenan, sam baka gajjiya da d'awainiya, toh yanzu waye ka aiko don nasan yanda zanyi na amshi aikan."
Amsar da ya bata ne ya sanyata d'aure fuska tamau, cike da b'acin rai ta soma fad'in "Haba Alhaji, haba, yaya zaka min haka, me zai kawoka Kano, nida nace maka zanje har gida na sameka, kasan Momma bata san da kai ba har yanzu, kuma kaga gidan wani nake, bana so su soma zargina."
Alh Aminu ya tattare naman goshin sa had'i da fuzar da iska kafin yace "Shema'u a gaskiya I'm tired of your excuses, why are you hiding me from your family, meyasa baki so 'yan uwanki su San dani, Shem'au sonki nake da aure ba zallan daduro ba ke kinsan da hakan."
Sam bataso ta sami sab'ani da Alh Aminu a yanzu, don kuwa yanzu ne take buk'atansa more than ever, she really needs to put up with his stupidities ... D'an gajeren murmushi tayi kafin tace "My Alhaji kenan, sam baka fahimce ni bane, amma yanzu text me your location I'll be on my way."
Cike da jin dad'i yana baje saman gadon hotel yana shafa tunbinsa yake k'yalk'yale dariya kafin yace "Shiyasa nake k'ara sonki, yanzu zan turo maki right away." Daga haka sallama sukayi.
Wata uwar tsaki Shema'u taja cikeda takaici, yanzu shikenan wannan kwalliyan a iska tayishi her AT bazai gani ba. K'arasawa tayi jikin bagrag ta d'au jaka ta zari mayafinta, saida ta lek'a parlorn AT tana mai tunanin watarana da yardan Allah suna cikin nan suna shan soyayyar su, wani murmushi tayi kafin ta nufo downstairs fuskar nan tasha heavy makeup.
A farfajiyan gidan ta hangi Momma na zaune saman faran kujera, k'arasawa tayi tana dubanta daga yanda take tsaye kafin tace "Momma ni zan fita."
Baki sake Momma tace "Ke wannan kwalliya da kikayi haka ai gwara ki tsaya Tahir ya gani tunda ya kusa dawowa, ina mai tabbatar maki har kama yau kikayi da marigayiya Aisha ta."
K'atutun bak'in ciki ne ya tokare mak'oshin Shema'u jin Momma na had'ata da Aysha, wato dukda ta mutu baza'a daina kawo tunaninta first ba, harta kamanni ma wato ba'ason nata sai na Aysha, miji ma sai sauran na Aysha ake neman lik'a mata, kodayake ai ta riga Aysha fara son AT don haka dama AT nata ne since from the very beginning. Kai ta tsani Aysha wllhi, dolema ta d'aid'aita rayuwar Sajida kota halin k'ak'a ne.
"Momma kenan kinsan nace maki zanje gidan k'awata a Sabon gari, tun d'azu taketa min waya.... Ba jimawa zanyi ba insha Allah." Ta k'arashe maganar tana ciro waya a jaka tana duba sak'on Alh Aminu da ya shigo mata.
"Toh ai shikenan, kardai kiyi dare kuma ki kula da kwalta."
D'an murmushi Shema'u tayi kafin tace "Momma kenan wani sa'in idan kinyi magana kina bani dariya, yanzu ni ce sai an fad'a min na kula da kwalta, kodayake tun bayan accident d'in nan sai kin fad'i haka kullum idan zamu fita, ki kwantar da hankalin ki Mommata yau kam ma da taxi zan fita don motata babu enough fuel kuma yanda zanje kinga da d'an nisa."
Momma ta jinjina kai kafin tace "Shikenan Allah Ya tsare,." ko amsa mata Shema'u batayi ba taci gaba da tafiyarta.
Momma tayi jigum tana kallon Shema'u, a kullum idan ta tuna bata sanar da Shema'u asalin wanene mahaifin ta ba, hankalin ta yana matuk'ar tashi, gani take kaman duk randa Shema'u tasan asalinta zata tsaneta na har Abada. Allah sarki Alh Mukhtar marigayi mijinta mai rasuwa kuma mahaifin Ayshan ta, ya rik'i Shema'u amana, har ya koma ga ubangiji Shema'u batasan bashine mahaifinta ba,. Momma tasa bayan hannunta ta share k'wallan da suka zubo mata tunowa datayi yau babu Mukhtar babu Aysha, duk sun tafi sun barta. Jikinta yayi sanyi sosai da wannan tunani ta mik'e ta nufi cikin gida.
Sauri-sauri ta soma tafiya da sawu a layin, alla-alla take ta sami abun hawa ta d'ale amma shiru bata samu ba, kaman daga sama ta hangi motar AT na shigowa layin, k'irjinta ya yanke ya fad'i. Gaba d'aya daburcewa tayi don bataso suka had'u da AT ba, tasan zai iya cewa ta shigo ya ajiyeta.
Parking ya d'anyi sanda ya hangeta, cike da murmushin k'issa ta k'araso yanda yake, d'an rage glass yayi suka gaisa kafin ya tambayeta ina zataje.
A d'an daburce ta sanar dashi gidan k'awarta zataje kaman yanda ta sanar da Momma,. AT ya d'an murmusa wanda yake kashe Shema'u kafin yace "Toh banda abinki Shema'u me anfanin motar ki, kije a ciki mana."
D'an murmushin yak'e tayi kafin tace "Dr kenan, ai motar tawa tana buk'atan ziyartan gareji ne ma, amma babu matsala zan sami ko taxi ko adaidaita ne na shiga."
AT ya d'an dubi agogon jikin motar sa kafin yace "Toh shigo na ajiyeki, ko kuma ki karb'i tawa motar kije da ita."
Shema'u ta k'walalo ido waje, dad'i kaman ya karta, wai yau ita AT kema magana haka har yana cewa zai kaita anguwa. "Em... Em wllhi ka barshi kawai Dr I can manage, haba ka dawo daga office ga gajjiya, kana buk'atan hutu pls ka shiga ka huta."
Murmushi ya kuma yi a karo na biyu kafin yace "Karki damu ni nace zan kaiki ai, this is the least I can do after all the sacrifices you've done for my family. Pls ki shiga na ajiyeki."
Murmushi ta d'anyi zuciyarta fari k'al lallai AT yana appreciating abubuwan da takeyi wa yaransa, tabbas sune her key to his house.
Suna tafe babu mai cewa komai, sai binsa da mayen kallo take da wutsiyar idanu, wayyo Allanta gaskiya ta matsu tana tsananin buk'atar AT a shimfid'arta, sosai take kwad'ayin shi... Muryarsa ne ya katse mata tunanin ta.
"Na gode da devoting lokutanki masu anfani da kikayi ma iyalai na sannan ina fatan hakan won't affect your job." Idanunsa naga kwalta yayi maganar.
Rausayar da idanu tayi kafin tace "Haba Dr, saikace wani abin nayi, yaran nan fah are my obligation tunda yaran 'yar uwatace, ko a shari'a ne sunada hakki akaina a matsayina na yayar mahaifiyar su, Dr bazan b'oye maka ba wllhi ina son yaranka so na hak'ik'a, soyayyar da nakejin sam bana son rabuwa dasu."
Saida ya d'an kaikaito da fuska ya dubeta kafin ya maida idanunsa ga kwalta.
A tak'aice ya furta "Na gode da soyayyar da kike masu." tundaga haka bai kuma cewa komai ba har suka isar unguwar da suka nufa.
Gaba d'aya ta daburce ta soma tunanin ina zata sauk'a, wata dabara ta fad'o mata, Shagon gyaran gashi dake a bakin titi ta hanga, tayi saurin ciro wayarta tamkar mai karanta sak'o kafin ta d'anyi murmushi ta furta "Kai Salma dai akwai shirirta, waifa kaga tun d'azu nake jira ta turo min location na gidan nasu amma shiru. Sai yanzu take ce min na jirata a wancan saloon d'in."
Baice komai ba don kuwa sam bashida hayaniya, karya kan motar kurum yayi ya k'arasa bakin shagon gyaran gashin yayi parking.
Sai wani kwarkwasa take sanda take masa godiya had'i da sallama, shikam sam hankalinsa ma baya gareta, a tak'aice ya amsata kafin ya tada motar sa ya bar wajen.
*************
Aaa'ah, mamaki ya cika Ashfaq ganin tulin fake d'in magungunan da akayi ordering, kai anmayi banning wasu magungunan an hana amfani dasu. Cikin sauri ya shiga neman layin AT.
AT yana gama parking motar sa wayar Ashfaq ya shigo masa, nan take Ashfaq ya fad'a masa halin da ake ciki.
"What!" AT ya furta cikeda tashin hankali kafin yace "Ina Hisham ya bari hakan ta kasance, shine alhakin sayan magunguna suke wuyarsa..... Okay, ka gane zamu gudanar da bincike, zan kira Hisham d'in, kar ka bari a sauk'e kayan ko k'wayar magani ce.
Sosai hankalin AT ya tashi wannan ka iya jefa asibitinsa cikin had'ari mai girma, amma yasan Hisham bazaiyi haka ba, duk yanda akayi hakan ta faru ne bada saninsa ba. Neman layin Hisham ya shiga yi.
"Hisham ya akayi hakan ta faru, kasan irin had'arin da hakan ka iya jefa hospital d'inmu?" In a furious tune yayi maganar.
Gaban Hisham ya yanke ya fad'i amma yayi saurin saita kansa kafin yace "Tahir kasan dai da sanina bazanyi hakan ba, amma kar ka damu zanyi magana dasu distributors d'in, in short zamu daina sayan magunguna a company d'insu... Oh my god I'm really sorry Friend, nasan hakan zai janyo fad'uwa sosai."
Gajeren tsaki AT ya d'anyi kafin yace "Ba kud'in da za'a rasa bane damuwar, what matters shine b'ata sunan asibitin da hakan ka iya haifarwa da kuma amfani da magungunan... Thank goodness Ashfaq was there sanda suka delivering, kasan meye zai faru mu had'u a asibitin yanzu." Daga haka katse wayar sa yayi.