← Book details Shakuwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 63

Sashe 52

Shakuwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallonsa tayi da rinannun idanunta kafin tayi murmushin yak'e tace "Idan dai akan Sajida ce kar ka damu zan ci gaba da kula da ita, domin wannan alk'awari nayi ma 'yaruwata amma idan akan kawo amaryar ka cikin gidan nan ne kasani bazan hana Sajida making decision d'inta ba, the girl had enough already...." ta k'arashe tana k'ok'arin k'wace kanta daga rik'on da yayi mata...

Cikeda mamaki AT ke kallonta, yanda tayi maganar kaman ba ita ba, sam bai zaci zata goyi bayan Sajida ta aiwatar da abinda Hisham ya sanar dashi ba....

Da mamaki yake fad'in "Why are you sounding this way...?"

A harzik'e tace dashi "How am I sounding...?"

AT ya kuma rungumota kafin yace "I mean you are speaking in a strange manner, meke faruwa ne My Shemah..."

Da mamaki take dubansa lallai kaga namiji ka k'yalesa, tunda suke da ita bai tab'a kiranta his Shemah ba sai yau, gashi yanda ya fad'i ba k'aramim dad'i ya mata ba..

Ta ci gaba da k'ok'arin k'watan kanta ta fashe masa da wani irin kuka tana fad'in "Kar ka yaudareni da kalaman ka Tahir, kayi aure babu sani na ina a matsayin matar ka, sannan nima yaushe ka sauk'e min hakkina da har zaka auro wata, nikam na gaji da zam......" bata kai aya ba taji ya had'e lips d'insu waje guda... Take ya soma kasheta da wasu irin salo, jikin Shema'u ya d'auki k'yarma shi kuwa AT lokaci guda ya soma jin aches ta ko ina anjikinsa...

A kasalce ta turesa daga jikinta tana ci gaba da hawaye take fad'in "Karma ka soma abinda bazaka iya ba...." ta yunk'ura zata tashi ya kuma rungumota murya can k'asan mak'oshi yake fad'in "Shema'u I'm sorry, I'm sorry kinji but pls kar kice zaki rabu dani my children still needs you, auren Maryama da nayi banida option ne, Maryam amanace a hannu na kinga tun daga yanzu an soma samun matsala irin haka inaga na Aura mata wani, pls ki taimaka min na tsare amanar da Allah Ya bani idan har kina sona kinji....."

Gashi dai with a cool voice yake mata maganar cikin kwantar da hankali amma banda suya babu abinda zuciyarta keyi. Lallai ma AT ya raina mata hankali, wato sabida yaransa dai take zaune dashi, sam batada wani amfani da ya wuce ta kula masa da yaransa, gashi yanzu yayo aure kenan ya auri wacce yake so, har wani wai bashida option ne shiyasa ya auri Maryama, har yana wani cewa ta taimaka masa ya rik'e amanar sa... Uwar amanar ma!.. Tayi murmushi a hankali kafin taci gaba da tunanin nata, da sannu zata shayar dasu mamaki kuma wllhi wllhi sai AT ya sota ko naman jikinsa ne yake gutsirewa ya fad'i...

Cikin jikinsa yau tayi bacci dukda babu wani abinda ya shiga tsakaninsu amma kam taji jiki don da k'yar bacci ya sace ta. Washe gari rigar da ta sai mashi birthday gift d'insa ya saka don kawai ya faranta mata ....

Ko fitowa Sajida batayi ba, Shema'u ce ta ringa sintirin kai mata abinci. Koda AT ya shiga ma rufe idanunta tayi kaman tana bacci, bai damu ya tasheta ba sai ficewa da yayi.... Ko sallama yauma baiyi ma Shema'u ba sai jin k'aran rufe gate tayi... Zuciyarta tamkar ta fito waje ta fashe.....

AT kuwa yana ficewa gidan Hajiya ya nufa, a veranda ta sami 'yan yaran shi, Jamal da Ni'ima nan suka tafi a guje suna hayewa jikinsa suna gaida shi.

Fuskar sa ya cika da annuri ya d'aga Ni'ima sama yana shafa kan Jamal yake tambayar su suna lafiya..?

Jamal yayi saurin gyad'a kai kafin yace "Daddy mu muna lafiya amma Adda Maryama bata da lafiya tana kwance d'akin Hajiya tun jiya ma batada lafiya.... "

Gaban AT ya yanke ya fad'i! Duban Jamal ya kuma yi kafin yace "Hajiya fah? "

Hajiya wai taje sayo mata magani saidai Baaba Delu ce take nan.."

Ya jinjina kai yana tunanin wato dai Hajiya bazata daina self medication ba, saikace wata likitiya kai tsaye sai tayi ma kanta prescribing magani, ya zaci ta daina tunda ya tab'a d'ura mata ruwa a ciki ashe bata daina ba.

"Champ, princess kuje wajen Baaba Delu ko, barin duba Addar taku."

Gaba d'aya suka gyad'a masa kai suka wuce suka nufi sashen Baaba Delu...

Gabansa na dukan tara-tara ya nufi d'akin don baisan yaya zasu kwashe ba sannan baisan labarin ya risketa ko kuma bai risketa ba.

Kwance ya hangeta saman gado ta duk'unk'une cikin bargo sai rawan d'ari take idanunta a lumshe.

A hankali ya k'araso har gaban gadon had'i da k'ura mata idanu, saida ya d'iba wasu mintoci kafin ya zauna dap da ita ya kai hannunsa goshinta, nan yaji jikin nata k'auuu, zafi sosai.

A hankali ta bud'e idanu ta sauk'e su kansa, dukda tana cikin ciwo hakan bai hana gabanta yankewa ya fad'i ba.

Cikin sauri ya mik'e ya nemo bowl da ruwa da handtowel, sosai ya razana da jin zafin jikin nata abinka da likita, temperature d'in nata is very high...

Zama yayi ya yaye bargon data rufu dashi yasa hannu ya d'agota.... Ba Maryama kawai ba shi kansa AT cak ya tsaya yana kallonta..

Itakam bata gane me Uncle keyi ba, tsoro ne ma da firgici suka rufeta, meyasa Uncle zai rik'eta haka, ko ya zaci har yanzu ita d'in k'aramar yarinya ce.

Gaba d'aya ya kasa tab'uka komai sai kallon k'urilla da yake binta dashi. Ita kuwa Maryama ko bud'e bakinta ta kasa sai kallon itama take binsa dashi, zuciyarta ta raya mata k'ila tausayin abinda Ashfaq ya mata Uncle yake...

Yana nan rik'e da ita a hannunsa sam basuji shigowar Hajiya ba, sai salati data soma lokaci guda ta k'arasa ta fincike Maryama tana fad'in "Toh uban 'yan rashin kunya tashi min a saman gado, ko kunya bakaji ba god'e-god'e da kai ka wani shigo ka kallame yarinya salon ka mata wani abin ko, toh ahir d'inka, kul ka d'aga idanunka akan d'iyata... Kuma kaji da kyau asaran sadaki kayi ehe Maryama ba MATARKA bace......"

Daga AT har Maryama saida k'irajensu yayi wani irin bugu....

Ta kasa gasgata abinda take ji sai kallon mamaki databi Hajiya dashi tana girgiza kanta hawaye na zubo mata

Cikin sauri AT ya fice daga d'akin..

Hajiya ta rik'i bakinta domin ita kanta batasan tayi wannan sub'ul da bakan ba don dama bata so Maryama ta sani ba sai AT ya rubuta mata takardan sakin Maryama.....

*Sameena Aleeyou Mrs*

💘💘💘💘💘💘💘💘

*SHAK'UWA CE*

💘💘💘💘💘💘💘💘

*43*

*©Sameena Aleeyou...✍🏼*

_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION 🤝_

Kuka take sosai tana girgiza kai tana kallon Hajiya ba tareda ta iya furta koda kalma ba, har lokacin ta kasa yarda da abinda kunnenta ya jiye mata... Uncle, Uncle dai a matsayin mijinta na aure.... Bata iya furta koda kalma ba sai wani sabon kukan da ya kuma kufce mata, Hajiya gaba d'aya jikinta yayi sanyi sai lallashinta take amma kaman cewa take ta k'ara.. Shi kuwa AT har cikin k'ahon zuciyar sa yake jin rad'ad'in kukan da Maryama keyi...

Hajiya taci gaba da fad'in "Haba Maryama ta kiyi hak'uri ki daina b'ata hawayen ki kinji koh, idan dai auren Attahiru ne ina mai tabbatar maki ni da kaina zan saka shi ya rubuta saki ehe, da yak'i da ya so......"

AT bai iya ci gaba da sauraren kalaman Hajiya ba sai mik'ewa da yayi ya fice daga parlorn..

Maryama ta dubi Hajiya da watery eyes d'inta murya na rawa take fad'in "Hajiya da gaske Uncle ne mijina...?"

Hajiya ta kasa furta komai sai kallon tausayi databi Maryama dashi, zuciyarta gaba d'aya zafi yake mata domin a duniyar nan bata k'aunan ganin b'acin ran Maryama balle har taga hawayen ta.. Lallashinta Hajiya taci gaba da yi gaba d'aya ma ta mance magungunan data sayo mata a chemist d'in Ema, gyara mata kwanciya ta kuma yi sai huci take tana yin k'wafa...

AT kuwa yana nan lab'e yana jin Hajiya ta shige bathroom ya sad'ad'o ya shigo, fuskar Maryama naga d'aya b'angaren bata gansa ba sai k'aran tab'a ledan magani taji...

Tana juyowa sukayi ido hud'u, tattara magungunan yayi kafin ya d'aura d'an yatsa a lips d'insa alamun tayi shiru don ya jiyo Hajiya na k'ok'arin fitowa... Cikin sauri ya kwashi magungunan sannan ya fice... Maryama ta bisa da kallo tana ganin lamarin tamkar a wasan kwaikwayo wai ita Uncle ya aura. Tabd'ijam! Ko kusa Allah Ya gani bazata iya zaman aure da Uncle ba.

Koda Hajiya ta fito tana neman magungunan shiru Maryama tayi mata bata sanar da ita Uncle ne ya tattara ba, haka ta k'araci nemanta k'arshe tayi tunanin k'ila to jefa wani wajen.

*************

Shema'u ta kuma kallon Sajida a karo na biyu kafin tace "Sweetheart abunda ya faru ya riga ya faru, kedai kawai kiyi abinda na fad'a maki shine kawai zai lalata auren Maryama da Daddyn ki but idan ba taimakon Maryama kika samu ba Daddyn ki namiji ne, kiga maza ki barsu yanda kika gansu shi ko ajikinsa zai yada kai gaban k'aramar yarinya idandai buk'atarsa zai biya, b'acin ranki won't solve anything saidai ma ya k'ara maki k'unci da takaici... Sajida ina sonki ne shiyasa nake sanar dake wannan abu, muddin kika sami goyon bayan Maryama I assure you komai zai wargaje kin gane, sannan Daddyn ki ki basa hak'uri kinji koh ta haka ne kurum bazaiyi suspecting wani abu daga gareki ba kinji koh....."

Sajida ta gyad'a kai tana murmushi kafin tace "Aunty you always ve solution for everything, ina sonki...without you bansan yaya rayuwa zata kasance mana ba..."

Shema'u tayi murmushi kana tace "Nima ina sonku farin cikin ku shine nawa, idan don ta nine zan bar AT ya kawo Amaryar sa cikin gidan nan babu wani abu a ciki, tazo mu fafata ko ni ko ita, amma sabida nasan zuwanta na nufin tashin hankalin ki ne shiyasa nake nema maki solution kin gane...."

Sajida ta kuma murmusawa kafin ta rungume Shema'u, saida Shema'u ta bata magungunanta ta sha kafin ta gyara mata kwanciyar ta tace ta sami bacci kafin ta fice...

**************

Kaman wani munafuki haka yake lek'en su, Hajiya dasu Jamal zaune tacan gefe wajen flowers... Yaran suna wasan su yayinda Hajiya da Baaba Delu keta faman labari...
Chapter 52 · 0% Book details