Sashe 52
Nida Patient Dina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna zaune suna hira lokacin su Abba da baba ma sun dawo suna cikin dakin , zuruf sukaga hairah ta mike jikinta ne yadau rawa , ko wannensu da al ajabi akan fuskokinsu suke kallonta, zubewa tayi aƙasa jikinta na ci gaba da rawa mikewa dukkansu sukayi suna tambayarta meya faruwa amma ba ta basu amsa ba ya Usman yasa hannu yadagota yazaunar da ita akan gadon fanan yana mata magana " hairah meyake damunki ?" hawaye takeyi jikinta na tsuma , fanan ce ta ce" kowa yanda yi shuru na wasu lokuta " mikawa hairah hannunta tayi duka biyu , daura hannayen hairah tayi da nata hannun lokaci daya jikinta yadena rawan dakyar ta iya cewa " yayana ! Zata kashemin yayana " fanan ta ce "ki fadamin meye kike kallo " ta ce " na naganta itadin makira ce kuma mara imani " sake matse hannun fanan tayi ta cigaba da magana " ta shaƙe yaya hafiz zata wurgoshi ƙasa daga upstairs" jin abinda tafada ya tsorata su de yanzu suka tuna da babu kowa agidan dasauri fanan ta ce " su waye agidan bayan hafiz din sannan akan waye kike magana?" Hairah ta ce " babu kowa agidan securites ne dasuke cikin compound babu wanda yasan abinda yake faruwa , yayana kuma ita da shine acikin falo yanzu haka tana gab da wurgoshi ƙasa" tana gama fadin haka Abba dasauri yazaro wayarshi yakira number securites din gidan nan take suka daga yasanar dasu abinda yake faruwa , kusan su ashirin suka shiga cikin falon lokacin da Jessica ta gansu dariyar mugunta tayi sannan ta ajiye hafiz a ƙasa shafa wuyanshi yayi yana tari ganin tana gangarawa downstairs ne yasa yafara rarrafawa yasulale yashiga part din Mr azaad daga nan ya bullo ta garden sannan yafito compound baba me gadi ne kaɗai se driver suka rage acikin gidan dakyar ya iya kwalawa driver kira suka shiga motar yace mishi yakaishi gun ummi da gudu driver yafisgi motar .
Gangarowa ƙasa Jessica tayi ta tsaya a tsakiyarsu wani daga cikinsu ne yafara tunkaronta duka daya ta mishi yazube aƙasa yasuma , dukansu takeyi baji ba gani kaff dinsu kaff seda ta sumar dasu da muguwar duka , sannan ta fito compound tunda baba me gadi yaganta yaji tabashi tsoro tunkafin ta ce yabude mata kofa yabude .
fita tayi tana kallon titin daya kasu gida uku nan take tagano hanyar da su hafiz sukafi ,gudu tafarayi tana ɓacewa kamar walkiya tana bin bayansu .
Hairah dake rike da hannun fanan tana kallon duk abinda ke faruwa a falon ta ce " dukkansu tamusu duka sannan ta sumar dasu , yayana kuma yanzu haka yashigo asibitin nan tana binshi abaya " tana karishe maganar da takeyi tasake hannun fanan, ta mike tsaye , tana magana da hafiz dake gudun ceton ranshi domin har cikin asibitin ta biyoshi mutane se kallonta sukeyi kamar sun samu tv , yana gudu itakuma tana tafiya cikin kwanciyar hankali.
Gudu yakeyi yana hakki yana jin kwantaccen da hairah takeyi mishi can yace " hairah naga wasu kofofi gudu biyu wanne zanshiga wanne ne kuke ciki ga ta nan abayana" tsayawa hairah tayi abakin kofa ta ce " na farko zaka shigo yaya " sude al'amarin ya matuƙar girgizasu tunani suka farayi suna tambayar kansu shin hafiz da hairah sudin su waye ?.
Da karfin gaske ya turo kofar yarungume hairah dake tsaye abakin kofa, fashewa tayi da kuka tana " yayana " suna a haka Jessica tashigo dakin ja da baya sukayi dagudu hairah taje ta buya abayan mama shikuma hafiz ya boye a bayan Mr azaad harde hannunta tayi akirjinta tana kallonsu kamar yanda suma ita suke kallo seyanzu suka gane ashe Maryam din da Abba yatsinto ce innalillahi wainna ilaijiraji unnn lallai duniya babu yadda aciki se ka taimaki mutum yazo ya cuceka shisaka yanzu taimako yayi karanci , zuciyar Abba se kuna yakeyi yana kallon Maryam yama kasa magana amma har cikin ranshi beyi danasanin taimaka mata da yayi ba domin shi tsakani da Allah yataimaka mata , kallon Mr azaad tayi ta ce " ka turo yaron bayanka ko kuma ta sanadiyyar shi kowa na dakin nan ya rasa rayuwarshi , mugun kallo fanan da Mr azaad suke watsa mata, ganin beze miko mata shi bane yasa taje gaban Mr azaad din tasa hannu zata jawoshi Mr azaad yakai mata damka a wuya sannan ya dagata sama ya hade kanta da jikin bangon dakin ta zube aƙasa, daman haushinta yakeji domin yanzu yasake tabbatarwa Ita ce nan ummul aba isin abinda yafaru da fanan tana kokarin mikewa daga bugun datasha Mr azaad ya taka ruwan cikinta so yakeyi kawai yaga ta mutu ko hakan ze rage mishi raradin abinda yakeji , sa hannu yayi ya sake damko gashin kanta , ɓacewa tayi ta dawo bayanshi ta ce " kana tunanin zaka gwada min kai jarumine hahaaa" tafada tana dariya nuna anty shayida ta yi da hairah da hafiz ta ce " dake , dake dakuma kai duk sena kasheku ayau din nan " a tsorace anty shayida ta je taboye akusa da Abba . Baba ne ya ce " baiwar Allah menene hadinki damu ? wani laifin mukayi miki ne ?" Abba ya kalli baba yace " ni ne nan nakawota gida da niyar taimaka mata ashe annoba nadauko bansaniba" Maida kallonta kan baba tayi ta ce " babu abinda kukayi mini nidin yar saƙoce nazo gudanar da abinda aka aiko nine " ummi ta ce " to waye ya aiko ki wajen mu " fanan da ranta yayi matuƙar ɓaci ne ta ce " yi shuru ummina kar wanda yasake ce mata ƙala yanzu zatayi da nasanin zuwa aikan da aka mata " tana magana tana zuro ƙafafuwan ta kasa mikewa tayi tsaye tana bin Jessica da kallo dama tun farkon ganin da ta mata taji tsanarta lokaci daya ashe akwai dalilin haka, tunkaro fanan tayi tana kallonta daga sama har kasa cikin shakiyanci ta ce" oho nagane wato ke ce sarauniya? Amma yanaga bakiyi kama da sarauniyar da kowa yake shakka ba yanda ake labarin ki se naga ba haka kike ba , kinmin kama da matsoraciya sede balaifi kinada kyau kam, dukda bake nazo kashewa ba wancar me cikin nazo kashewa sekuma kema kina da ciki sekiyi kokarin taimaka mata ta hanyar zuwa a madadin ta , hakanma ba laifi tunda kema kinada cikin " tayi magana tana kallon anty shayida dake bayan Abba ,murmushi fanan tayi ta ce" kwantar da hankali, ai gane asali ba daga fuska take ba se angwada ake ganewa . shin kinason ganin asalina? amma fa kisani in kika gani ba lallai ba kici gaba da rayuwa ba " cewar fanan da idonta yakoma kalar fari tayi magana tana damkar wuyan Jessica kokarin kwatar kanta Jessica tafara tana fisge_fisge amma takasa kwatar kanta a hannun fanan, matso da fuskanta fanan tayi daff dana Jessica,sannan ta zaro idonta da suka koma fari tass babu digon baƙi aciki , hasken cikin idonta ne yafara shiga cikin idon Jessica nan take tafara konewa ta ciki ihu tafarayi . Fanan ta ce" nasan zaki bawa wa'yanda suka aiko ki labari inkun hadu a lahira " tana gama fadin haka tasake Jessica ta fadi ƙasa nan take jikinta yafara karkarwa kamar wacce aka jonawa shocking jikinta nafitar da hayaƙi me tururi haka tadingayi har ta koma kwarangwal daga nan kuma takoma toka tabace.
Dukkansu ajiyar zuciya suka sauke ganin sun rabu da ita , jinjina mata zeenat dake ɓoye abayan mama tayi ta ce " aikin ki na kyau anty fanan" hararanta fanan tayi ta ce " kema naki nakyau saboda kin iya ɓuya kam " dariya sukayi .
Kallon hafiz fanan tayi ta ce " lallai hafiz kaiɗin jarumine kayi na mijin kokari " hafiz da se yanzu hankalin shi yakwanta ganin fanan ta gabama da Jessica yayi murmushi kawai yaje bayan mama yariko hannun hairah suka zauna akusa da ya usman ya ce" fatan babu abinda yake damunki " kai ta gyada mishi sannan ta kwantar da kanta akan kafadarshi , sude yanzu tunda sun samu sun rabu da Jessica damuwar su susan su hairah sudin menene suke dauke dashi koɗe karya sukayi musu adangane da asalinsu.
Babane ya ce " hafiz shin ya akayi kuke iya magana da junanku batare da waya ba kuma hairah take iya ganinka aduk inda kake ? " Ajiyar zuciya hairah da hafiz suka sauke atare domin sun san dama dole sesunyi zargin wani abu , hafiz ya ce " mahaifinmu yakasance babban wanzami ne dake taimako sosai kuma yana bada magani , yana aiki da aljanu to tun muna yara wata rana yadawo gida da daddare muna bacci yasa mamanmu ta tashemu , zama mukayi agabanshi ya ce " hafiz ga hairah kanwarka ce ko bayan ranmu nasan zaka iya kula da ita " sannan ya yafito da wasu abubuwa acikin leda wanda nida hairah bamu san meye aciki ba, sunce ledar yayi nan take mukaga wasu abubuwa guda uku biyu masu zubi da kunne daya kuma kamar ido , miƙa min kunnen yayi yace in rike shi da karfi sannan yabawa hairah ido da hannu ya ce itama tarike, bamufi mintuna 30 da rikewa ba muka nemi abubuwan mukarasa domin ji mukayi babu su ahannun namu ashe cikin jikinmu yashige , se babanmu yace mana wannan abinda yabamu shine zezama garkuwa garemu duk nisar duniyar damuke zamu iya magana da junanmu sannan hairah zata na kallona inde wani mugun abu ze faru ne kaɗai hakan ze kasance, tundaga wannan lokacin in waninmu yana cikin hatsari mukan iya jiyowa har musamu wa'yanda zasu taimaka , wannan shine " shuru sukayi suna jinjina wannan lamarin ta wani bangaren za'a iya cewa hakan ze taimakawa yaran amma ta tawani bangaren hakan tsubbu ne tunda bawai dashi aka haife su ba rana tsaka yasaka musu shi ajikinsu , abba ne ya ce" Allah yajikansu da rahama " suka amsa da ameen.
Gangarowa ƙasa Jessica tayi ta tsaya a tsakiyarsu wani daga cikinsu ne yafara tunkaronta duka daya ta mishi yazube aƙasa yasuma , dukansu takeyi baji ba gani kaff dinsu kaff seda ta sumar dasu da muguwar duka , sannan ta fito compound tunda baba me gadi yaganta yaji tabashi tsoro tunkafin ta ce yabude mata kofa yabude .
fita tayi tana kallon titin daya kasu gida uku nan take tagano hanyar da su hafiz sukafi ,gudu tafarayi tana ɓacewa kamar walkiya tana bin bayansu .
Hairah dake rike da hannun fanan tana kallon duk abinda ke faruwa a falon ta ce " dukkansu tamusu duka sannan ta sumar dasu , yayana kuma yanzu haka yashigo asibitin nan tana binshi abaya " tana karishe maganar da takeyi tasake hannun fanan, ta mike tsaye , tana magana da hafiz dake gudun ceton ranshi domin har cikin asibitin ta biyoshi mutane se kallonta sukeyi kamar sun samu tv , yana gudu itakuma tana tafiya cikin kwanciyar hankali.
Gudu yakeyi yana hakki yana jin kwantaccen da hairah takeyi mishi can yace " hairah naga wasu kofofi gudu biyu wanne zanshiga wanne ne kuke ciki ga ta nan abayana" tsayawa hairah tayi abakin kofa ta ce " na farko zaka shigo yaya " sude al'amarin ya matuƙar girgizasu tunani suka farayi suna tambayar kansu shin hafiz da hairah sudin su waye ?.
Da karfin gaske ya turo kofar yarungume hairah dake tsaye abakin kofa, fashewa tayi da kuka tana " yayana " suna a haka Jessica tashigo dakin ja da baya sukayi dagudu hairah taje ta buya abayan mama shikuma hafiz ya boye a bayan Mr azaad harde hannunta tayi akirjinta tana kallonsu kamar yanda suma ita suke kallo seyanzu suka gane ashe Maryam din da Abba yatsinto ce innalillahi wainna ilaijiraji unnn lallai duniya babu yadda aciki se ka taimaki mutum yazo ya cuceka shisaka yanzu taimako yayi karanci , zuciyar Abba se kuna yakeyi yana kallon Maryam yama kasa magana amma har cikin ranshi beyi danasanin taimaka mata da yayi ba domin shi tsakani da Allah yataimaka mata , kallon Mr azaad tayi ta ce " ka turo yaron bayanka ko kuma ta sanadiyyar shi kowa na dakin nan ya rasa rayuwarshi , mugun kallo fanan da Mr azaad suke watsa mata, ganin beze miko mata shi bane yasa taje gaban Mr azaad din tasa hannu zata jawoshi Mr azaad yakai mata damka a wuya sannan ya dagata sama ya hade kanta da jikin bangon dakin ta zube aƙasa, daman haushinta yakeji domin yanzu yasake tabbatarwa Ita ce nan ummul aba isin abinda yafaru da fanan tana kokarin mikewa daga bugun datasha Mr azaad ya taka ruwan cikinta so yakeyi kawai yaga ta mutu ko hakan ze rage mishi raradin abinda yakeji , sa hannu yayi ya sake damko gashin kanta , ɓacewa tayi ta dawo bayanshi ta ce " kana tunanin zaka gwada min kai jarumine hahaaa" tafada tana dariya nuna anty shayida ta yi da hairah da hafiz ta ce " dake , dake dakuma kai duk sena kasheku ayau din nan " a tsorace anty shayida ta je taboye akusa da Abba . Baba ne ya ce " baiwar Allah menene hadinki damu ? wani laifin mukayi miki ne ?" Abba ya kalli baba yace " ni ne nan nakawota gida da niyar taimaka mata ashe annoba nadauko bansaniba" Maida kallonta kan baba tayi ta ce " babu abinda kukayi mini nidin yar saƙoce nazo gudanar da abinda aka aiko nine " ummi ta ce " to waye ya aiko ki wajen mu " fanan da ranta yayi matuƙar ɓaci ne ta ce " yi shuru ummina kar wanda yasake ce mata ƙala yanzu zatayi da nasanin zuwa aikan da aka mata " tana magana tana zuro ƙafafuwan ta kasa mikewa tayi tsaye tana bin Jessica da kallo dama tun farkon ganin da ta mata taji tsanarta lokaci daya ashe akwai dalilin haka, tunkaro fanan tayi tana kallonta daga sama har kasa cikin shakiyanci ta ce" oho nagane wato ke ce sarauniya? Amma yanaga bakiyi kama da sarauniyar da kowa yake shakka ba yanda ake labarin ki se naga ba haka kike ba , kinmin kama da matsoraciya sede balaifi kinada kyau kam, dukda bake nazo kashewa ba wancar me cikin nazo kashewa sekuma kema kina da ciki sekiyi kokarin taimaka mata ta hanyar zuwa a madadin ta , hakanma ba laifi tunda kema kinada cikin " tayi magana tana kallon anty shayida dake bayan Abba ,murmushi fanan tayi ta ce" kwantar da hankali, ai gane asali ba daga fuska take ba se angwada ake ganewa . shin kinason ganin asalina? amma fa kisani in kika gani ba lallai ba kici gaba da rayuwa ba " cewar fanan da idonta yakoma kalar fari tayi magana tana damkar wuyan Jessica kokarin kwatar kanta Jessica tafara tana fisge_fisge amma takasa kwatar kanta a hannun fanan, matso da fuskanta fanan tayi daff dana Jessica,sannan ta zaro idonta da suka koma fari tass babu digon baƙi aciki , hasken cikin idonta ne yafara shiga cikin idon Jessica nan take tafara konewa ta ciki ihu tafarayi . Fanan ta ce" nasan zaki bawa wa'yanda suka aiko ki labari inkun hadu a lahira " tana gama fadin haka tasake Jessica ta fadi ƙasa nan take jikinta yafara karkarwa kamar wacce aka jonawa shocking jikinta nafitar da hayaƙi me tururi haka tadingayi har ta koma kwarangwal daga nan kuma takoma toka tabace.
Dukkansu ajiyar zuciya suka sauke ganin sun rabu da ita , jinjina mata zeenat dake ɓoye abayan mama tayi ta ce " aikin ki na kyau anty fanan" hararanta fanan tayi ta ce " kema naki nakyau saboda kin iya ɓuya kam " dariya sukayi .
Kallon hafiz fanan tayi ta ce " lallai hafiz kaiɗin jarumine kayi na mijin kokari " hafiz da se yanzu hankalin shi yakwanta ganin fanan ta gabama da Jessica yayi murmushi kawai yaje bayan mama yariko hannun hairah suka zauna akusa da ya usman ya ce" fatan babu abinda yake damunki " kai ta gyada mishi sannan ta kwantar da kanta akan kafadarshi , sude yanzu tunda sun samu sun rabu da Jessica damuwar su susan su hairah sudin menene suke dauke dashi koɗe karya sukayi musu adangane da asalinsu.
Babane ya ce " hafiz shin ya akayi kuke iya magana da junanku batare da waya ba kuma hairah take iya ganinka aduk inda kake ? " Ajiyar zuciya hairah da hafiz suka sauke atare domin sun san dama dole sesunyi zargin wani abu , hafiz ya ce " mahaifinmu yakasance babban wanzami ne dake taimako sosai kuma yana bada magani , yana aiki da aljanu to tun muna yara wata rana yadawo gida da daddare muna bacci yasa mamanmu ta tashemu , zama mukayi agabanshi ya ce " hafiz ga hairah kanwarka ce ko bayan ranmu nasan zaka iya kula da ita " sannan ya yafito da wasu abubuwa acikin leda wanda nida hairah bamu san meye aciki ba, sunce ledar yayi nan take mukaga wasu abubuwa guda uku biyu masu zubi da kunne daya kuma kamar ido , miƙa min kunnen yayi yace in rike shi da karfi sannan yabawa hairah ido da hannu ya ce itama tarike, bamufi mintuna 30 da rikewa ba muka nemi abubuwan mukarasa domin ji mukayi babu su ahannun namu ashe cikin jikinmu yashige , se babanmu yace mana wannan abinda yabamu shine zezama garkuwa garemu duk nisar duniyar damuke zamu iya magana da junanmu sannan hairah zata na kallona inde wani mugun abu ze faru ne kaɗai hakan ze kasance, tundaga wannan lokacin in waninmu yana cikin hatsari mukan iya jiyowa har musamu wa'yanda zasu taimaka , wannan shine " shuru sukayi suna jinjina wannan lamarin ta wani bangaren za'a iya cewa hakan ze taimakawa yaran amma ta tawani bangaren hakan tsubbu ne tunda bawai dashi aka haife su ba rana tsaka yasaka musu shi ajikinsu , abba ne ya ce" Allah yajikansu da rahama " suka amsa da ameen.