← Book details Nida Patient Dina Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 66

Sashe 51

Nida Patient Dina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahanzarce yayi wanka yashirya yafito yasamu yaseer afalo ya ce " dude mutafi nagama " riko hannunshi yaseer yayi ya zaunar da shi ya ce " dude calm down please ka kwantar da hankalinka fanan yanzu na cikin koshin lafiya, yanzu ka tsaya ka sa wani abu a cikinka " ajiyar zuciya Mr azaad yasauke ya ce " banida lokacin wani cin abinci yanzu kawai mutafi karka ɓata min rai" yanda yaga ya haƙiƙice sesun tafi yasa cikin sauri ya shiga kitchen ya dauko mishi yogurt yabashi ya ce " dude ɗan Allah kayi hakuri kasha wannan se mu tafi kaga kai kanka yanzu baka cikin yanayi me kyau kamar fah zaka fadi " ganin yaseer baze barshi su tafi ahaka bane yasa ya karbi yogurt din yabude yakafa abakinshi seda yashanye tas yayi cilli da goran sannan ya ce " yanzu zamu iya tafiya ?" Yar murmushin yaseer yayi at least yasamu Mr azaad yasa wani abu a cikinshi ya ce " to muje " gaba Mr azaad yayi yabarshi abaya saukowa sukayi dede zasu fita a falon ya hangi maryam rakube abayan kujera , " keeee" yafurta yana tsaye yariƙe kugu yaseer kuma na gefenashi yanason ganin wayake ƙira fitowa tayi daga lungu kujerun jikinta na rawa ta ce " naaam" watsa mata harara yayi ya ce " karki yarda in dawo gidan nan in sameki " yana gama fadin haka yafice kare mata kallo yaseer yayi fuskanshi adan hade yabi bayan Mr azaad motar suka shiga yaseer yafara driving hankalinshi nakan titi ya ce " dude wancan yarinyar daga ina ? wallahi kallo daya na mata naji hankalina be kwanta da itaba, kamar wata mara gaskiya" kwantar da kanshi Mr azaad yayi akan seat din motar ya ce " nima haka dazun bayan dawuwarmu naganta agidan kallo daya na mata naji na tsaneta , banason ganinta jikina na bani kamar akwai abinda yakawota gidanmu " dukan siterin motar yaseer yayi ya ce" exactly wallahi dude dole abinciki yarinyar nan kasan yanzu duniya ba yarda ,bakowa ne zaka yarda dashi ba daga baya seka taimaki mutum yazo ya cutar dakai " sake maimaita maganar yaseer Mr azaad yakeyi acikin ranshi se yanzu ne ma yafara zargin wannan yarinyar tabbas akwai abinda yakawota gidan, zarginta yafara abisa abinda yafaru da fanan tuna maganar abashiyya yayi na kancewa abin akan anty shayida yaso faruwa sekuma fanan taje amaimakonta tabbas akwai wani abinda ba dede ba , haka yadinga tunani har suka iso asibitin, shiga cikin resting room din sukayi suka samu abba da baba basa nan , da sallama dauke abakinsu suka shigo mikewa Amira tayi ta bashi kujeran gaban gadon fanan zama yayi yariƙe hannunta yana kallon fuskanta, mama kam kunya ne ya kamata se kawar da kanta gefe takeyi saboda rike hannun fanan da Mr azaad yayi,ummi ta lura da haka murmushi tayi aranta ta ce " kunyan fanan ashe ga do tayi " karban wayarta tayi ahannun zeenat dake zaune waje daya tayi tagumi tazubawa fanan ido , kiran layin gida ummi tayi abu me aiki tadauka sanar da ita tayi girki sukawo itada driver asibiti tayi sannan ta katse kiran.

Kiran sallah la'asar akayi mazan suka tafi masallaci matan kuma sukayi acikin dakin bayan sun idar suka zauna a lokacin mazan duk sun dawo . Kusan atare anty firdausi tadawo hannunta rike da katon basket na abinci daddyn junior kuma na rike da junior haka abu me aiki itama hannunta rike da basket din abinci gaishesu abu me aiki tayi tana tambayar yame jiki suka bata amsa da sauki sannan ta zauna .

Kowa sa mishi abinci akayi yanaci amma banda mama da Mr azaad dake zaune yana rike da hannun fanan. Bayan kamar awa daya lokacin har biyar yayi hannunta dake cikin nashine yaji yana motsawa maida hankalinshi yayi kan hannun yaga yana motsi , ahankali tafara ware idanunta da tajisu sunyi mata nauyi kamar ba nata ba hasken dataci karo da shine yasa tamaida idon ta rufe sake jarraba bude su tayi nan tafara gani dishi_dishi , akan kyakkyawar fuskar Mr azaad tafara bude idonta da shima itadin yake kallo murmushi yamata itama tamayar mishi tana kokarin mikewa rungumeta yayi ajikinshi sannan yazaunar da ita , ya sa hannu yashafa gashinta ya ce " alhamdulillah wifey thank god you're awake" yagama magana yana manna mata kiss agoshinta , ganin ta farka ne yasa sukayi hamdala suna godewa Allah rike hannunta ummi tayi ta ce " my feena ya jikin naki ?" Muryanta da dan karfi saboda ta tashi taji jikinta da karfi kamar babu abinda yake damunta sedan ciwon kai kadan ta ce " da sauki sosai ummina " haka suka dinga mata ya jiki hairah da zeenat Amira duk dawuwa kusa da ita sukayi suka zauna kallon mama fanan tayi ta ce" mamaana " murmushi kawai mama tayi ta ce" na'am fanan ya jikin naki ?" " Dasauki mama " motsa hannunta dake cikin na Mr azaad tayi amma yaƙi sakinta shi babu ruwan shi bedamu da mutanen da suke cikin dakin ba . Hairah ce ta kalli zeenat ta ce" anty zeenat ina ya hafiz ?" Kafin zeenat tayi magana ma areef ya rigata da" hafiz na makaranta yanzu hakama maybe ko sun tashi kokuma sun kusa tashi " jin ya'yan nata na makaranta yasa bata sake cewa komai ba.

Kamar ba mara lafiya ba haka ta sake anata hira da ita duk sunyi farin ciki da ganin condition din nata is not critical, shide Mr azaad ƙala bece ba se aikin kallon yanda fanan take hira yakeyi yana jin dadi aranshi ɗan dawani abu yasameta besan yazeyi da ranshi ba .

Se yamma liris hafiz yadawo gida driver nayin packing yafita rike da school bag dinshi da laptop yashiga cikin main falo babu kowa gidan shuru beyi tunanin babu kowa ba yawuce part dinsu yashiga bedroom dinshi ya ajiye school bag din da laptop akan table yashiga toilet wanka yayi yafito yashirya yadau wayarshi acikin locker dan inze tafi makaranta ajiyeta yakeyi dukda makarantarsu makarantar masu kudine yara suna abinda suka gadama amma shi barin waya yakeyi agida saboda karatu ne yakaishi beze yi abinda wa'yanda suka taimaki rayuwarshi zasuji ba dadi ba. Part din ummi yashiga ze gaisheta yayi ta sallama a bedroom yaji shuru ba amsa se ya dawo main falo kawai yazauna yana danna waya , motsi yafaraji abayan kujera beyi tunanin komai ba yatashi ya leka bayan kujeran ganin mutum yayi tana zaune ta rakube mamaki ne yakama hafiz dan yasan shide be santa ba amma daga ina take to ya ce " sannunki" kallonshi Maryam tayi ta ce " inayini " be bata amsa ba se tambayar ta dayayi " me kikeyi anan ?" Inda_inda ta fara " uhmm ina zaune ne " "okay to kifito abayan kujera wani inya ganki ahaka zeyi tunanin bakida gaskiya ne " yafada yakoma inda yake yazauna besake bin ta kanta ba yaci gaba da danna wayarshi.

Alamun mutum yaji tsaye akanshi hakan yasa yaɗago kai , kallonta yayi tsaye akanshi tana kallonshi haɗe fuska hafiz yayi dan ta bashi haushi ya ce" ke meye haka zaki tsayamin akai bakisan babu kyau ba " wani irin munafikin murmushi maryam tayi batace mishi komai ba , kuma bata tashi mishi akai ba ganin hakane yasa yatashi akan kujeran dayake ya koma wani yaci gaba da abinda yake yi sake tsayawa tayi akanshi , kallonta kawai yayi bece komai ba yadauki wayarshi yabar falon yahaura upstairs kamar daga sama yaganta agabanshi ja da baya yayi ɗan yadan tsorata saboda yasan afalo yabarta maida kallonshi yayi fallon yaga tana nan a inda yabarta sannan yakalli wacce take gabanshi addu'a yafarayi acikin zuciyarshi kafin ya ce " meye kike bukata awajena ? Meya kawoki wannan gida?" Murmushi tayi mishi kafin ta ce " abinda nake buƙata awajanka shine ranka , abinda yakawo gidan nan kuma shine kashe duk wani wanda yake cikin wannan ahalin " duk adan tsorace hafiz yake amma afusace ya ce " Allah baze taba baki nasara ba , kuma nima bazan bar hakan yafaru ba sede koke koni! Koki kasheni ko ni in kasheki" dariyar bosawa tayi harda rike ciki ganin yanda yake da karfin hali kyasta yatsunta tayi nan take kayan jikinta da ita kanta ta sauya, fara ce sol tana sanye da bakaken kaya ,matsetsen riga da wando baƙi jikin riga da wandon akwai chains , ga uban hills shima baƙi , gashin kanta brown color ne curly bakinta yasha baƙin janbaki , shiganta da komai nata na yan America ne , ja baya yakeyi tana biye dashi ta ce " zamu gani yau kaiɗin jarumine ko kuma ragone " juyawa hafiz yayi yana neman abinda ze buga mata mopper ya hango yadauko ya buga mata akanta nan take mopper ya karye sake ja da baya hafiz yayi ya ce " to ke din wacece ? meye mugun nufin ki akan mu?" Hannunta ta mika nan take yayi tsayi tashaƙo wuyar hafiz ta dagashi sama kafin ta ce" okay tunda abinda kake so ka ji kafin ka mutu , sunana Jessica kelvin " tana fadar haka ta kara shaƙe mishi wuya sannan taje can saman upstairs tana shirin wurgoshi ƙasa, kallon ƙasa hafiz yayi yaga irin mugun nisa dayake dashi da ƙasa yasan tabbas ta wurgoshi mutuwa zeyi hakan yasa muryarshi da baya fita sosai saboda shaƙeshin datayi ya ce " hairahhhhhhhhhh" dariya tayi ta ce " itakuma wacece haka shin kana ganin zata ceceka ne ?" .
Chapter 51 · 0% Book details