← Book details Nida Patient Dina Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 66

Sashe 5

Nida Patient Dina Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Batare da hujja ba munyi abinda be kamataba a madadina da tashar BBC news muna me matukar bawa Mr and Mrs azaad mainasara hakuri akan laifin da muka musu " shigowa manager da chairman sukayi suname basu hakuri akan kuskuren da akayi domin sunsan muddin Mr azaad yabar wajan nan batare daya hakuraba to kashinsu yabushe. Kafin nan da abinda be wuce 1hr ba labari yabaza duniya kota ina se sakon bada hakuri ne yake shigo TikTok, YouTube, Facebook, Twitter, Instagram, mikewa Mr azaad yayi yace " Nina gama abinda yakoni nan dan haka banda lokacin batawa " yafada yana rike hannun fanan suka fara tafiya se hotuna da video ake musu har suka fita bin bayansu masu tsaronshi sukayi suna bude musu marfin motar shiga yayi yana rike da hannunta zama tayi tana kallon fuskanshi sake hannunta yayi haka sukaci gaba zamansu kamar kurame harsuka iso gida ana bude motar tayi gaba dan sotakeyj taje tabawa su ummi labari , aharzuke ta hango aneesa ta nufota, tana isowa gurinta ta wanketa da mari ta shaketa " wallahi yau sena kasheki ko ni ko ke " kakari fanan tafara saboda shakan da aneesa tayi mata bana wasa bane cikin sauri azaad yakaraso yafisge aneesa daga jikin fanan rike wuyanta fanan tayi tana kuka mari azaad yawanka mata yana fadin " bakida hankali ne kasheta kikeson kiyine " kuka tafashe mishi dashi " baby you betrayed me nizaka yaudara kaje kayi aure a munafurce bayan anmana baiko dama kai munafiki ne bansaniba " ji yayi tabashi tausayi yasan baa kyauta mataba riko hannunta yayi yace" calm down muje ciki " wuce fanan sukayi dake tsaye tana kuka kallonta aneesa tayi tana mata gwalo, goge fuskanta tayi tashiga falo babu kowa aciki haurawa tayi part dinsu afalo tasamesu aneesa nakwance akan kafadarshi shikuma yana aiki a laptop ko kallonsu bata sakeyi ba tashiga bedroom dinta tarage kayan jikinta zuwa wata dogon riga me hannun vest mara nauyi yakamata sosai duk shape dinta yafito tasa hula fitowa falon tayi still suna zaune suna kallon labaran da akeyi akan sharrin da akamusu an wanke sunansu tare dabasu hakuri tanajin sanda Mr azaad yayi kiran waya yana cewa adakatar da su dukda batasan dawaye yake magana ba Amma tafahimci BBC news yabada umarnin adakatar . Jin haka yasa fanan tashiga matsanancin farin ciki jitayi duk bacin rai dinda take ciki ya yaye kitchen tashiga tayi jallof din macaroni da beef yasha vegetables se tashin kamshi yakeyi tadawo falon dan nesa dasu tanacin abincinta gaba daya kamshin yacika musu ciki sedataji ta koshi ta ajiye plate din gefe kasa hakuri aneesa tayi tamike tashiga kitchen din bude tukunyan da fanan tayi girki tayi kozata samu sauran macaroni babu komai aciki dan iya cikinta tadafa dawuwa falon tayi " baby yunwa nakeji kuma abinci kadan tayi basaura kace mata tamin wani kaji" shuru yamata be kulata ba sake nanata maganar tayi ganin zata dameshi ne yasa ya kalli fanan dake zaune tana kallon tv tanashan drinks hankalinta kwance yace " Meye dalilin dazesa kiyi abincin dan kadan tunda yakare seki dafa mata wani " dariyar renin hankali tayi ta kalli aneesar cike da tsiwa tace " ohhh really indafa abinci wata katuwa taci ? To ni baa kawoni gidan nan dan indafawa wata katuwar banza abinci taci ba" cike da mamaki azaad ke binta da kallo with his sexy voice yace " me aka kawo ki kiyi?" Ko ajikinta tace bautar aure da kula da miji dan haka kar wata takara cemin inmata abinci yauwa" mamakin yanda take zaro zance yakeyi yar yarinya da ita wato hartasan wani bautan aure .
Akule aneesa tace " to dakike maganar wani kinzo bautar aure nasan komai baby yafadamin dalilin auren naku kuma yanzu da sunanshi yawanku zesake ki ya aureni kinzo kina wani iyayi " magana fanan tayi azuciyarta yazama dole in koya mata hankali , fari tayi da manya_manyan idonta tadaura kafa daya kan daya, Mr azaad de da ido kawai yakebinta . Sa idonta tayi cikin na aneesa tana fadin" kalleni dakyau namiki kama da wacce zaa aura asaka? To shi saurayin naki daya fada miki hakan yafadane dan kawai yakwantar miki da hankali amma inbanda haka meye zeyi dake nifa yarinya ce me kananan shekaru shisa yakyasa yatakura, hankalinshi be kwanta ba seda yaga nazama matarshi kuma yana bani kulawa sosai ko bahaka bane honey sugar ?" Tafada tana kashewa Mr azaad ido daya, yama rasa mezece mata kullum iyayin yarinyar nan da yarintar ta karuwa yakeyi cize libs dinshi nakasa yayi.
Kuka aneesa tasa tafita da gudu zuwa part din mommy tana kudurta aniyar ganin bayan fanan domin yau ta wulakanta ta setadau mataki .
Seyanzu tafara danasanin abubuwan data fada meya kaita nema, mikewa tayi simi_simi tashige dakinta takwanta tana dariya inta tuna abinda tawa aneesa , kamar amafarki taganshi atsaye akanta tashi tayi tazauna tana narai_narai da ido dukufowa yayi, ja baya tayi, rumfa yamata da faffadar kirjinshi da hannayenshi guda biyu , kallon cikin idon juna sukeyi without a blink sa hannu yayi yazame hulan dake kanta gashinta yazubo akan bed din hannunsa yasa yadamki kan da karfinshi ihu tasa jin azaba rike hannunshi tayi da duk hannayenta biyu tana kuka dagota yayi tsaye still yana rike da gashin. dayan hannunshi yasa yamatse dan karamin bakinta yace " banason inga ina hurting din mutum amma kinja dole sena hukuntaki abinda nakeso dake stay in your limits don't try to cross it inba haka ba sekinyi dana sanin sanina! Bantaba sonki ba kuma har abada bazansoki ba dan ke yarinyace dakanta ke cike da yarinta impact ke bakima kai girman dazan yi rayuwar aure dakeba kinmin yarinya kikarewa kanki kallo dakyau reason din dayasa akayi auren nan shine saboda awanke sunanmu and komai yanzu is steady zansake ki kije kiyi rayuwarki freely kwaila kawai " duk maganar dayakeyi besaketaba yana damke da gashin kanta da kuma bakinta daya matse seda yagama magana tukun yayi wurgi da ita kan gadon yafice.
Kukanta tasha mecin rai ahaka bacci yadauketa.

" Mommy wallahi sena kasheta inbahaka ba hankalina baze taba kwanciya ba " cewar aneesa dake magana tana kuka tsaki mommy tayi tace " yanzu ke ko kunya bakiji ba kanwar bayanki zaki tsaya kina mata kuka baki kamata ba kin manta jakin duka ! Wallahi shame on you" sake fashewa tayi da kuka tazo tafada mata instead of sunemi solution tahau ta da fada lura da hakan ne yasa mommy takwantar da murya " is okay my angel karki damu yau yau din nan zandau mataki setayi danasanin abinda ta aikata miki karki kara shiga part din se gobe kinji ko angel din dadi" sake fuska tayi tana murmushi seyanzu hankalinta yakwanta jin mommy tace zatadau mataki akanta.

Har seda time din sallah yayi ta farka taje tayi sallah har time din tana tuna bakaken maganganun da Mr azaad yamata haka tazura dogon hijab dinta tayi falon ummi samun zeenat tayi afalo tana shan rufaida yogurt zama tayi tana karban roban yogurt din tafara sha sake baki zeenat tayi dan batasan da shigowarta ba tace " ikon Allah anty fanan yaushe kika shigo " tana Shan yogurt din tace mata " sanda kike kwadayi mana" dariya zeenat tayi tace" to naji ya kike ya program munganku a tv alhamdulillah komai yatafi successful yanda akeso" " hmmm kede bari kawai nikadai nasan irin farin cikin danake ciki " hira sukeyi har anty Amina tafito tasamesu kallon fuskan fanan tayi taga alamar tayi kuka kiranta tayi wajanta fanan taje tazauna waigawa tayi ga zeenat tace " to anty kwadayis kidan bamu waje zamuyi magana " tashi tayi tayi dakinta maida kallonta tayi kan fanan sannan tace " my fanan meke damunki wani abu azaad yamiki " dasauri ta girgiza mata kai alamar ah ah ta fahimmci tanason boye mata ne yasa tace " karkimin kallon sirka kidaukeni amatsayin antynki firdausi duk wata damuwarki karki boyemin dakuma tsakaninki da azaad semu samo solutions kinji" sosai hankalinta yakwanta dan dama tarasa wazata fadawa damuwarta , bata labarin tun daga dawuwarsu da shaketa da aneesa tayi har izuwa abinda Mr azaad yamata dakuma maganganu daya fada mata. Jinjina kai tayi dan tasan zaa rina kuma bakomai yasa yakula aneesa ba sedon taji haushi amma yanzu dole tadaura fanan akan hanya dazata gyarawa azaad zama dakuma ita kanta aneesa datakeson takurawa rayuwarsu.
____" kinaji abinda kikayi yau kinmin dede domin inkika sake kika kyale aneesa tsaf zata renaki sannan inason kinunawa azaad ke ba yarinya bace kamar yanda yafada shida kanshi zedawo yana baki hakuri da lallabaki ! Tunda harya ce miki kwaila yayi mukuma zamuyi iya kokarinmu dan muyi proving dinshi wrong " zare ido tayi tana kallon anty Amina kamar amafarki " yanzu Mr azaad dinne zewani lallaba mutum har yabada hakuri tabb " sosai anty Amina ta dinga bata shawarwari tayanda zatajawo hankalin Mr azaad duk da fanan tanajin kunyan wasu Abubuwa amma haka tanutsu tana sauraran anty Amina dan tadau aniyar nunawa Mr azaad ita ba yarinya bace. Farin ciki anty Amina tayi ganin fanan tadauki shawararta dakuma wayon data mata yayi tasiri dan ita tayi hakan ne da tasamu su dede ta kansu dan tasan yanda Mr azaad baya son fanan, haka itama fanan bata sanshi auren kawai Allah yayi de zaayi shine .
Chapter 5 · 0% Book details